• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buga Kudi: EFCC Za Ta Sake Gurfanar Da Emefiele A Kotu A Ranar Laraba

by Sadiq
1 year ago
EFCC

Hukumar yaki da yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa (EFCC), za ta gurfanar da tsohon gwamnan babban bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele a gaban kuliya bisa kashe Naira biliyan 18.96 wajen buga takardun kudi miliyan 684.5.

Tun da farko dai an shirya gurfanar da shi a ranar 30 ga watan Afrilu, 2024, amma aka dage zaman bayan yarjejeniyar da kotu ta yi da bangarorin EFCC da na Emefiele.

  • Gwamnatin Nijeriya Ta Kafa Makarantar Bayar Da Horo Kan Al’adun Ƙasa – NICO
  • Sojar Ukraine Ta Zama Bazawara Kwana Biyu Da Aurenta

A tuhume-tuhume hudu da EFCC ta shigar gaban kotun, ta yi zargin cewa Emefiele ya bijire wa umarnin doka lokacin sauya takardun Naira a lokacin gwamnatin tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari.

EFCC ta kuma zargi Emefiele da cire Naira biliyan 124.8 daga asusun tara kudaden shiga na tarayya ba bisa ka’ida ba.

LEADERSHIP ta tattaro cewa tsohon gwamnan na CBN zai gurfana a gaban mai shari’a Maryann Anenih ta babbar kotun tarayya da ke Abuja.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Wannan shari’ar za ta kawo adadin tuhume-tuhumen da ake yi wa tsohon gwamnan na CBN zuwa uku.

A ranar 17 ga watan Nuwamba, 2023, Emefiele ya gurfana a gaban mai shari’a Hamza Muazu a kan tuhume-tuhume shida da suka hada da damfara, almundahana, wanda ya ki amsa laifinsa.

An kuma zarge shi da cin zarafin ofishinsa ta hanyar kwangilar sayen motoci 43 da suka kai Naira biliyan 1.2 daga 2018 zuwa 2020.

A ranar 8 ga watan Afrilu, 2024, EFCC ta kuma sake gurfanar da Emefiele tare da wani Henry Omoile a gaban mai shari’a Rahman Oshodi na kotun laifuffuka da ke Ikeja a Jihar Legas, kan zargin almundahanar dala biliyan 4.5 da Naira biliyan 2.8.

Sai dai Emefiele ya musanta wadannan tuhume-tuhume.

Rotimi Oyedepo (SAN) ne, ya sake shigar da sabuwar tuhuma a ranar 2 ga watan Afrilu, 2024 a madadin EFCC tare da wasu lauyoyi takwas da ke aiki da babban lauyan tarayya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi
Manyan Labarai

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

October 10, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta
Manyan Labarai

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Next Post
Matar Aure Ta Kashe Mijinta Saboda Yawan Jima’i A Benuwe

Matar Aure Ta Kashe Mijinta Saboda Yawan Jima'i A Benuwe

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

October 10, 2025
EFCC

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

October 10, 2025
Matatar dangote

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

October 10, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

October 10, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

October 10, 2025
Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

October 10, 2025
Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

October 10, 2025
Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

October 10, 2025
Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

October 10, 2025
An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.