• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bola Tinubu Ya Gana Da Wang Yi

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Bola Tinubu Ya Gana Da Wang Yi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasar Najeirya Bola Tinubu, ya gana da ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi a jiya Alhamis 9 ga wata, a birnin Abuja, fadar mulkin Najeriya.

Yayin ganawar tasu, Wang Yi ya isar da gaisuwa da kyakkyawan fatan sabuwar shekara daga shugaban kasar Sin Xi Jinping zuwa shugaban Najeriya. Ya ce, mai girma shugaba Tinubu ya kammala ziyarar aikinsa a kasar Sin cikin watan Satumban bara, inda shi da shugaba Xi Jinping suka sanar da raya huldar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a duk fannoni, don tabbatar da raya huldar kasashen biyu zuwa wani sabon mataki.

  • Xi Jinping Ya Amsa Wasikar Da Wasu Matasa ’Yan Wasan Peking Opera Suka Aika Masa
  • Alkaluman Hauhawar Farashi Na Sin Sun Karu Da Kaso 0.2% A 2024

Ya ce huldar dake tsakanin Sin da Najeriya misali ce ta ingantacciyar huldar Sin da kasashen Afirka, kuma ta wuce hulda tsakanin kasashen biyu, kamata ya yi bangarorin biyu sun kara hadin gwiwarsu don raya kyakkyawar makomar al’ummun kasashen biyu a dukkan fannoni a sabon zamani, da samar da abin koyi ga hadin kan kasashe masu tasowa da saurin bunkasuwa.

Wang Yi ya jinjinawa matsayin da Najeriya ke kai, na nacewa ga manufar “kasar Sin daya tak a duniya”, kuma Sin na goyon bayan Najeriya da ta bi hanyar raya kai bisa halayenta, da mara mata baya ga aikin yaki da ta’addanci, da kiyaye zaman lafiya, da kwanciyar hankali a wannan yanki, da kara mata kwarin gwiwar taka karin rawarta a duniya.

A nasa bangaren, shugaba Tinubu ya isar da sahihiyar gaisuwarsa ta bakin Wang Yi ga shugaba Xi Jinping. Ya ce, Najeriya ta dora muhimmanci matuka kan huldar kasashen biyu, kuma tabbatar da ci gaban da aka samu a taron koli na dandalin tattauna hadin kan Sin da Afirka, na da ma’ana sosai ga bunkasar kasarsa. Ya ce, Sin na da ingantaciyyar kima a duniya, kuma yana fatan Sin za ta ci gaba da goyawa Najeriya baya don ta kara taka rawa a cikin harkokin duniya.

Labarai Masu Nasaba

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Ban da wannan kuma, shugaba Tinubu ya bayyana juyayi ga aukuwar bala’in girgizar kasa a jihar Xizang. Yana mai jinjinawa matakin ceto kan lokaci da gwamnatin Sin ta dauka.

Har ila yau a dai jiyan, Wang Yi ya yi shawarwari da takwaransa na Najeriya Yusuf Tuggar da kuma ganawa da manema labarai tare. (Amina Xu)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rahoto : Kasar Sin Ta Samu Karuwar Baje Kolin Masana’antu Da Fasahohi A Shekarar 2024

Next Post

Kasar Sin Ta Ba Da Rahoton Karuwar Kamfanoni Masu Kasuwanci

Related

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?
Daga Birnin Sin

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

15 hours ago
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

16 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

18 hours ago
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

18 hours ago
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya
Daga Birnin Sin

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

20 hours ago
Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC
Daga Birnin Sin

Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

21 hours ago
Next Post
Kasar Sin Ta Ba Da Rahoton Karuwar Kamfanoni Masu Kasuwanci

Kasar Sin Ta Ba Da Rahoton Karuwar Kamfanoni Masu Kasuwanci

LABARAI MASU NASABA

Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hukumar NRC Ta Dakatar Da Zirga-zirgar Jiragen Kasa Na Abuja zuwa Kaduna

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.