ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojar Ukraine Ta Zama Bazawara Kwana Biyu Da Aurenta

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Ukraine

Ya hada zoben aure ta hanyar amfani da gwangwani kuma ya nemi na aure shi. Tabbas na amince,” a cewar Baleria Subotina.

“Masoyina ne na kwarai. Zobinanmu sun yi kyau sosai,” in ji ta.

  • Ba Gwamnati Ce Kadai Za Ta Magance Yawan Barace-Barace Ba
  • Kabilar Bayankole Da Innar Amarya Ke Jima’i Da Ango Domin Gwaji

Ita da saurayinta Andriy Subotin mai shekara 34 kuma sajan a rundunar sojin Ukraine, suna shirin daura aure a Mariupol kafin yaki ya barke tsakanin kasar da Rasha.

ADVERTISEMENT

Sun yi ta burin hada gagarumin biki tare da ‘yan’uwa da abokan arziki.

Sai dai jim kadan bayan mamayen da Rasha, dakarun kasar sun wuce kai-tsaye zuwa wannan gari mai tashar jiragen ruwa kuma mai muhimmanci a Kudancin Ukraine kuma suka yi masa zobe cikin ‘yan kwanaki.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Dakarun Rasha sun yi ta luguden wuta a kan Birnin Mariupol, tituna suka dinga ci da wuta, babu abinci, babu wuta, babu ruwa, babu wata hanyar barin garin.

Garin ya shafe kusan wata uku a garkame. An yi imanin cewa an kashe dubun dubatar fararen hula.

A gefe guda kuma, mazauna Mariupol da yawa sun nemi mafaka a ginin masana’antar karafa ta Azobstal, inda ake da maboya sama da 30 wadanda aka gina tun lokacin Tarayyar Sobiet saboda tsoron harin nukiliya.

A nan ne kuma aka daura wa Baleria aure – kuma ta zama bazawara a kwana biyu kacal.

‘Yunwa a kan iyaka’

Baleria mawakiya ce lokacin da Rasha ta afka wa Ukraine. Daga nan kuma sai ta zama kakakin Bataliyar Azob.

Yayin da Rasha ke tsananta hare-hare a kan Mariupol, dole aka tilasta wa dakarun Ukraine guduwa zuwa maboyar Azobstal tare da fararen hula.

Mashigar maboyar kamar rami take, kuma sai mutum ya yi ta yin kasa a kan matattakalar da suka lalace, in ji Baleria.

Mutane sun giggina madafa a cikin maboyar, inda ake sake girka abincin da aka ci aka rage.

Idan suka samu fulawa sai su kwaba ta don hada ket (cake).

“Muna kiran sa burodi amma dai ket ne kawai da ruwa. A haka muka rayu. Yunwa ce kawai a wurin,” a cewar Baleria.

“Mun zama kamar wasu beraye saboda duk abin da muka samu ci kawai muke. Mu kan yi barci a kasa ko kuma a kan tsimma.

“A wani wurin babu haske ko kadan, amma sai da idanuwanmu suka saba har ma ya zama jiki. Amma maganar gaskiya rayuwarmu ta daban ce a lokacin.”

A ranar 15 ga watan Afrilun 2022, an jefa wani babban bam a kan masana’antar, wanda ya raunata baleria.

“A cikin gawarwaki aka gano ni, kuma ni kadai ce a raye. Sa’a ce kawai, amma kuma bala’i ne me tsauri.”

Bayan rauni da ta ji a ka saboda buguwa, Baleria ta shafe kwana takwas a asibitin da ke maboyar ta karkashin kasa tare da sauran marasa lafiya.

“Ba su iya samun kulawar da ta dace ba saboda babu isassun magunguna. Warin jini da kuma na rubewar abubuwa sun cika wurin,” in ji ta.

Shi ma mijin Baleria mai suna Andriy a Azobstal yake. Jim kadan bayan raunukan da ta ji, nan take ya nemi aurenta kuma a wurin.

A ranar 5 ga watan Mayu, ma’auratan suka sanya hannu kan yarjejeniyar aure kuma suka aika wa iyayen Andriy kwafin takardun ta intanet a Kyib, wadanda daga baya suka je ofishin hukuma don karkare shirin.

Sun yi bikinsu a maboyar sanye da kakin soja a matsayin kwalliyar biki, da kuma zobinansu da aka yi da gwangwani.

Andriy ya yi alkawarin zai saya mata zoben gaske idan aka gama yakin.

Amma an kashe shi ranar 7 ga watan Mayu a bakin daga.

Ukraine
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
tallafi

Ba Za Ta Saɓu Ba, Mun Maka CBN A Kotu Kan Janye Wa Mutane Kuɗaɗensu A Asusunsu - Ƙungiyoyi

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.