ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojar Ukraine Ta Zama Bazawara Kwana Biyu Da Aurenta

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Ukraine

Ya hada zoben aure ta hanyar amfani da gwangwani kuma ya nemi na aure shi. Tabbas na amince,” a cewar Baleria Subotina.

“Masoyina ne na kwarai. Zobinanmu sun yi kyau sosai,” in ji ta.

  • Ba Gwamnati Ce Kadai Za Ta Magance Yawan Barace-Barace Ba
  • Kabilar Bayankole Da Innar Amarya Ke Jima’i Da Ango Domin Gwaji

Ita da saurayinta Andriy Subotin mai shekara 34 kuma sajan a rundunar sojin Ukraine, suna shirin daura aure a Mariupol kafin yaki ya barke tsakanin kasar da Rasha.

ADVERTISEMENT

Sun yi ta burin hada gagarumin biki tare da ‘yan’uwa da abokan arziki.

Sai dai jim kadan bayan mamayen da Rasha, dakarun kasar sun wuce kai-tsaye zuwa wannan gari mai tashar jiragen ruwa kuma mai muhimmanci a Kudancin Ukraine kuma suka yi masa zobe cikin ‘yan kwanaki.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Dakarun Rasha sun yi ta luguden wuta a kan Birnin Mariupol, tituna suka dinga ci da wuta, babu abinci, babu wuta, babu ruwa, babu wata hanyar barin garin.

Garin ya shafe kusan wata uku a garkame. An yi imanin cewa an kashe dubun dubatar fararen hula.

A gefe guda kuma, mazauna Mariupol da yawa sun nemi mafaka a ginin masana’antar karafa ta Azobstal, inda ake da maboya sama da 30 wadanda aka gina tun lokacin Tarayyar Sobiet saboda tsoron harin nukiliya.

A nan ne kuma aka daura wa Baleria aure – kuma ta zama bazawara a kwana biyu kacal.

‘Yunwa a kan iyaka’

Baleria mawakiya ce lokacin da Rasha ta afka wa Ukraine. Daga nan kuma sai ta zama kakakin Bataliyar Azob.

Yayin da Rasha ke tsananta hare-hare a kan Mariupol, dole aka tilasta wa dakarun Ukraine guduwa zuwa maboyar Azobstal tare da fararen hula.

Mashigar maboyar kamar rami take, kuma sai mutum ya yi ta yin kasa a kan matattakalar da suka lalace, in ji Baleria.

Mutane sun giggina madafa a cikin maboyar, inda ake sake girka abincin da aka ci aka rage.

Idan suka samu fulawa sai su kwaba ta don hada ket (cake).

“Muna kiran sa burodi amma dai ket ne kawai da ruwa. A haka muka rayu. Yunwa ce kawai a wurin,” a cewar Baleria.

“Mun zama kamar wasu beraye saboda duk abin da muka samu ci kawai muke. Mu kan yi barci a kasa ko kuma a kan tsimma.

“A wani wurin babu haske ko kadan, amma sai da idanuwanmu suka saba har ma ya zama jiki. Amma maganar gaskiya rayuwarmu ta daban ce a lokacin.”

A ranar 15 ga watan Afrilun 2022, an jefa wani babban bam a kan masana’antar, wanda ya raunata baleria.

“A cikin gawarwaki aka gano ni, kuma ni kadai ce a raye. Sa’a ce kawai, amma kuma bala’i ne me tsauri.”

Bayan rauni da ta ji a ka saboda buguwa, Baleria ta shafe kwana takwas a asibitin da ke maboyar ta karkashin kasa tare da sauran marasa lafiya.

“Ba su iya samun kulawar da ta dace ba saboda babu isassun magunguna. Warin jini da kuma na rubewar abubuwa sun cika wurin,” in ji ta.

Shi ma mijin Baleria mai suna Andriy a Azobstal yake. Jim kadan bayan raunukan da ta ji, nan take ya nemi aurenta kuma a wurin.

A ranar 5 ga watan Mayu, ma’auratan suka sanya hannu kan yarjejeniyar aure kuma suka aika wa iyayen Andriy kwafin takardun ta intanet a Kyib, wadanda daga baya suka je ofishin hukuma don karkare shirin.

Sun yi bikinsu a maboyar sanye da kakin soja a matsayin kwalliyar biki, da kuma zobinansu da aka yi da gwangwani.

Andriy ya yi alkawarin zai saya mata zoben gaske idan aka gama yakin.

Amma an kashe shi ranar 7 ga watan Mayu a bakin daga.

Ukraine
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
Labarai

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Next Post
tallafi

Ba Za Ta Saɓu Ba, Mun Maka CBN A Kotu Kan Janye Wa Mutane Kuɗaɗensu A Asusunsu - Ƙungiyoyi

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026
Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.