Aƙalla mutane bakwai ne suka rasu, wasu kuma suka jikkata bayan da Boko Haram suka kai wa masu zaman makoki hari a garin Kopl, da ke ƙaramar hukumar Chibok a Jihar Borno.
Harin ya auku ne da misalin ƙarfe 6 na yammacin ranar Litinin, lokacin da mutanen garin suka taru don yin zaman makokin mutumin da ya rasu a makon da ya gabata, sai maharan sun afka musu da harbi.
- Sojoji Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace, Sun Ƙwato Shanu 32 A Katsina
- ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Mutum 8 Da Bam A Borno
Shugaban ƙaramar hukumar Chibok, Hon. Modu Mustapha, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce waɗanda suka jikkata an kai su Asibitin Mubi da ke Jihar Adamawa.
Ya ƙara da cewa adadin mamatan zai iya haura bakwai domin har yanzu ana neman waɗanda suka ɓace.
Harin na zuwa ne sa’o’i kaɗan bayan wasu fasinjoji sun mutu bayan motarsu ta taka bam da Boko Haram suka birne a kan hanyar Gamboru Ngala zuwa Kala Balge.
Sanata Ali Ndume, mai wakiltar yankin Borno ta Kudu, ya bayyana cewa hare-haren na ƙara ƙamari a yankin abun takaici ne.
Ya ce ya samu rahoto tsakanin Hawul da Garkida inda aka ce an kashe ’yan sa-kai sama da 10 a ranar Litinin.
A cewarsa, sama da mutane 100 aka kashe cikin wata guda a hare-hare da aka kai Sabon Gari, Izge, Kirawa, Pulka, Damboa, Chibok, Askira Uba da wasu garuruwa da dama.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp