ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

BUƊA-BAKI [Falalarsa Da Lokacinsa] Na 1

by Nuhu Ubale Ibrahim
2 years ago
Buda

Allah Ta’ala Yana cewa: “Kuma ku ci ku sha, har farin zare ya bayyana a gare ku daga baƙin zare na alfijir, sa’an nan kuma ku cika azumi zuwa dare” Suratul Baƙara aya ta 187.

Wannan aya ta bayyana mana lokacin da azumi yake tuƙewa, watau dare. Dare kuma yana shiga ne daga lokacin da rana ta faɗi. Saboda haka azumi yana ƙarewa ne da shigar dare. An karɓo hadisi daga Umar ɗan Khaɗɗabi Allah ya ƙara yarda a gare shi ya ce: Manzon Allah (S.A.W) ya ce:” Idan dare ya fuskanto, yini kuma ya juya baya, rana kuma ta faɗi, to, lokacin sha ruwa ya yi” Bukhari[#1954] da Muslim [#1100].

  • BUƊA-BAKI [Falalarsa Da Lokacinsa] Na 2
  • BUƊA-BAKI [Falalarsa Da Lokacinsa] Na 3

Gaggauta Buɗa-Baki: Akwai hadisai da suka tabbatar da haka;

ADVERTISEMENT

1. An karbo hadisi daga Sahalu dan Sa’adu, Allah Ya ƙara yarda a gare shi. Lalle Manzon Allah (S.A.W) ya ce:” Mutane ba za su gushe ba cikin alheri matuƙar suna gaggauta buɗa-baki” Bukhari [#1957] da Muslim [#1098]

2. An karbo hadisi daga Abu Huraira Allah ya ƙara yarda a gare shi, daga Annabi (S.A.W) ya ce:” Addini ba zai gushe ba yana yin rinjaye da galaba ba, matuƙar mutane suna gaggauta buɗa baki. Ku gaggauta buɗa-baki, domin Yahudu da Nasara suna jirkinta shi” Hadisi ne mai kyau Abu Dawud [#2353] da Ibnu Maja [#1689] da Ahmad [#9810] da Ibnu Abi Shaiba [#8944].

LABARAI MASU NASABA

An Tantance Masu Neman Aikin Koyarwa 500 A Jigawa

JAMB Ta Ƙara Wa’adin Amincewar Guraben Karatu Zuwa 30 Satumba

Imam an-Nawawi Allah ya yi masa rahama yana cewa: “A cikin wannan hadisi akwai zaburarwa a kan gaggauta buɗa-baki bayan an tabbatar da fuɗuwar rana, kuma al’amarin al’ummar Musulmi ba zai gushe ba cikin tsari da alheri matuƙar suka kasance suna tsare wannan sunna, idan kuma suka jirkinta yin buɗa-baki, to , alama ce da take nuna za su faɗa cikin wani tasku” an-Nawawi; al-Minhaju Sharhu Sahihi Muslim [7/206] . Ibnu Hajar Allah ya yi masa rahama ya ce: “Addini ya yi galaba da rinjaye yana lazimta wanzuwar alheri” Fathul Bãri [4/555].

Abul Walid al-Baji Allah ya yi masa rahama ya ce: “Mutane ba za su gushe ba game da addininsu suna cikin alheri matuƙar suna gaggauta buɗa-baki a bisa tafarki na sunna. Gaggauta buɗa-baki shi ne kada a yi jinkirin shan ruwa bayan rana ta faɗi domin nuna kai maƙura da matuƙa wajen ibada da ƙudurce cewa azumi bai yi ba idan aka sha ruwa bayan rana ta faɗi…” al-Baji; al-Muntaƙã Aharhul Muwaɗɗã [2/42].

Hukuncin Gaggauta Buɗa-baki:
Mustahabbi ne mai azumi ya gaggauta buɗa-baki bayan ya tabbar da rana ta faɗi. Duba al-Ƙadi Abdulwahab; al-Ma’unatu [1/347] da Ibnu Ƙudama; al-Muguni [3/174], da Ishaƙ bin Mansur; Masa’ilul Imami Ahmad wa Iahaƙ bin Rahuya [3/1224].

Yana daga cikin sunna gaggauta buɗa-baki. duba Ibu Abi Zaid al-Ƙairawani, ar-Risalatu [shafi na 83] da Ibni Abdilbarri; al-Kafi [1/350] da al-Ƙarafi; az-Zakhiratu [2/510] da Muhd. Binu Yusuf; at-Taju wal-Iklilu [3/304].

Buda
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

Buda
Ilimi

An Tantance Masu Neman Aikin Koyarwa 500 A Jigawa

August 31, 2026
Buda
Ilimi

JAMB Ta Ƙara Wa’adin Amincewar Guraben Karatu Zuwa 30 Satumba

August 29, 2026
Zanga-Zanga: Gwamnatin Yobe Ta Bayar Da Umarnin Rufe Makarantun Jihar
Bakon Marubuci

Buni Ya Nuna Kwarewarsa Ta Diflomasiyya

August 28, 2026
Next Post
Yadda Magidanta, Samari Da ‘Yan Mata Za Su Daidaita Rayuwarsu A Azumin Bana

Yadda Magidanta, Samari Da ‘Yan Mata Za Su Daidaita Rayuwarsu A Azumin Bana

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.