• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

BUƊA-BAKI [Falalarsa Da Lokacinsa] Na 1

by Nuhu Ubale Ibrahim
1 year ago
in Bakon Marubuci, Fatawa, Ilimi
0
BUƊA-BAKI [Falalarsa Da Lokacinsa] Na 1
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Allah Ta’ala Yana cewa: “Kuma ku ci ku sha, har farin zare ya bayyana a gare ku daga baƙin zare na alfijir, sa’an nan kuma ku cika azumi zuwa dare” Suratul Baƙara aya ta 187.

Wannan aya ta bayyana mana lokacin da azumi yake tuƙewa, watau dare. Dare kuma yana shiga ne daga lokacin da rana ta faɗi. Saboda haka azumi yana ƙarewa ne da shigar dare. An karɓo hadisi daga Umar ɗan Khaɗɗabi Allah ya ƙara yarda a gare shi ya ce: Manzon Allah (S.A.W) ya ce:” Idan dare ya fuskanto, yini kuma ya juya baya, rana kuma ta faɗi, to, lokacin sha ruwa ya yi” Bukhari[#1954] da Muslim [#1100].

  • BUƊA-BAKI [Falalarsa Da Lokacinsa] Na 2
  • BUƊA-BAKI [Falalarsa Da Lokacinsa] Na 3

Gaggauta Buɗa-Baki: Akwai hadisai da suka tabbatar da haka;

1. An karbo hadisi daga Sahalu dan Sa’adu, Allah Ya ƙara yarda a gare shi. Lalle Manzon Allah (S.A.W) ya ce:” Mutane ba za su gushe ba cikin alheri matuƙar suna gaggauta buɗa-baki” Bukhari [#1957] da Muslim [#1098]

2. An karbo hadisi daga Abu Huraira Allah ya ƙara yarda a gare shi, daga Annabi (S.A.W) ya ce:” Addini ba zai gushe ba yana yin rinjaye da galaba ba, matuƙar mutane suna gaggauta buɗa baki. Ku gaggauta buɗa-baki, domin Yahudu da Nasara suna jirkinta shi” Hadisi ne mai kyau Abu Dawud [#2353] da Ibnu Maja [#1689] da Ahmad [#9810] da Ibnu Abi Shaiba [#8944].

Labarai Masu Nasaba

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

Imam an-Nawawi Allah ya yi masa rahama yana cewa: “A cikin wannan hadisi akwai zaburarwa a kan gaggauta buɗa-baki bayan an tabbatar da fuɗuwar rana, kuma al’amarin al’ummar Musulmi ba zai gushe ba cikin tsari da alheri matuƙar suka kasance suna tsare wannan sunna, idan kuma suka jirkinta yin buɗa-baki, to , alama ce da take nuna za su faɗa cikin wani tasku” an-Nawawi; al-Minhaju Sharhu Sahihi Muslim [7/206] . Ibnu Hajar Allah ya yi masa rahama ya ce: “Addini ya yi galaba da rinjaye yana lazimta wanzuwar alheri” Fathul Bãri [4/555].

Abul Walid al-Baji Allah ya yi masa rahama ya ce: “Mutane ba za su gushe ba game da addininsu suna cikin alheri matuƙar suna gaggauta buɗa-baki a bisa tafarki na sunna. Gaggauta buɗa-baki shi ne kada a yi jinkirin shan ruwa bayan rana ta faɗi domin nuna kai maƙura da matuƙa wajen ibada da ƙudurce cewa azumi bai yi ba idan aka sha ruwa bayan rana ta faɗi…” al-Baji; al-Muntaƙã Aharhul Muwaɗɗã [2/42].

Hukuncin Gaggauta Buɗa-baki:
Mustahabbi ne mai azumi ya gaggauta buɗa-baki bayan ya tabbar da rana ta faɗi. Duba al-Ƙadi Abdulwahab; al-Ma’unatu [1/347] da Ibnu Ƙudama; al-Muguni [3/174], da Ishaƙ bin Mansur; Masa’ilul Imami Ahmad wa Iahaƙ bin Rahuya [3/1224].

Yana daga cikin sunna gaggauta buɗa-baki. duba Ibu Abi Zaid al-Ƙairawani, ar-Risalatu [shafi na 83] da Ibni Abdilbarri; al-Kafi [1/350] da al-Ƙarafi; az-Zakhiratu [2/510] da Muhd. Binu Yusuf; at-Taju wal-Iklilu [3/304].


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AzumiBUƊA-BAKIRamadan
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dokar Masana’antar Fetur (PIB): Yadda Aka Yi Wa Kudin Man Fetur Kofar-raggo A Nijeriya

Next Post

Yadda Magidanta, Samari Da ‘Yan Mata Za Su Daidaita Rayuwarsu A Azumin Bana

Related

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

15 hours ago
Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan
Bakon Marubuci

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

2 days ago
Hoton Kwankwaso da Ganduje da Shekarau
Bakon Marubuci

Daga Sawaba Zuwa Asara: Baje Kolin Kasuwancin Siyasa A Kano – Auwalu Anwar

4 days ago
Kungiyoyi Masu Fada Aji Kan Harkar Ilimi Sun Nemi A Yi Wa Sashen Kwaskwarima
Ilimi

Kungiyoyi Masu Fada Aji Kan Harkar Ilimi Sun Nemi A Yi Wa Sashen Kwaskwarima

1 week ago
Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata
Bakon Marubuci

Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata

1 week ago
Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah
Ilimi

Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

3 weeks ago
Next Post
Yadda Magidanta, Samari Da ‘Yan Mata Za Su Daidaita Rayuwarsu A Azumin Bana

Yadda Magidanta, Samari Da ‘Yan Mata Za Su Daidaita Rayuwarsu A Azumin Bana

LABARAI MASU NASABA

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.