• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Binciken Gwamnatin El-Rufai: Ko Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Za Ta Rusa Mai Rusau?

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Gwamnatin

Kallo ya koma kan Majalisar Dokokin Jihar Kaduna yayin da ta kafa kwamitin mutum 13 domin gudanar da bincike a kan harkokin kudaden da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasir el-Rufai ta gudanar a tsawon shekara takwas da gwamnatin ta kwashe a kan karagar mulki.

Har ila yau, majalisar ta dora wa kwamitin alhakin binciken kudaden tallafi da na bashin da gwamnatin el-Rufai ta amso.

  • Baje Kolin Kayayyakin Amfani Na Kasa Da Kasa Na Sin Ya Gabatar Da Fitattun Kamfanoni Sama Da 4019
  • Zulum Ya Amince Da Fitar Da Naira Biliyan 1.3 Don Tallafawa Dalibai 997 Na Aikin Kiwon Lafiya 

Dan majalisa mai wakiltar mazabar Kaura a zauren majalisar dokokin jihar, Hon. Yusuf Mugu ne ya gabatar da kudurin a zauren majalisar a tsakiyar makon nan.

Haka kuma majalisar ta ce za ta bi diddigin kudaden da tsohuwar gwamnatin ta kashe wajen aiwatar da manyan ayyuka a tsawon wa’adin mulkin el-Rufai tun daga 2015 zuwa 2023.

Shugaban majalisar, Hon. Yusuf Dahiru Liman ya nemi ‘yan kwamitin da su gayyaci duk masu ruwa da tsaki da suke da alaka da binciken domin su amsa tambayoyi kan lamarin.

LABARAI MASU NASABA

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

Ya tabbatar da cewa za a gudanar da binciken ne bisa adalci tare da bai wa koya damar gabatar da gaskiyarsa.

Shi dai Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani ya bayyana cewa ya gaji bashin dala miliyan 587 da naira biliyan 85 da kuma kwangiloli har 115 daga gwamnatin el-Rufai.

Ya nuna damuwarsa kan illar da bashin ke janyo wa jihar, wanda ya ce bashin ya hana biyan albashin ma’aikatan jihar.

Sai dai da yawa sun yi watsi da kalaman gwamnan bisa cewa da sa hannunsa aka karbi bashin lokacin da yake kujerar Sanata mai wakiltar Kaduna ta Tsakiya.

Masu sharhin al’amuran yau da kullum na ganin wannan yunkurin na majalisa na da alaka da siyasa bisa yadda ake ganin kamar dangantaka ta dan fara tsami a tsakanin el-Rufai da Gwamnatin Tinubu wacce ta yi masa ta leko ta koma a kan mukamin minista, shi kuma ya fara hada kai da wasu ‘yan adawar jam’iyya mai mulki.

Abin da mutanen Kaduna ke jiran gani shi ne, ko majalisar za ta iya rusa mai rusau kamar yadda el-Rufai ya yi farin jini da sunan a yakin neman zaben 2015, ganin cewa galibin wadanda ya yi aiki da su suna nan birjik a cikin gwamnatin da ke ci wadda take korafi a kan bashin da tsohuwar gwamnatin ta ci?

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato
Labarai

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

November 7, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

November 7, 2025
Next Post
A Watan Mayu Za A Bude Bikin Baje Kolin Motoci Na Afrika A Legas

A Watan Mayu Za A Bude Bikin Baje Kolin Motoci Na Afrika A Legas

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

November 7, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

November 7, 2025
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

November 7, 2025
Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

November 7, 2025
Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)

Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)

November 7, 2025
Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

November 7, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.