• English
  • Business News
Sunday, June 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Binciken Digirin Cuwa-cuwa Na Kasashen Waje Ya Tayar Da Kura

by Bello Hamza
1 year ago
in Labarai
0
NUC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Binciken da wani dan jarida na kafar yada labarai ta intanet, Daily Nigeria ya gudanar a kan yadda ake samun shaidar karatun Digiri ta cuwa-cuwa cikin mako shida a wata Jami’ar Kwantano da ke kasar Benin ya tayar da kura a Nijeriya cikin wannan makon inda Ministan Ilimi ya ba da umarnin dakatar da tantance duk wata shaidar karatun Digiri daga kasashen Benin da Togo.

Wakazalika, binciken wanda ya dangana har da shiga tsarin bautar kasa (NYSC) ta amfani da shaidar karatun ba tare da wata matsala ba, ya kuma jaza wa wasu jami’o’in waje guda 18 da ke Nijeriya, inda aka dakatar da harkokinsu da bayar da shaidar karatunsu nan take.

  • Yadda ANA Ta Shugabanci Gangamin Saukaka Zuwa Hajjin 2024 A Nijeriya
  • Dangote Ya Sauko Daga Matsayin Attajirin Da Ya Fi Kudi A Afrika

Hukumar kula da jami’o’i (NUC) ta gargadi al’umma da su guji mu’amala da wadannan jami’o’in.
Huhukumar, ta fitar da cikakken sunayen jami’o’in da aka haramta takardar shaidar digirinsu, inda ta wallafa sunayensu a shafinta na Intanet, da suka hada da: 1. Jami’ar Kimiyya da Gudanarwa ta Port No-bo, Jamhuriyar Benin, da sauran cibiyoyin ta da ke Nijeriya. 2. Jami’ar Bolta, da ke Ghana, da sauran cibiyoyin ta a Nijeriya. 3. Jami’ar International Unibersity, Missouri, USA, Kano da Lagos, da duk wasu cibiyoyin ta a Nijeriya. 4. Jami’ar Collumbus, UK, tana aiki da duk wasu cibiyoyin ta a Nijeriya. 5. Tiu In-ternational Unibersity, UK, da duk wasu cibiyoyin ta a Nijeriya.

Sauran su ne: 6. Jami’ar Pebbles, UK, da duk wasu cibiyoyin ta a Nijeriya. 7. London Edternal Studies UK, da duk wasu cibiyoyin ta a Nijeriya. 8. Jami’ar Pilgrims da duk wasu cibiyoyin ta a Nijeriya. 9. Jami’ar Kirista ta Yammacin Afirka, da duk wasu cibiyoyin ta a Nijeriya. 10. Jami’ar EC-Council Unibersity, Amurka, da ke da reshe a Ikeja a Jihar Legas. 11. Kwaleji Concept (London), Ilorin, da duk wasu ci-biyoyin ta a Nijeriya.

Bugu da kari, matakin ya kuma shafi 12. Jami’ar Houdegbe ta Arewacin Amurka da ke Nijeriya. 13. Makarantar Kasuwanci ta Jami’ar Irish a London, da duk wasu cibiyoyin ta a Nijeriya. 14. Jami’ar Ilimi, Winneba, Ghana, da duk wasu cibiyoyin ta a Nijeriya. 15. Jami’ar Cape Coast, Ghana, da duk wasu ci-biyoyin ta a Nijeriya. 16. Jami’ar Gamayya ta Afrika, da ke Kwatano da duk wasu cibiyoyinta a Nijeriya. Sai Jami’ar Yammacin Pacific, Denber, Colorado, da ke da Cibiya a Owerri da kuma 18. Jami’ar Ebangel ta Amurka da Chudick Management Academic, da ke Legas.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati

Binciken da aka gudanar tun da dadewa ya sa ake ta cece-kuce a kan yadda matasan kasar nan ke tafiya Kwatano suna kammala karatun Digiri cikin dan kankanin lokaci.

Sai dai yanzu bisa wannan sanarwa, ba a san ko ma’aikatar ilimin za ta fito ta wallafa sunayen Jami’o’in da ta amince da su ba a kasashen.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ilimijabun digiriNUC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasafin 2024 Na Tarayya Da Jihohi Naira Tiriliyan 44.9 A Faifai

Next Post

Kirsimati: ‘Yan Nijeriya 163,000 Suka Ci Gajiyar Tallafin Sufurin Gwamnati – Minista

Related

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

7 hours ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati
Labarai

Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati

8 hours ago
Ƙungiyar Gwamnoni Sun Yi Ta’aziya Kan Rasuwar Ƴan Wasan Kano 21
Labarai

Ƙungiyar Gwamnoni Sun Yi Ta’aziya Kan Rasuwar Ƴan Wasan Kano 21

11 hours ago
Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano
Labarai

Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano

12 hours ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

13 hours ago
Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

13 hours ago
Next Post
minista

Kirsimati: ‘Yan Nijeriya 163,000 Suka Ci Gajiyar Tallafin Sufurin Gwamnati – Minista

LABARAI MASU NASABA

Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu

Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu

May 31, 2025
CMG Ya Watsa Shirin Musamman Na Bikin Duanwu Na 2025

CMG Ya Watsa Shirin Musamman Na Bikin Duanwu Na 2025

May 31, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (2)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (2)

May 31, 2025
Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

May 31, 2025
Ministocin Wajen Sin Da Kamaru Sun Gana Kan Alakar Kasashensu Da Batun Kafa IOMed

Ministocin Wajen Sin Da Kamaru Sun Gana Kan Alakar Kasashensu Da Batun Kafa IOMed

May 31, 2025
Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum

Zulum Ya Ba Da Tallafin Karatu Ga Mata ‘Yan Asalin Jihar Da Suka Samu Maki 250 A JAMB

May 31, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati

Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati

May 31, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Kasashe Masu Tasowa Ya Dade Da Zama Kan Gaba A Bangaren Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Waje

Hadin Gwiwar Sin Da Kasashe Masu Tasowa Ya Dade Da Zama Kan Gaba A Bangaren Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Waje

May 31, 2025
Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara

Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara

May 31, 2025
Hukumar Shiga Tsakani Za Ta Samar Da Sabbin Damammakin Sulhunta Rikici

Hukumar Shiga Tsakani Za Ta Samar Da Sabbin Damammakin Sulhunta Rikici

May 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.