• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

BRICS Ta Bi Sahun Sassan Dake Neman Kawo Karshen Rikicin Isra’ila Da Palasdinu

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
BRICS Ta Bi Sahun Sassan Dake Neman Kawo Karshen Rikicin Isra’ila Da Palasdinu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da yammacin jiya ne shugabannin kungiyar BRICS suka kira taron musamman kan batun Palasdinu da Isra’ila. Wannan ganawa na zuwa ne bayan wani muhimmin taron ministocin harkokin wajen kasashen Larabawa da na musulmi da kasar Sin ta jagoranta da nufin kawo karshen rikicin Israila da Palasdinu, ta yadda daga karshe za a kai ga tabbatar da zaman lafiya a yankin Gabas ta Tsakiya.

A jawabin da ya gabatar yayin taron shugabannin na BRICS ta kafar bidiyo daga birnin Beijing, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana cewa, bisa la’akari da yanayin da ake ciki, ya zama wajibi kasashen BRICS su nemi a tabbatar da adalci da zaman lafiya kan batun Palasdinu da Isra’ila.

  • Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Na Wucin Gadi Tsakanin Palasdinu Da Isra’ila 
  • Xi Jinping Ya Gana Da Takwaransa Na Uruguay

Abu mafi dacewa na kawo karshen rikicin da yaki-ci-yaki-cinyewa tsakanin Palasdinu da Isra’ila shi ne, aiwatar da shirin nan na “kafa kasashe biyu masu ’yancin cin gashin kai”, da dawo da halaltattun hakkokin Palasdinu da kafa kasar Palasdinu mai cin gashin kanta.

Shugaba Xi ya ce, idan har ba a warware matsalar bisa adalci ba, to, ba za a taba samun zaman lafiya da kwanciyar hankali mai dorewa a yankin Gabas ta Tsakiya ba.
Galibin shugabannin kungiyar da suka yi jawabi, sun bayyana bukatar mutunta yarjejeniyar tsagaida bude wuta da sassan biyu suka cimma, wadda za ta kai ga sakin wadanda sassan biyu ke rike da su.

Kan haka shugaba Xi ya gabatar da shawarwari 3, inda ya yi kira da a dakatar da bude wuta domin cimma zaman lafiya da tsaro mai dorewa. Kuma dukkan bangarori masu rikici su dakatar da bude wuta da duk wani nau’i na rikici da kai hari kan fararen hula, a saki fararen hular da ake tsare da su domin kaucewa karuwar asarar rayuka da wahalhalu, a tabbatar da isar da kayayyakin agaji ba tare da tangarda ba da fadada ayyukan agajin jin kai ga mutanen Gaza da dakatar da tilasta musu kaura da katse wuta da ruwa da mai da ake wa al’ummar Gaza a matsayin hukunci na gama gari.

Labarai Masu Nasaba

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

Masana na kira ga kasashen duniya da su dauki kwararan matakai domin kaucewa tsanantar rikicin da bazuwar tasirinsa kan baki dayan yankin Gabas ta Tsakiya.

Baya ga wadannan muhimman taruka, shi ma babban sakataren MDD Anthony Guterres, ya bukaci da a kai zuciya nesa a mutunta dokoki da ka’idojin jin kai da bukatar kare rayukan fararen hula da kaucewa tsanantar rikici, ta yadda za a kai ga tabbatar da zaman lafiya a yankin baki daya. Wannan ya kara nuna muhimmancin wanzar da zaman lafiya a duniya maimakon yin fito na fito. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaIsra'ilaSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Na Wucin Gadi Tsakanin Palasdinu Da Isra’ila 

Next Post

Labarin Rasuwar Janar CG Musa Ba Gaskiya Ba Ne – Rundunar Tsaron Nijeriya

Related

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu
Daga Birnin Sin

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

2 hours ago
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan
Daga Birnin Sin

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

3 hours ago
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

4 hours ago
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

5 hours ago
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

6 hours ago
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”
Daga Birnin Sin

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

7 hours ago
Next Post
Labarin Rasuwar Janar CG Musa Ba Gaskiya Ba Ne – Rundunar Tsaron Nijeriya

Labarin Rasuwar Janar CG Musa Ba Gaskiya Ba Ne - Rundunar Tsaron Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

September 19, 2025
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

September 19, 2025
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

September 19, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
BRICS

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.