• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bola Tinubu Ya Gana Da Wang Yi

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Bola Tinubu Ya Gana Da Wang Yi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasar Najeirya Bola Tinubu, ya gana da ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi a jiya Alhamis 9 ga wata, a birnin Abuja, fadar mulkin Najeriya.

Yayin ganawar tasu, Wang Yi ya isar da gaisuwa da kyakkyawan fatan sabuwar shekara daga shugaban kasar Sin Xi Jinping zuwa shugaban Najeriya. Ya ce, mai girma shugaba Tinubu ya kammala ziyarar aikinsa a kasar Sin cikin watan Satumban bara, inda shi da shugaba Xi Jinping suka sanar da raya huldar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a duk fannoni, don tabbatar da raya huldar kasashen biyu zuwa wani sabon mataki.

  • Xi Jinping Ya Amsa Wasikar Da Wasu Matasa ’Yan Wasan Peking Opera Suka Aika Masa
  • Alkaluman Hauhawar Farashi Na Sin Sun Karu Da Kaso 0.2% A 2024

Ya ce huldar dake tsakanin Sin da Najeriya misali ce ta ingantacciyar huldar Sin da kasashen Afirka, kuma ta wuce hulda tsakanin kasashen biyu, kamata ya yi bangarorin biyu sun kara hadin gwiwarsu don raya kyakkyawar makomar al’ummun kasashen biyu a dukkan fannoni a sabon zamani, da samar da abin koyi ga hadin kan kasashe masu tasowa da saurin bunkasuwa.

Wang Yi ya jinjinawa matsayin da Najeriya ke kai, na nacewa ga manufar “kasar Sin daya tak a duniya”, kuma Sin na goyon bayan Najeriya da ta bi hanyar raya kai bisa halayenta, da mara mata baya ga aikin yaki da ta’addanci, da kiyaye zaman lafiya, da kwanciyar hankali a wannan yanki, da kara mata kwarin gwiwar taka karin rawarta a duniya.

A nasa bangaren, shugaba Tinubu ya isar da sahihiyar gaisuwarsa ta bakin Wang Yi ga shugaba Xi Jinping. Ya ce, Najeriya ta dora muhimmanci matuka kan huldar kasashen biyu, kuma tabbatar da ci gaban da aka samu a taron koli na dandalin tattauna hadin kan Sin da Afirka, na da ma’ana sosai ga bunkasar kasarsa. Ya ce, Sin na da ingantaciyyar kima a duniya, kuma yana fatan Sin za ta ci gaba da goyawa Najeriya baya don ta kara taka rawa a cikin harkokin duniya.

Labarai Masu Nasaba

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

Ban da wannan kuma, shugaba Tinubu ya bayyana juyayi ga aukuwar bala’in girgizar kasa a jihar Xizang. Yana mai jinjinawa matakin ceto kan lokaci da gwamnatin Sin ta dauka.

Har ila yau a dai jiyan, Wang Yi ya yi shawarwari da takwaransa na Najeriya Yusuf Tuggar da kuma ganawa da manema labarai tare. (Amina Xu)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rahoto : Kasar Sin Ta Samu Karuwar Baje Kolin Masana’antu Da Fasahohi A Shekarar 2024

Next Post

Kasar Sin Ta Ba Da Rahoton Karuwar Kamfanoni Masu Kasuwanci

Related

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

12 hours ago
Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya
Daga Birnin Sin

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

13 hours ago
Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

14 hours ago
Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

15 hours ago
An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025

16 hours ago
Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

17 hours ago
Next Post
Kasar Sin Ta Ba Da Rahoton Karuwar Kamfanoni Masu Kasuwanci

Kasar Sin Ta Ba Da Rahoton Karuwar Kamfanoni Masu Kasuwanci

LABARAI MASU NASABA

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

September 15, 2025
Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

September 15, 2025
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

September 14, 2025
Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

September 14, 2025
Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

September 14, 2025
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

September 14, 2025
Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

September 14, 2025
Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.