• English
  • Business News
Monday, September 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Binciken Gwamnatin El-Rufai: Ko Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Za Ta Rusa Mai Rusau?

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Labarai
0
Binciken Gwamnatin El-Rufai: Ko Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Za Ta Rusa Mai Rusau?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kallo ya koma kan Majalisar Dokokin Jihar Kaduna yayin da ta kafa kwamitin mutum 13 domin gudanar da bincike a kan harkokin kudaden da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasir el-Rufai ta gudanar a tsawon shekara takwas da gwamnatin ta kwashe a kan karagar mulki.

Har ila yau, majalisar ta dora wa kwamitin alhakin binciken kudaden tallafi da na bashin da gwamnatin el-Rufai ta amso.

  • Baje Kolin Kayayyakin Amfani Na Kasa Da Kasa Na Sin Ya Gabatar Da Fitattun Kamfanoni Sama Da 4019
  • Zulum Ya Amince Da Fitar Da Naira Biliyan 1.3 Don Tallafawa Dalibai 997 Na Aikin Kiwon Lafiya 

Dan majalisa mai wakiltar mazabar Kaura a zauren majalisar dokokin jihar, Hon. Yusuf Mugu ne ya gabatar da kudurin a zauren majalisar a tsakiyar makon nan.

Haka kuma majalisar ta ce za ta bi diddigin kudaden da tsohuwar gwamnatin ta kashe wajen aiwatar da manyan ayyuka a tsawon wa’adin mulkin el-Rufai tun daga 2015 zuwa 2023.

Shugaban majalisar, Hon. Yusuf Dahiru Liman ya nemi ‘yan kwamitin da su gayyaci duk masu ruwa da tsaki da suke da alaka da binciken domin su amsa tambayoyi kan lamarin.

Labarai Masu Nasaba

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

Ya tabbatar da cewa za a gudanar da binciken ne bisa adalci tare da bai wa koya damar gabatar da gaskiyarsa.

Shi dai Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani ya bayyana cewa ya gaji bashin dala miliyan 587 da naira biliyan 85 da kuma kwangiloli har 115 daga gwamnatin el-Rufai.

Ya nuna damuwarsa kan illar da bashin ke janyo wa jihar, wanda ya ce bashin ya hana biyan albashin ma’aikatan jihar.

Sai dai da yawa sun yi watsi da kalaman gwamnan bisa cewa da sa hannunsa aka karbi bashin lokacin da yake kujerar Sanata mai wakiltar Kaduna ta Tsakiya.

Masu sharhin al’amuran yau da kullum na ganin wannan yunkurin na majalisa na da alaka da siyasa bisa yadda ake ganin kamar dangantaka ta dan fara tsami a tsakanin el-Rufai da Gwamnatin Tinubu wacce ta yi masa ta leko ta koma a kan mukamin minista, shi kuma ya fara hada kai da wasu ‘yan adawar jam’iyya mai mulki.

Abin da mutanen Kaduna ke jiran gani shi ne, ko majalisar za ta iya rusa mai rusau kamar yadda el-Rufai ya yi farin jini da sunan a yakin neman zaben 2015, ganin cewa galibin wadanda ya yi aiki da su suna nan birjik a cikin gwamnatin da ke ci wadda take korafi a kan bashin da tsohuwar gwamnatin ta ci?


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasafin 2024 Ya Tona Asirin Yadda Ma’aikatu Ke ‘Sharholiya’

Next Post

A Watan Mayu Za A Bude Bikin Baje Kolin Motoci Na Afrika A Legas

Related

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩
Manyan Labarai

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

9 hours ago
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

9 hours ago
Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama
Manyan Labarai

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

10 hours ago
NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma
Manyan Labarai

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

11 hours ago
Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku
Tsaro

Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku

13 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

15 hours ago
Next Post
A Watan Mayu Za A Bude Bikin Baje Kolin Motoci Na Afrika A Legas

A Watan Mayu Za A Bude Bikin Baje Kolin Motoci Na Afrika A Legas

LABARAI MASU NASABA

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

September 7, 2025
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

September 7, 2025
Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

September 7, 2025
El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

September 7, 2025
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

September 7, 2025
An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

September 7, 2025
Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

September 7, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

September 7, 2025
NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

September 7, 2025
Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.