• English
  • Business News
Thursday, May 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

BUƊA-BAKI [Falalarsa Da Lokacinsa] Na 1

by Nuhu Ubale Ibrahim
1 year ago
in Bakon Marubuci, Fatawa, Ilimi
0
BUƊA-BAKI [Falalarsa Da Lokacinsa] Na 1
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Allah Ta’ala Yana cewa: “Kuma ku ci ku sha, har farin zare ya bayyana a gare ku daga baƙin zare na alfijir, sa’an nan kuma ku cika azumi zuwa dare” Suratul Baƙara aya ta 187.

Wannan aya ta bayyana mana lokacin da azumi yake tuƙewa, watau dare. Dare kuma yana shiga ne daga lokacin da rana ta faɗi. Saboda haka azumi yana ƙarewa ne da shigar dare. An karɓo hadisi daga Umar ɗan Khaɗɗabi Allah ya ƙara yarda a gare shi ya ce: Manzon Allah (S.A.W) ya ce:” Idan dare ya fuskanto, yini kuma ya juya baya, rana kuma ta faɗi, to, lokacin sha ruwa ya yi” Bukhari[#1954] da Muslim [#1100].

  • BUƊA-BAKI [Falalarsa Da Lokacinsa] Na 2
  • BUƊA-BAKI [Falalarsa Da Lokacinsa] Na 3

Gaggauta Buɗa-Baki: Akwai hadisai da suka tabbatar da haka;

1. An karbo hadisi daga Sahalu dan Sa’adu, Allah Ya ƙara yarda a gare shi. Lalle Manzon Allah (S.A.W) ya ce:” Mutane ba za su gushe ba cikin alheri matuƙar suna gaggauta buɗa-baki” Bukhari [#1957] da Muslim [#1098]

2. An karbo hadisi daga Abu Huraira Allah ya ƙara yarda a gare shi, daga Annabi (S.A.W) ya ce:” Addini ba zai gushe ba yana yin rinjaye da galaba ba, matuƙar mutane suna gaggauta buɗa baki. Ku gaggauta buɗa-baki, domin Yahudu da Nasara suna jirkinta shi” Hadisi ne mai kyau Abu Dawud [#2353] da Ibnu Maja [#1689] da Ahmad [#9810] da Ibnu Abi Shaiba [#8944].

Labarai Masu Nasaba

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (2)

Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3

Imam an-Nawawi Allah ya yi masa rahama yana cewa: “A cikin wannan hadisi akwai zaburarwa a kan gaggauta buɗa-baki bayan an tabbatar da fuɗuwar rana, kuma al’amarin al’ummar Musulmi ba zai gushe ba cikin tsari da alheri matuƙar suka kasance suna tsare wannan sunna, idan kuma suka jirkinta yin buɗa-baki, to , alama ce da take nuna za su faɗa cikin wani tasku” an-Nawawi; al-Minhaju Sharhu Sahihi Muslim [7/206] . Ibnu Hajar Allah ya yi masa rahama ya ce: “Addini ya yi galaba da rinjaye yana lazimta wanzuwar alheri” Fathul Bãri [4/555].

Abul Walid al-Baji Allah ya yi masa rahama ya ce: “Mutane ba za su gushe ba game da addininsu suna cikin alheri matuƙar suna gaggauta buɗa-baki a bisa tafarki na sunna. Gaggauta buɗa-baki shi ne kada a yi jinkirin shan ruwa bayan rana ta faɗi domin nuna kai maƙura da matuƙa wajen ibada da ƙudurce cewa azumi bai yi ba idan aka sha ruwa bayan rana ta faɗi…” al-Baji; al-Muntaƙã Aharhul Muwaɗɗã [2/42].

Hukuncin Gaggauta Buɗa-baki:
Mustahabbi ne mai azumi ya gaggauta buɗa-baki bayan ya tabbar da rana ta faɗi. Duba al-Ƙadi Abdulwahab; al-Ma’unatu [1/347] da Ibnu Ƙudama; al-Muguni [3/174], da Ishaƙ bin Mansur; Masa’ilul Imami Ahmad wa Iahaƙ bin Rahuya [3/1224].

Yana daga cikin sunna gaggauta buɗa-baki. duba Ibu Abi Zaid al-Ƙairawani, ar-Risalatu [shafi na 83] da Ibni Abdilbarri; al-Kafi [1/350] da al-Ƙarafi; az-Zakhiratu [2/510] da Muhd. Binu Yusuf; at-Taju wal-Iklilu [3/304].


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AzumiBUƊA-BAKIRamadan
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dokar Masana’antar Fetur (PIB): Yadda Aka Yi Wa Kudin Man Fetur Kofar-raggo A Nijeriya

Next Post

Yadda Magidanta, Samari Da ‘Yan Mata Za Su Daidaita Rayuwarsu A Azumin Bana

Related

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (2)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (2)

5 days ago
Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3
Ilimi

Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3

6 days ago
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)
Bakon Marubuci

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)

6 days ago
Tarihin Makarantar Katsina-kwalej Zuwa Ta Horon Malamai (1)
Ilimi

Tarihin Makarantar Katsina-kwalej Zuwa Ta Horon Malamai (1)

2 weeks ago
Hanyoyin Kare kai Ga Ɗalibai Da Ke Makarantun Kwana
Ilimi

Hanyoyin Kare kai Ga Ɗalibai Da Ke Makarantun Kwana

2 weeks ago
Kyakkyawan Tunanin Kwankwaso Na Kafa Jami’ar Kimiyya Ta Wudil Ta Zama Alkairi Ga Al’umma – Alhaji Abdukadir
Ilimi

Kyakkyawan Tunanin Kwankwaso Na Kafa Jami’ar Kimiyya Ta Wudil Ta Zama Alkairi Ga Al’umma – Alhaji Abdukadir

2 weeks ago
Next Post
Yadda Magidanta, Samari Da ‘Yan Mata Za Su Daidaita Rayuwarsu A Azumin Bana

Yadda Magidanta, Samari Da ‘Yan Mata Za Su Daidaita Rayuwarsu A Azumin Bana

LABARAI MASU NASABA

Zaman lafiya

MDD Ta Gudanar Da Bikin Ranar Tunawa Da Dakarun Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Duniya Ta 2025

May 29, 2025
Buhari Ya Yabi Tinubu, Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Rage Tsammani Da Dogon Buri

Buhari Ya Yabi Tinubu, Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Rage Tsammani Da Dogon Buri

May 29, 2025
Gwamnatin Kano Ta Fara Biyan Tsoffin Kansiloli Na APC Sama Da Naira Biliyan 16

Gwamnatin Kano Ta Fara Biyan Tsoffin Kansiloli Na APC Sama Da Naira Biliyan 16

May 29, 2025
Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Har Da Na Amurka 

Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Har Da Na Amurka 

May 28, 2025
Miƙa Mulki Daga Buhari Zuwa Tinubu: Abubuwan Da Suka Fi Jan Hankali

Tinubu Ya Yi Ƙoƙari, Gyaran Nijeriya Aikin Kowa Da Kowa Ne – Buhari

May 28, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Yankin Turai Na Kara Kawo Haske Ga Tattalin Arzikin Duniya

Hadin Gwiwar Sin Da Yankin Turai Na Kara Kawo Haske Ga Tattalin Arzikin Duniya

May 28, 2025
Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

May 28, 2025
Yunkurin Philippines Bai Kai Gaci Ba A Tekun Kudancin Kasar Sin 

Yunkurin Philippines Bai Kai Gaci Ba A Tekun Kudancin Kasar Sin 

May 28, 2025
Babu Wata Sauran Mafaka Ga ‘Yan Ta’adda, In Ji Shugaban Rundunar Sojin Sama

Babu Wata Sauran Mafaka Ga ‘Yan Ta’adda, In Ji Shugaban Rundunar Sojin Sama

May 28, 2025
Kamfanoni Mallakin Gwamnatin Sin Sun Samu Bunkasa Bisa Daidaito Cikin Watanni Hudu Na Farkon Bana

Kamfanoni Mallakin Gwamnatin Sin Sun Samu Bunkasa Bisa Daidaito Cikin Watanni Hudu Na Farkon Bana

May 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.