ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

BUƊA-BAKI [Falalarsa Da Lokacinsa] Na 1

by Nuhu Ubale Ibrahim
2 years ago
Buda

Allah Ta’ala Yana cewa: “Kuma ku ci ku sha, har farin zare ya bayyana a gare ku daga baƙin zare na alfijir, sa’an nan kuma ku cika azumi zuwa dare” Suratul Baƙara aya ta 187.

Wannan aya ta bayyana mana lokacin da azumi yake tuƙewa, watau dare. Dare kuma yana shiga ne daga lokacin da rana ta faɗi. Saboda haka azumi yana ƙarewa ne da shigar dare. An karɓo hadisi daga Umar ɗan Khaɗɗabi Allah ya ƙara yarda a gare shi ya ce: Manzon Allah (S.A.W) ya ce:” Idan dare ya fuskanto, yini kuma ya juya baya, rana kuma ta faɗi, to, lokacin sha ruwa ya yi” Bukhari[#1954] da Muslim [#1100].

  • BUƊA-BAKI [Falalarsa Da Lokacinsa] Na 2
  • BUƊA-BAKI [Falalarsa Da Lokacinsa] Na 3

Gaggauta Buɗa-Baki: Akwai hadisai da suka tabbatar da haka;

ADVERTISEMENT

1. An karbo hadisi daga Sahalu dan Sa’adu, Allah Ya ƙara yarda a gare shi. Lalle Manzon Allah (S.A.W) ya ce:” Mutane ba za su gushe ba cikin alheri matuƙar suna gaggauta buɗa-baki” Bukhari [#1957] da Muslim [#1098]

2. An karbo hadisi daga Abu Huraira Allah ya ƙara yarda a gare shi, daga Annabi (S.A.W) ya ce:” Addini ba zai gushe ba yana yin rinjaye da galaba ba, matuƙar mutane suna gaggauta buɗa baki. Ku gaggauta buɗa-baki, domin Yahudu da Nasara suna jirkinta shi” Hadisi ne mai kyau Abu Dawud [#2353] da Ibnu Maja [#1689] da Ahmad [#9810] da Ibnu Abi Shaiba [#8944].

LABARAI MASU NASABA

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki

Imam an-Nawawi Allah ya yi masa rahama yana cewa: “A cikin wannan hadisi akwai zaburarwa a kan gaggauta buɗa-baki bayan an tabbatar da fuɗuwar rana, kuma al’amarin al’ummar Musulmi ba zai gushe ba cikin tsari da alheri matuƙar suka kasance suna tsare wannan sunna, idan kuma suka jirkinta yin buɗa-baki, to , alama ce da take nuna za su faɗa cikin wani tasku” an-Nawawi; al-Minhaju Sharhu Sahihi Muslim [7/206] . Ibnu Hajar Allah ya yi masa rahama ya ce: “Addini ya yi galaba da rinjaye yana lazimta wanzuwar alheri” Fathul Bãri [4/555].

Abul Walid al-Baji Allah ya yi masa rahama ya ce: “Mutane ba za su gushe ba game da addininsu suna cikin alheri matuƙar suna gaggauta buɗa-baki a bisa tafarki na sunna. Gaggauta buɗa-baki shi ne kada a yi jinkirin shan ruwa bayan rana ta faɗi domin nuna kai maƙura da matuƙa wajen ibada da ƙudurce cewa azumi bai yi ba idan aka sha ruwa bayan rana ta faɗi…” al-Baji; al-Muntaƙã Aharhul Muwaɗɗã [2/42].

Hukuncin Gaggauta Buɗa-baki:
Mustahabbi ne mai azumi ya gaggauta buɗa-baki bayan ya tabbar da rana ta faɗi. Duba al-Ƙadi Abdulwahab; al-Ma’unatu [1/347] da Ibnu Ƙudama; al-Muguni [3/174], da Ishaƙ bin Mansur; Masa’ilul Imami Ahmad wa Iahaƙ bin Rahuya [3/1224].

Yana daga cikin sunna gaggauta buɗa-baki. duba Ibu Abi Zaid al-Ƙairawani, ar-Risalatu [shafi na 83] da Ibni Abdilbarri; al-Kafi [1/350] da al-Ƙarafi; az-Zakhiratu [2/510] da Muhd. Binu Yusuf; at-Taju wal-Iklilu [3/304].

Buda
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund
Ilimi

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki
Bakon Marubuci

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki

June 12, 2026
A Karshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Damar Yin Takara
Bakon Marubuci

A Karshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Damar Yin Takara

June 12, 2026
Next Post
Yadda Magidanta, Samari Da ‘Yan Mata Za Su Daidaita Rayuwarsu A Azumin Bana

Yadda Magidanta, Samari Da ‘Yan Mata Za Su Daidaita Rayuwarsu A Azumin Bana

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Mata Ta Hallaka Mijinta Da Wuƙa Watanni Biyu Bayan Aure A Kano

June 17, 2026
An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka 

An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka 

June 16, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Shugabanni Game Da Barkewar Cutar Ebola

Mataimakin Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Shugabanni Game Da Barkewar Cutar Ebola

June 16, 2026
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar Da INEC Game Da Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar Da INEC Game Da Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu

June 16, 2026
Tattalin Arzikin Sin Ya Tafiya Cikin Kwanciyar Hankali

Tattalin Arzikin Sin Ya Tafiya Cikin Kwanciyar Hankali

June 16, 2026
Gaza

Farashin Mai Ya Faɗi Ƙasa Da Dala 80 Bayan cimma Yarjejeniyar Amurka Da Iran

June 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Myanmar

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Myanmar

June 16, 2026
Tinubu Ya Kaddamar Da Katafaren Gidajen Alƙalan Kotun Ɗaukaka Ƙara A Abuja

Tinubu Ya Kaddamar Da Katafaren Gidajen Alƙalan Kotun Ɗaukaka Ƙara A Abuja

June 16, 2026
Kasar Sin Na Samar Da Managarcin Yanayi Na Bunkasa Kirkire-kirkire Ga Masana’antun Kasa Da Kasa

Kasar Sin Na Samar Da Managarcin Yanayi Na Bunkasa Kirkire-kirkire Ga Masana’antun Kasa Da Kasa

June 16, 2026
Kogi: Mambobin APC Sun Koma PDP, Sun Mara Wa Natasha Baya Domin Wa’adi Na Biyu

Kogi: Mambobin APC Sun Koma PDP, Sun Mara Wa Natasha Baya Domin Wa’adi Na Biyu

June 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.