• English
  • Business News
Wednesday, July 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojar Ukraine Ta Zama Bazawara Kwana Biyu Da Aurenta

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Labarai
0
Sojar Ukraine Ta Zama Bazawara Kwana Biyu Da Aurenta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ya hada zoben aure ta hanyar amfani da gwangwani kuma ya nemi na aure shi. Tabbas na amince,” a cewar Baleria Subotina.

“Masoyina ne na kwarai. Zobinanmu sun yi kyau sosai,” in ji ta.

  • Ba Gwamnati Ce Kadai Za Ta Magance Yawan Barace-Barace Ba
  • Kabilar Bayankole Da Innar Amarya Ke Jima’i Da Ango Domin Gwaji

Ita da saurayinta Andriy Subotin mai shekara 34 kuma sajan a rundunar sojin Ukraine, suna shirin daura aure a Mariupol kafin yaki ya barke tsakanin kasar da Rasha.

Sun yi ta burin hada gagarumin biki tare da ‘yan’uwa da abokan arziki.

Sai dai jim kadan bayan mamayen da Rasha, dakarun kasar sun wuce kai-tsaye zuwa wannan gari mai tashar jiragen ruwa kuma mai muhimmanci a Kudancin Ukraine kuma suka yi masa zobe cikin ‘yan kwanaki.

Labarai Masu Nasaba

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

Dakarun Rasha sun yi ta luguden wuta a kan Birnin Mariupol, tituna suka dinga ci da wuta, babu abinci, babu wuta, babu ruwa, babu wata hanyar barin garin.

Garin ya shafe kusan wata uku a garkame. An yi imanin cewa an kashe dubun dubatar fararen hula.

A gefe guda kuma, mazauna Mariupol da yawa sun nemi mafaka a ginin masana’antar karafa ta Azobstal, inda ake da maboya sama da 30 wadanda aka gina tun lokacin Tarayyar Sobiet saboda tsoron harin nukiliya.

A nan ne kuma aka daura wa Baleria aure – kuma ta zama bazawara a kwana biyu kacal.

‘Yunwa a kan iyaka’

Baleria mawakiya ce lokacin da Rasha ta afka wa Ukraine. Daga nan kuma sai ta zama kakakin Bataliyar Azob.

Yayin da Rasha ke tsananta hare-hare a kan Mariupol, dole aka tilasta wa dakarun Ukraine guduwa zuwa maboyar Azobstal tare da fararen hula.

Mashigar maboyar kamar rami take, kuma sai mutum ya yi ta yin kasa a kan matattakalar da suka lalace, in ji Baleria.

Mutane sun giggina madafa a cikin maboyar, inda ake sake girka abincin da aka ci aka rage.

Idan suka samu fulawa sai su kwaba ta don hada ket (cake).

“Muna kiran sa burodi amma dai ket ne kawai da ruwa. A haka muka rayu. Yunwa ce kawai a wurin,” a cewar Baleria.

“Mun zama kamar wasu beraye saboda duk abin da muka samu ci kawai muke. Mu kan yi barci a kasa ko kuma a kan tsimma.

“A wani wurin babu haske ko kadan, amma sai da idanuwanmu suka saba har ma ya zama jiki. Amma maganar gaskiya rayuwarmu ta daban ce a lokacin.”

A ranar 15 ga watan Afrilun 2022, an jefa wani babban bam a kan masana’antar, wanda ya raunata baleria.

“A cikin gawarwaki aka gano ni, kuma ni kadai ce a raye. Sa’a ce kawai, amma kuma bala’i ne me tsauri.”

Bayan rauni da ta ji a ka saboda buguwa, Baleria ta shafe kwana takwas a asibitin da ke maboyar ta karkashin kasa tare da sauran marasa lafiya.

“Ba su iya samun kulawar da ta dace ba saboda babu isassun magunguna. Warin jini da kuma na rubewar abubuwa sun cika wurin,” in ji ta.

Shi ma mijin Baleria mai suna Andriy a Azobstal yake. Jim kadan bayan raunukan da ta ji, nan take ya nemi aurenta kuma a wurin.

A ranar 5 ga watan Mayu, ma’auratan suka sanya hannu kan yarjejeniyar aure kuma suka aika wa iyayen Andriy kwafin takardun ta intanet a Kyib, wadanda daga baya suka je ofishin hukuma don karkare shirin.

Sun yi bikinsu a maboyar sanye da kakin soja a matsayin kwalliyar biki, da kuma zobinansu da aka yi da gwangwani.

Andriy ya yi alkawarin zai saya mata zoben gaske idan aka gama yakin.

Amma an kashe shi ranar 7 ga watan Mayu a bakin daga.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: SojaUkraineYaki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Harba Sabon Tauraron Dan Adam Zuwa Sararin Samaniya

Next Post

Ba Za Ta SaÉ“u Ba, Mun Maka CBN A Kotu Kan Janye Wa Mutane KuÉ—aÉ—ensu A Asusunsu – Ƙungiyoyi

Related

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa
Ra'ayi Riga

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

1 hour ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Labarai

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

4 hours ago
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba
Manyan Labarai

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

5 hours ago
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820
Manyan Labarai

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

7 hours ago
Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki
Manyan Labarai

Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

8 hours ago
Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

16 hours ago
Next Post
tallafi

Ba Za Ta Saɓu Ba, Mun Maka CBN A Kotu Kan Janye Wa Mutane Kuɗaɗensu A Asusunsu - Ƙungiyoyi

LABARAI MASU NASABA

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

July 9, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Babu Wanda Ya BuÆ™aci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC

July 9, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

July 9, 2025
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

July 9, 2025
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

July 9, 2025
Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

July 9, 2025
Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

July 9, 2025
Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

July 9, 2025
Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

July 8, 2025
Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

July 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.