ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Binciken Gwamnatin El-Rufai: Ko Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Za Ta Rusa Mai Rusau?

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Gwamnatin

Kallo ya koma kan Majalisar Dokokin Jihar Kaduna yayin da ta kafa kwamitin mutum 13 domin gudanar da bincike a kan harkokin kudaden da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasir el-Rufai ta gudanar a tsawon shekara takwas da gwamnatin ta kwashe a kan karagar mulki.

Har ila yau, majalisar ta dora wa kwamitin alhakin binciken kudaden tallafi da na bashin da gwamnatin el-Rufai ta amso.

  • Baje Kolin Kayayyakin Amfani Na Kasa Da Kasa Na Sin Ya Gabatar Da Fitattun Kamfanoni Sama Da 4019
  • Zulum Ya Amince Da Fitar Da Naira Biliyan 1.3 Don Tallafawa Dalibai 997 Na Aikin Kiwon Lafiya 

Dan majalisa mai wakiltar mazabar Kaura a zauren majalisar dokokin jihar, Hon. Yusuf Mugu ne ya gabatar da kudurin a zauren majalisar a tsakiyar makon nan.

ADVERTISEMENT

Haka kuma majalisar ta ce za ta bi diddigin kudaden da tsohuwar gwamnatin ta kashe wajen aiwatar da manyan ayyuka a tsawon wa’adin mulkin el-Rufai tun daga 2015 zuwa 2023.

Shugaban majalisar, Hon. Yusuf Dahiru Liman ya nemi ‘yan kwamitin da su gayyaci duk masu ruwa da tsaki da suke da alaka da binciken domin su amsa tambayoyi kan lamarin.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Ya tabbatar da cewa za a gudanar da binciken ne bisa adalci tare da bai wa koya damar gabatar da gaskiyarsa.

Shi dai Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani ya bayyana cewa ya gaji bashin dala miliyan 587 da naira biliyan 85 da kuma kwangiloli har 115 daga gwamnatin el-Rufai.

Ya nuna damuwarsa kan illar da bashin ke janyo wa jihar, wanda ya ce bashin ya hana biyan albashin ma’aikatan jihar.

Sai dai da yawa sun yi watsi da kalaman gwamnan bisa cewa da sa hannunsa aka karbi bashin lokacin da yake kujerar Sanata mai wakiltar Kaduna ta Tsakiya.

Masu sharhin al’amuran yau da kullum na ganin wannan yunkurin na majalisa na da alaka da siyasa bisa yadda ake ganin kamar dangantaka ta dan fara tsami a tsakanin el-Rufai da Gwamnatin Tinubu wacce ta yi masa ta leko ta koma a kan mukamin minista, shi kuma ya fara hada kai da wasu ‘yan adawar jam’iyya mai mulki.

Abin da mutanen Kaduna ke jiran gani shi ne, ko majalisar za ta iya rusa mai rusau kamar yadda el-Rufai ya yi farin jini da sunan a yakin neman zaben 2015, ganin cewa galibin wadanda ya yi aiki da su suna nan birjik a cikin gwamnatin da ke ci wadda take korafi a kan bashin da tsohuwar gwamnatin ta ci?

Gwamnatin
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
A Watan Mayu Za A Bude Bikin Baje Kolin Motoci Na Afrika A Legas

A Watan Mayu Za A Bude Bikin Baje Kolin Motoci Na Afrika A Legas

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.