• English
  • Business News
Wednesday, June 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bola Tinubu Ya Gana Da Wang Yi

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Bola Tinubu Ya Gana Da Wang Yi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasar Najeirya Bola Tinubu, ya gana da ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi a jiya Alhamis 9 ga wata, a birnin Abuja, fadar mulkin Najeriya.

Yayin ganawar tasu, Wang Yi ya isar da gaisuwa da kyakkyawan fatan sabuwar shekara daga shugaban kasar Sin Xi Jinping zuwa shugaban Najeriya. Ya ce, mai girma shugaba Tinubu ya kammala ziyarar aikinsa a kasar Sin cikin watan Satumban bara, inda shi da shugaba Xi Jinping suka sanar da raya huldar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a duk fannoni, don tabbatar da raya huldar kasashen biyu zuwa wani sabon mataki.

  • Xi Jinping Ya Amsa Wasikar Da Wasu Matasa ’Yan Wasan Peking Opera Suka Aika Masa
  • Alkaluman Hauhawar Farashi Na Sin Sun Karu Da Kaso 0.2% A 2024

Ya ce huldar dake tsakanin Sin da Najeriya misali ce ta ingantacciyar huldar Sin da kasashen Afirka, kuma ta wuce hulda tsakanin kasashen biyu, kamata ya yi bangarorin biyu sun kara hadin gwiwarsu don raya kyakkyawar makomar al’ummun kasashen biyu a dukkan fannoni a sabon zamani, da samar da abin koyi ga hadin kan kasashe masu tasowa da saurin bunkasuwa.

Wang Yi ya jinjinawa matsayin da Najeriya ke kai, na nacewa ga manufar “kasar Sin daya tak a duniya”, kuma Sin na goyon bayan Najeriya da ta bi hanyar raya kai bisa halayenta, da mara mata baya ga aikin yaki da ta’addanci, da kiyaye zaman lafiya, da kwanciyar hankali a wannan yanki, da kara mata kwarin gwiwar taka karin rawarta a duniya.

A nasa bangaren, shugaba Tinubu ya isar da sahihiyar gaisuwarsa ta bakin Wang Yi ga shugaba Xi Jinping. Ya ce, Najeriya ta dora muhimmanci matuka kan huldar kasashen biyu, kuma tabbatar da ci gaban da aka samu a taron koli na dandalin tattauna hadin kan Sin da Afirka, na da ma’ana sosai ga bunkasar kasarsa. Ya ce, Sin na da ingantaciyyar kima a duniya, kuma yana fatan Sin za ta ci gaba da goyawa Najeriya baya don ta kara taka rawa a cikin harkokin duniya.

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Da Ya Sa Sin Ta Samu Bunkasar Tattalin Arziki Mai Dorewa Duk Da Kalubalolin Da Ake Fuskanta A Duniya

Xi Da Shugabannin Kasashe 5 Na Tsakiyar Asiya Sun Halarci Bikin Rattaba Hannu

Ban da wannan kuma, shugaba Tinubu ya bayyana juyayi ga aukuwar bala’in girgizar kasa a jihar Xizang. Yana mai jinjinawa matakin ceto kan lokaci da gwamnatin Sin ta dauka.

Har ila yau a dai jiyan, Wang Yi ya yi shawarwari da takwaransa na Najeriya Yusuf Tuggar da kuma ganawa da manema labarai tare. (Amina Xu)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rahoto : Kasar Sin Ta Samu Karuwar Baje Kolin Masana’antu Da Fasahohi A Shekarar 2024

Next Post

Kasar Sin Ta Ba Da Rahoton Karuwar Kamfanoni Masu Kasuwanci

Related

Dalilin Da Ya Sa Sin Ta Samu Bunkasar Tattalin Arziki Mai Dorewa Duk Da Kalubalolin Da Ake Fuskanta A Duniya
Daga Birnin Sin

Dalilin Da Ya Sa Sin Ta Samu Bunkasar Tattalin Arziki Mai Dorewa Duk Da Kalubalolin Da Ake Fuskanta A Duniya

15 hours ago
Xi Da Shugabannin Kasashe 5 Na Tsakiyar Asiya Sun Halarci Bikin Rattaba Hannu
Daga Birnin Sin

Xi Da Shugabannin Kasashe 5 Na Tsakiyar Asiya Sun Halarci Bikin Rattaba Hannu

17 hours ago
Sin Ta Cimma Sabuwar Nasarar Bincike Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Sin Ta Cimma Sabuwar Nasarar Bincike Duniyar Wata

17 hours ago
An Gudanar Da Bikin Mu’amalar Jama’a Da Al’adu A Tsakanin Sin Da Tsakiyar Asiya A Astana
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Bikin Mu’amalar Jama’a Da Al’adu A Tsakanin Sin Da Tsakiyar Asiya A Astana

19 hours ago
Masu Karanta Adabin Shafin Intanet Na Sin Sun Kai Miliyan 575
Daga Birnin Sin

Masu Karanta Adabin Shafin Intanet Na Sin Sun Kai Miliyan 575

21 hours ago
Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53

21 hours ago
Next Post
Kasar Sin Ta Ba Da Rahoton Karuwar Kamfanoni Masu Kasuwanci

Kasar Sin Ta Ba Da Rahoton Karuwar Kamfanoni Masu Kasuwanci

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Kai Ziyara Benuwe Sakamakon Kisan Kiyashi Da Aka Yi Wa Jama’a

Tinubu Ya Kai Ziyara Benuwe Sakamakon Kisan Kiyashi Da Aka Yi Wa Jama’a

June 18, 2025
PDP Ta Yi Satar Amsa Daga Manufofin Buhari – Tinubu

Gwamnatin Tarayya Za Ta Kwaso ‘Yan Nijeriya Da Suka Maƙale A Isra’ila Da Iran

June 18, 2025
An Ɗaure Wani Mutum Wata 6 Kan Satar Takalma A Masallaci A Kaduna

An Ɗaure Wani Mutum Wata 6 Kan Satar Takalma A Masallaci A Kaduna

June 18, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama

June 18, 2025
Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 

Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 

June 18, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sin Ta Samu Bunkasar Tattalin Arziki Mai Dorewa Duk Da Kalubalolin Da Ake Fuskanta A Duniya

Dalilin Da Ya Sa Sin Ta Samu Bunkasar Tattalin Arziki Mai Dorewa Duk Da Kalubalolin Da Ake Fuskanta A Duniya

June 17, 2025
An Kama Mutane 26 Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Kogi

An Kama Mutane 26 Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Kogi

June 17, 2025
Xi Da Shugabannin Kasashe 5 Na Tsakiyar Asiya Sun Halarci Bikin Rattaba Hannu

Xi Da Shugabannin Kasashe 5 Na Tsakiyar Asiya Sun Halarci Bikin Rattaba Hannu

June 17, 2025
Sin Ta Cimma Sabuwar Nasarar Bincike Duniyar Wata

Sin Ta Cimma Sabuwar Nasarar Bincike Duniyar Wata

June 17, 2025
Majalisar Wakilai Ta Fara Binciken Yadda Aka Raba Naira Tiriliyan 1.12 Kan Shirin Lamuni Ga Manoma Da Masana’antu

Majalisar Wakilai Ta Fara Binciken Yadda Aka Raba Naira Tiriliyan 1.12 Kan Shirin Lamuni Ga Manoma Da Masana’antu

June 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.