• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bikin murnar cika shekaru 80 da cimma nasarar babban yakin kare kasa na tsohuwar tarayyar Soviet da aka gudanar kwanan nan a birnin Moscow na kasar Rasha, ya sake tunatar da al’ummomin duniya game da abubuwan da suka wakana a tarihi. Yadda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gudanar da ziyarar aiki a kasar Rasha a daidai wannan lokaci tare da halartar bikin yana da ma’ana mai matukar muhimmanci, wanda ya isar da sakon kasar Sin ga duniya, wato har kullum kasar tana tsayawa tsayin daka a kan kiyaye tsarin duniya, kuma kullum tana daukar nauyin da ke bisa wuyanta na gina al’ummar duniya mai kyakkyawar makoma ta bai daya.  

Tarihi tamkar madubi ne. A yakin da aka gudanar a tsakanin masu kishin adalci da masu zalunci yau da kimanin shekaru 80 da suka wuce, da Sin da Rasha sun kasance muhimman fagage na yakin a Asiya da kuma Turai, wadanda suka ba da gudummawa mai matukar muhimmanci wajen cimma nasarar yakar ‘yan “Fascist” a duniya. Sai dai har bayan wucewar shekaru 80, ba a kai ga kawo karshen nuna fin karfi a duniya ba, inda ra’ayin kashin kai, da yin fito na fito a tsakanin kasa da kasa ke ci gaba da addabar duniya.

  • Sin Na Fatan India Da Pakistan Za Su Kaucewa Kara Rura Wutar Tashin Hankali
  • Nijeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taro Karo Na 4 Na Ƙananan Sana’oi Na Ƙungiyar AU

A kwanakin baya, shugaban kasar Amurka Donald Trump ya sanar da tsai da ranar 8 ga watan Mayun kowace shekara a matsayin “ranar nasarar Amurka”, kuma a cewarsa, “Ko kana so ko ba ka so, sabo da mu ne aka kai ga samun nasarar”, “tankoki da jiragen yaki, da manyan motoci, da jiragen sama, da kuma sojoji na kasar Amurka ne suka ci nasara a kan makiya a shekaru 80 da suka wuce. Idan babu Amurka, to sam sam ba nasarar yakin.” Lallai furucin na shugaba Trump da ya mai da nasarar da kasa da kasa suka samu a matsayin gudummawar da Amurka ita kadai ta bayar, ya sake shaida mana nuna fin karfi da kasar Amurka ta saba yi.

Nasarar yakin duniya na biyu nasara ce ga dukkanin bil Adama, sabanin ta wata kasa daya kadai. Miyagun hasarorin da yakin ya haifar sun bayyana cewa, danniya da zalunci ba hanyar da ta dace ta cudanyar al’ummomin duniya ba ce, kuma nuna karfin soja ba dabara ce ta kiyaye zaman lafiya ba, haka kuma cin nasara daga faduwar wani bangare ba zai kai ga ci gaban dan Adam ba. Za a iya tabbatar da kyakkyawar makoma ta bai daya ga dukkanin bil Adam, matukar an yi koyi daga darasin tarihin yakin duniya na biyu, tare da yin watsi da kowane irin ra’ayi na nuna fin karfi.

Kasashen duniya na rungumar adalci a maimakon nuna fin karfi, kuma manufar gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya ga dukkanin bil Adam da kasar Sin ta gabatar ta nuna mana hanyar da ta dace ta cudanyar kasashen duniya. Don haka ma, tun bayan da aka gabatar da ita a shekaru 10 da suka wuce, an shigar da ita cikin kudurin MDD, da ma tsarin kungiyar SCO da ta BRICS, lamarin da ya shaida yadda kasa da kasa suka cimma daidaito a kan wannan dabara ta kasar Sin.

Labarai Masu Nasaba

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Baya ga haka, duniya ta shaida yadda kasar Sin ta yi watsi da mulkin mallaka, da cin nasara daga faduwar wani bangare a yayin da take zamanantar da kanta, har ma ta bude sabon babin hadin gwiwar samun nasarar juna. Daga nasarorin da aka cimma bisa shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya”, zuwa bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin da ya samar da dandalin more damammaki ga duniya, kuma daga samar da hidimomin tauraron dan Adam na Beidou ga kasa da kasa, zuwa yadda fasahar Juncao ta samar da moriya ga kasashe sama da 100, kasar Sin ta shaida wa duniya cewa, kasashe masu tasowa suna iya zamantar da kansu ba tare da bin hanyar da kasashen yamma suka bi a baya ba.

Tarihi ya haskaka makomar dan Adam, kuma muna da imanin cewa, Bil’adama zai iya samar wa kansa kyakkyawar makoma muddin ya rike tarihi a zuci, kuma ba za su kai ga cimma nasara a kan kalubalen da ke gabansu ba, har sai sun hada kai da juna. (Lubabatu)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Na Fatan India Da Pakistan Za Su Kaucewa Kara Rura Wutar Tashin Hankali

Next Post

Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

Related

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…
Ra'ayi Riga

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

4 days ago
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba
Ra'ayi Riga

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

6 days ago
Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
Ra'ayi Riga

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

2 weeks ago
Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
Ra'ayi Riga

Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta

2 weeks ago
Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada
Ra'ayi Riga

Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

2 weeks ago
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

2 weeks ago
Next Post
Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.