• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ya Bai Wa ‘Yan Kasar Waje 286 Shaidar  Zama ‘Yan Nijeriya

by Sadiq
3 years ago
Kasar Waje

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, ya bai wa wasu ‘yan kasashen waje 286 takardar shaidar zama ‘yan Nijeriya, inda ya bukace su da su kasance ‘yan na gari domin cin gajiyar duk wani hakki da alfarmar da aka ba su.

“Kun yi mubaya’a ga Nijeriya. Lokacin da kuka bai wa Nijeriya soyayya da amincinku, sai ta mayar muku da soyayyar ta da amincinta a gare ku.”

  • Kowa Ya Yi Da Kyau Zai Ga Da Kyau
  • Ya Shiga Hannun ‘Yansanda Bayan Sayan Bindiga Don Kashe Mahaifansa

Shugaban ya shaida wa wadanda suka ci gajiyar shirin a wani taron da aka yi a fadar gwamnatin tarayya a Abuja a yau Alhamis.

Shugaba Buhari, ya bayyana cewa daga cikin ‘yan kasashen waje 286 da aka bai wa takardar shaidar zama ‘yan Nijeriya, 208 sun karbi takardar shaidar zama ‘yan kasa, yayin da 78 suka samu takardar shaidar rajista.

A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasa, Femi Adesina ya fitar, Buhari ya bukace su da su bayar da gudumawa mai kyau kuma mai amfani ga ci gaba da jin dadin al’ummomin da suke zaune a kasar nan, inda ya kara da cewa a matsayinsu na ‘yan kasa dole ne su kasance masu bin ka’idojin kasa da kasa da ka’idar aiki.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

“Ana sa ran ku kasance masu mutunta dukkan hukumomin da aka kafa.

“Duk wadanda suka shafi al’amuran shige da fice su bai wa sabbin ‘yan kasarmu shaidar doka cikin gaggawa. Haka kuma ya kamata kananan hukumominsu su taimaka wajen hada kansu a cikin al’umma domin su samu damar cin gajiyar duk wani hakki na dan Nijeriya,” in ji Buhari.

Yayin aiwatar da ikon da kundin tsarin mulkin kasar ya ba shi, a babi na uku, sashe na 25-31 na kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya, 1999 (kamar yadda aka yi wa kwaskwarima), shugaban ya shaida wa sabbin ‘yan kasar cewa Nijeriya kasa ce da ta hade da ka’idojin samun dama, daidaito, da ‘yanci kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.

“Ko daga ina kuka fito, ko wace irin imani kuka yi, kasar nan ita ce kasarku. Tarihinmu yanzu ya zama tarihinku, al’adunmu kuma yanzu sun zama al’adunku ne. Nijeriya ita ce gidanku da abin alfahari da farin cikinku.

Ya kara da cewa, “A bisa manufofinmu na kawo sauyi na bin ka’ida da tsare-tsare na gaskiya, Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida ta tabbatar da cewa wadanda suka cancanta ne kawai aka bai wa izinin zama ‘yan Nijeriya,” in ji shi.

Shugaba Buhari ya kara da cewa gwamnatin tarayya a shekarar 2020 ta dauki tsarin aiki na kasa don kawar da rashin jihadi, don haka ne ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola, ya kaddamar da babban kwamitin gudanarwa na kawar da rashin jiha a Nijeriya nan da shekarar 2024.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI
Manyan Labarai

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka
Kiwon Lafiya

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025
Next Post
Mata Ta Kai Karar Mijinta Kotu Saboda Ya Daina Cin Abincinta

Mata Ta Kai Karar Mijinta Kotu Saboda Ya Daina Cin Abincinta

LABARAI MASU NASABA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

October 25, 2025

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025
Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.