• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Biyan Sabon Haraji: Gwamnati Ta Tsame Kananan Kamfanoni Da Manoma

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
1 year ago
haraji

Gwamnatin tarayya ta amince da tsame kananan masana’antu, kamfanoni da manoma daga biyan kebantaccen haraji da nufin rage yawan haraji da ke kan kamfanonin.

Kazalika, gwamnatin ta kuma yi garanbawul ga tsarin harajin da ake kan a da rage yawan harajin ga kamfanoni da kuma aiwatar da manufofi masu rahusa domin kaucewa rugujewar kamfanonin.

  • Harajin Da EU Ta Sanyawa Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Kasar Sin, Ita Zai Yi Wa Illa
  • EU Na Shirin Kakaba Harajin Wucin Gadi Kan Ababen Hawa Masu Amfani Da Lantarki Kirar Kasar Sin

Shugaban kwamitin shugaban kasa kan gyara fasalin haraji, Taiwo Oyedele shi ne ya sanar da hakan a ranar Talata a shafinsa na Tiwita, inda ya kara da cewa, Shugaban kasa Bola Tinubu ya amince da sabon kebantaccen harajin.

A cewarsa, tsohon kebantaccen haraji da ake amfani da shi da aka aiwatar tun a 1978, cike yake da batutuwan da suka shafi janyo karuwar adadi a yayin hulda na babu gaira babu sabab, janyo karancin masu biyan haraji na tsawon lokaci, rashin adalci, lafta wa kamfanoni kudi sosai da dai sauransu.

Kebantaccen haraji wani hanya ne na tattara kudin shiga na haraji da ya kama daga kaso 5 cikin 100 zuwa 10 cikin 100, ya dangane da irin kasuwancin da za a yi. Ana tattara shi ne zuwa ranar 21 na watan da ke tafe. Rashin biya a kan lokaci ka iya janyo a ci tarar kamfani har naira 25,000 a watan farko da kuma 5,000 kari kan haka a kowace wata da aka kasa cika ka’ida.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

Ya ce: “Kebantaccen haraji an gabatar da shi a Nijeriya ne tun 1977 da nufin biyan haraji gabanin gudanar da wasu takaitattun kasuwanci. Tsawon lokaci tsarin na wahalar da kamfanoni da janyo musu matsaloli da dama, sannan ya na kawo musu nakasu wajen biyan faraji.

“A kokarin gwamnati na kyautata biyan haraji, don haka ne aka gabatar da sabon tsarin amsar kebantaccen haraji a Nijeriya da nufin saukaka wa kananan kamfanoni.

“Wadanda aka tsame daga biyan kebantaccen harajin sun hada da kananan masana’antu, kamfanoni da manoma domin rage musu wahalhalun biyan haraji.

“Hakan don saukaka biyan haraji da tafiya daidai da duniya ne aka dauki wannan matakin,” ya shaida.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140
Labarai

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Majalisar Dattawa
Labarai

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa
Labarai

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Next Post
Ministan Yaɗa Labarai Ya Jajanta Wa Mataimakin Gwamnan Neja Kan Rasuwar Matarsa

Ministan Yaɗa Labarai Ya Jajanta Wa Mataimakin Gwamnan Neja Kan Rasuwar Matarsa

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.