• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

BRICS Ta Bi Sahun Sassan Dake Neman Kawo Karshen Rikicin Isra’ila Da Palasdinu

by CGTN Hausa
2 years ago
BRICS

Da yammacin jiya ne shugabannin kungiyar BRICS suka kira taron musamman kan batun Palasdinu da Isra’ila. Wannan ganawa na zuwa ne bayan wani muhimmin taron ministocin harkokin wajen kasashen Larabawa da na musulmi da kasar Sin ta jagoranta da nufin kawo karshen rikicin Israila da Palasdinu, ta yadda daga karshe za a kai ga tabbatar da zaman lafiya a yankin Gabas ta Tsakiya.

A jawabin da ya gabatar yayin taron shugabannin na BRICS ta kafar bidiyo daga birnin Beijing, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana cewa, bisa la’akari da yanayin da ake ciki, ya zama wajibi kasashen BRICS su nemi a tabbatar da adalci da zaman lafiya kan batun Palasdinu da Isra’ila.

  • Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Na Wucin Gadi Tsakanin Palasdinu Da Isra’ila 
  • Xi Jinping Ya Gana Da Takwaransa Na Uruguay

Abu mafi dacewa na kawo karshen rikicin da yaki-ci-yaki-cinyewa tsakanin Palasdinu da Isra’ila shi ne, aiwatar da shirin nan na “kafa kasashe biyu masu ’yancin cin gashin kai”, da dawo da halaltattun hakkokin Palasdinu da kafa kasar Palasdinu mai cin gashin kanta.

Shugaba Xi ya ce, idan har ba a warware matsalar bisa adalci ba, to, ba za a taba samun zaman lafiya da kwanciyar hankali mai dorewa a yankin Gabas ta Tsakiya ba.
Galibin shugabannin kungiyar da suka yi jawabi, sun bayyana bukatar mutunta yarjejeniyar tsagaida bude wuta da sassan biyu suka cimma, wadda za ta kai ga sakin wadanda sassan biyu ke rike da su.

Kan haka shugaba Xi ya gabatar da shawarwari 3, inda ya yi kira da a dakatar da bude wuta domin cimma zaman lafiya da tsaro mai dorewa. Kuma dukkan bangarori masu rikici su dakatar da bude wuta da duk wani nau’i na rikici da kai hari kan fararen hula, a saki fararen hular da ake tsare da su domin kaucewa karuwar asarar rayuka da wahalhalu, a tabbatar da isar da kayayyakin agaji ba tare da tangarda ba da fadada ayyukan agajin jin kai ga mutanen Gaza da dakatar da tilasta musu kaura da katse wuta da ruwa da mai da ake wa al’ummar Gaza a matsayin hukunci na gama gari.

LABARAI MASU NASABA

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Masana na kira ga kasashen duniya da su dauki kwararan matakai domin kaucewa tsanantar rikicin da bazuwar tasirinsa kan baki dayan yankin Gabas ta Tsakiya.

Baya ga wadannan muhimman taruka, shi ma babban sakataren MDD Anthony Guterres, ya bukaci da a kai zuciya nesa a mutunta dokoki da ka’idojin jin kai da bukatar kare rayukan fararen hula da kaucewa tsanantar rikici, ta yadda za a kai ga tabbatar da zaman lafiya a yankin baki daya. Wannan ya kara nuna muhimmancin wanzar da zaman lafiya a duniya maimakon yin fito na fito. (Ibrahim Yaya)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya
Daga Birnin Sin

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103
Daga Birnin Sin

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Next Post
Labarin Rasuwar Janar CG Musa Ba Gaskiya Ba Ne – Rundunar Tsaron Nijeriya

Labarin Rasuwar Janar CG Musa Ba Gaskiya Ba Ne - Rundunar Tsaron Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.