ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
Tarihi

Bikin murnar cika shekaru 80 da cimma nasarar babban yakin kare kasa na tsohuwar tarayyar Soviet da aka gudanar kwanan nan a birnin Moscow na kasar Rasha, ya sake tunatar da al’ummomin duniya game da abubuwan da suka wakana a tarihi. Yadda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gudanar da ziyarar aiki a kasar Rasha a daidai wannan lokaci tare da halartar bikin yana da ma’ana mai matukar muhimmanci, wanda ya isar da sakon kasar Sin ga duniya, wato har kullum kasar tana tsayawa tsayin daka a kan kiyaye tsarin duniya, kuma kullum tana daukar nauyin da ke bisa wuyanta na gina al’ummar duniya mai kyakkyawar makoma ta bai daya.  

Tarihi tamkar madubi ne. A yakin da aka gudanar a tsakanin masu kishin adalci da masu zalunci yau da kimanin shekaru 80 da suka wuce, da Sin da Rasha sun kasance muhimman fagage na yakin a Asiya da kuma Turai, wadanda suka ba da gudummawa mai matukar muhimmanci wajen cimma nasarar yakar ‘yan “Fascist” a duniya. Sai dai har bayan wucewar shekaru 80, ba a kai ga kawo karshen nuna fin karfi a duniya ba, inda ra’ayin kashin kai, da yin fito na fito a tsakanin kasa da kasa ke ci gaba da addabar duniya.

  • Sin Na Fatan India Da Pakistan Za Su Kaucewa Kara Rura Wutar Tashin Hankali
  • Nijeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taro Karo Na 4 Na Ƙananan Sana’oi Na Ƙungiyar AU

A kwanakin baya, shugaban kasar Amurka Donald Trump ya sanar da tsai da ranar 8 ga watan Mayun kowace shekara a matsayin “ranar nasarar Amurka”, kuma a cewarsa, “Ko kana so ko ba ka so, sabo da mu ne aka kai ga samun nasarar”, “tankoki da jiragen yaki, da manyan motoci, da jiragen sama, da kuma sojoji na kasar Amurka ne suka ci nasara a kan makiya a shekaru 80 da suka wuce. Idan babu Amurka, to sam sam ba nasarar yakin.” Lallai furucin na shugaba Trump da ya mai da nasarar da kasa da kasa suka samu a matsayin gudummawar da Amurka ita kadai ta bayar, ya sake shaida mana nuna fin karfi da kasar Amurka ta saba yi.

ADVERTISEMENT

Nasarar yakin duniya na biyu nasara ce ga dukkanin bil Adama, sabanin ta wata kasa daya kadai. Miyagun hasarorin da yakin ya haifar sun bayyana cewa, danniya da zalunci ba hanyar da ta dace ta cudanyar al’ummomin duniya ba ce, kuma nuna karfin soja ba dabara ce ta kiyaye zaman lafiya ba, haka kuma cin nasara daga faduwar wani bangare ba zai kai ga ci gaban dan Adam ba. Za a iya tabbatar da kyakkyawar makoma ta bai daya ga dukkanin bil Adam, matukar an yi koyi daga darasin tarihin yakin duniya na biyu, tare da yin watsi da kowane irin ra’ayi na nuna fin karfi.

Kasashen duniya na rungumar adalci a maimakon nuna fin karfi, kuma manufar gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya ga dukkanin bil Adam da kasar Sin ta gabatar ta nuna mana hanyar da ta dace ta cudanyar kasashen duniya. Don haka ma, tun bayan da aka gabatar da ita a shekaru 10 da suka wuce, an shigar da ita cikin kudurin MDD, da ma tsarin kungiyar SCO da ta BRICS, lamarin da ya shaida yadda kasa da kasa suka cimma daidaito a kan wannan dabara ta kasar Sin.

LABARAI MASU NASABA

Bikin Baje Koli CIIE, Bikin Zaburar Da Manoman Afirka

CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

Baya ga haka, duniya ta shaida yadda kasar Sin ta yi watsi da mulkin mallaka, da cin nasara daga faduwar wani bangare a yayin da take zamanantar da kanta, har ma ta bude sabon babin hadin gwiwar samun nasarar juna. Daga nasarorin da aka cimma bisa shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya”, zuwa bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin da ya samar da dandalin more damammaki ga duniya, kuma daga samar da hidimomin tauraron dan Adam na Beidou ga kasa da kasa, zuwa yadda fasahar Juncao ta samar da moriya ga kasashe sama da 100, kasar Sin ta shaida wa duniya cewa, kasashe masu tasowa suna iya zamantar da kansu ba tare da bin hanyar da kasashen yamma suka bi a baya ba.

Tarihi ya haskaka makomar dan Adam, kuma muna da imanin cewa, Bil’adama zai iya samar wa kansa kyakkyawar makoma muddin ya rike tarihi a zuci, kuma ba za su kai ga cimma nasara a kan kalubalen da ke gabansu ba, har sai sun hada kai da juna. (Lubabatu)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bikin Baje Koli CIIE, Bikin Zaburar Da Manoman Afirka
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Koli CIIE, Bikin Zaburar Da Manoman Afirka

November 12, 2025
CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 
Ra'ayi Riga

CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

November 11, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Next Post
Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Tsohuwar Firaministan Bangaladesh Sheikha Hasina,

An Yanke Wa Tsohuwar Shugabar Bangladesh Hukuncin Kisa

November 17, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

November 17, 2025
Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

November 17, 2025
Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

November 17, 2025
Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.