ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bola Tinubu Ya Gana Da Wang Yi

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Wang yi

Shugaban kasar Najeirya Bola Tinubu, ya gana da ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi a jiya Alhamis 9 ga wata, a birnin Abuja, fadar mulkin Najeriya.

Yayin ganawar tasu, Wang Yi ya isar da gaisuwa da kyakkyawan fatan sabuwar shekara daga shugaban kasar Sin Xi Jinping zuwa shugaban Najeriya. Ya ce, mai girma shugaba Tinubu ya kammala ziyarar aikinsa a kasar Sin cikin watan Satumban bara, inda shi da shugaba Xi Jinping suka sanar da raya huldar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a duk fannoni, don tabbatar da raya huldar kasashen biyu zuwa wani sabon mataki.

  • Xi Jinping Ya Amsa Wasikar Da Wasu Matasa ’Yan Wasan Peking Opera Suka Aika Masa
  • Alkaluman Hauhawar Farashi Na Sin Sun Karu Da Kaso 0.2% A 2024

Ya ce huldar dake tsakanin Sin da Najeriya misali ce ta ingantacciyar huldar Sin da kasashen Afirka, kuma ta wuce hulda tsakanin kasashen biyu, kamata ya yi bangarorin biyu sun kara hadin gwiwarsu don raya kyakkyawar makomar al’ummun kasashen biyu a dukkan fannoni a sabon zamani, da samar da abin koyi ga hadin kan kasashe masu tasowa da saurin bunkasuwa.

ADVERTISEMENT

Wang Yi ya jinjinawa matsayin da Najeriya ke kai, na nacewa ga manufar “kasar Sin daya tak a duniya”, kuma Sin na goyon bayan Najeriya da ta bi hanyar raya kai bisa halayenta, da mara mata baya ga aikin yaki da ta’addanci, da kiyaye zaman lafiya, da kwanciyar hankali a wannan yanki, da kara mata kwarin gwiwar taka karin rawarta a duniya.

A nasa bangaren, shugaba Tinubu ya isar da sahihiyar gaisuwarsa ta bakin Wang Yi ga shugaba Xi Jinping. Ya ce, Najeriya ta dora muhimmanci matuka kan huldar kasashen biyu, kuma tabbatar da ci gaban da aka samu a taron koli na dandalin tattauna hadin kan Sin da Afirka, na da ma’ana sosai ga bunkasar kasarsa. Ya ce, Sin na da ingantaciyyar kima a duniya, kuma yana fatan Sin za ta ci gaba da goyawa Najeriya baya don ta kara taka rawa a cikin harkokin duniya.

LABARAI MASU NASABA

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Ban da wannan kuma, shugaba Tinubu ya bayyana juyayi ga aukuwar bala’in girgizar kasa a jihar Xizang. Yana mai jinjinawa matakin ceto kan lokaci da gwamnatin Sin ta dauka.

Har ila yau a dai jiyan, Wang Yi ya yi shawarwari da takwaransa na Najeriya Yusuf Tuggar da kuma ganawa da manema labarai tare. (Amina Xu)

 

Wang yi
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Wang yi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy
  • Sulaiman
    “Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa
  • Sulaiman
    Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya
  • Sulaiman
    Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

MASU ALAKA

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa
Daga Birnin Sin

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya
Daga Birnin Sin

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026
Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa

September 9, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Ba Da Rahoton Karuwar Kamfanoni Masu Kasuwanci

Kasar Sin Ta Ba Da Rahoton Karuwar Kamfanoni Masu Kasuwanci

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026
Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.