ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buga Kudi: EFCC Za Ta Sake Gurfanar Da Emefiele A Kotu A Ranar Laraba

by Sadiq
2 years ago
EFCC

Hukumar yaki da yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa (EFCC), za ta gurfanar da tsohon gwamnan babban bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele a gaban kuliya bisa kashe Naira biliyan 18.96 wajen buga takardun kudi miliyan 684.5.

Tun da farko dai an shirya gurfanar da shi a ranar 30 ga watan Afrilu, 2024, amma aka dage zaman bayan yarjejeniyar da kotu ta yi da bangarorin EFCC da na Emefiele.

  • Gwamnatin Nijeriya Ta Kafa Makarantar Bayar Da Horo Kan Al’adun Ƙasa – NICO
  • Sojar Ukraine Ta Zama Bazawara Kwana Biyu Da Aurenta

A tuhume-tuhume hudu da EFCC ta shigar gaban kotun, ta yi zargin cewa Emefiele ya bijire wa umarnin doka lokacin sauya takardun Naira a lokacin gwamnatin tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari.

ADVERTISEMENT

EFCC ta kuma zargi Emefiele da cire Naira biliyan 124.8 daga asusun tara kudaden shiga na tarayya ba bisa ka’ida ba.

LEADERSHIP ta tattaro cewa tsohon gwamnan na CBN zai gurfana a gaban mai shari’a Maryann Anenih ta babbar kotun tarayya da ke Abuja.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

Wannan shari’ar za ta kawo adadin tuhume-tuhumen da ake yi wa tsohon gwamnan na CBN zuwa uku.

A ranar 17 ga watan Nuwamba, 2023, Emefiele ya gurfana a gaban mai shari’a Hamza Muazu a kan tuhume-tuhume shida da suka hada da damfara, almundahana, wanda ya ki amsa laifinsa.

An kuma zarge shi da cin zarafin ofishinsa ta hanyar kwangilar sayen motoci 43 da suka kai Naira biliyan 1.2 daga 2018 zuwa 2020.

A ranar 8 ga watan Afrilu, 2024, EFCC ta kuma sake gurfanar da Emefiele tare da wani Henry Omoile a gaban mai shari’a Rahman Oshodi na kotun laifuffuka da ke Ikeja a Jihar Legas, kan zargin almundahanar dala biliyan 4.5 da Naira biliyan 2.8.

Sai dai Emefiele ya musanta wadannan tuhume-tuhume.

Rotimi Oyedepo (SAN) ne, ya sake shigar da sabuwar tuhuma a ranar 2 ga watan Afrilu, 2024 a madadin EFCC tare da wasu lauyoyi takwas da ke aiki da babban lauyan tarayya.

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Matar Aure Ta Kashe Mijinta Saboda Yawan Jima’i A Benuwe

Matar Aure Ta Kashe Mijinta Saboda Yawan Jima'i A Benuwe

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.