• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ya Bai Wa ‘Yan Kasar Waje 286 Shaidar  Zama ‘Yan Nijeriya

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Buhari Ya Bai Wa ‘Yan Kasar Waje 286 Shaidar  Zama ‘Yan Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, ya bai wa wasu ‘yan kasashen waje 286 takardar shaidar zama ‘yan Nijeriya, inda ya bukace su da su kasance ‘yan na gari domin cin gajiyar duk wani hakki da alfarmar da aka ba su.

“Kun yi mubaya’a ga Nijeriya. Lokacin da kuka bai wa Nijeriya soyayya da amincinku, sai ta mayar muku da soyayyar ta da amincinta a gare ku.”

  • Kowa Ya Yi Da Kyau Zai Ga Da Kyau
  • Ya Shiga Hannun ‘Yansanda Bayan Sayan Bindiga Don Kashe Mahaifansa

Shugaban ya shaida wa wadanda suka ci gajiyar shirin a wani taron da aka yi a fadar gwamnatin tarayya a Abuja a yau Alhamis.

Shugaba Buhari, ya bayyana cewa daga cikin ‘yan kasashen waje 286 da aka bai wa takardar shaidar zama ‘yan Nijeriya, 208 sun karbi takardar shaidar zama ‘yan kasa, yayin da 78 suka samu takardar shaidar rajista.

A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasa, Femi Adesina ya fitar, Buhari ya bukace su da su bayar da gudumawa mai kyau kuma mai amfani ga ci gaba da jin dadin al’ummomin da suke zaune a kasar nan, inda ya kara da cewa a matsayinsu na ‘yan kasa dole ne su kasance masu bin ka’idojin kasa da kasa da ka’idar aiki.

Labarai Masu Nasaba

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

“Ana sa ran ku kasance masu mutunta dukkan hukumomin da aka kafa.

“Duk wadanda suka shafi al’amuran shige da fice su bai wa sabbin ‘yan kasarmu shaidar doka cikin gaggawa. Haka kuma ya kamata kananan hukumominsu su taimaka wajen hada kansu a cikin al’umma domin su samu damar cin gajiyar duk wani hakki na dan Nijeriya,” in ji Buhari.

Yayin aiwatar da ikon da kundin tsarin mulkin kasar ya ba shi, a babi na uku, sashe na 25-31 na kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya, 1999 (kamar yadda aka yi wa kwaskwarima), shugaban ya shaida wa sabbin ‘yan kasar cewa Nijeriya kasa ce da ta hade da ka’idojin samun dama, daidaito, da ‘yanci kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.

“Ko daga ina kuka fito, ko wace irin imani kuka yi, kasar nan ita ce kasarku. Tarihinmu yanzu ya zama tarihinku, al’adunmu kuma yanzu sun zama al’adunku ne. Nijeriya ita ce gidanku da abin alfahari da farin cikinku.

Ya kara da cewa, “A bisa manufofinmu na kawo sauyi na bin ka’ida da tsare-tsare na gaskiya, Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida ta tabbatar da cewa wadanda suka cancanta ne kawai aka bai wa izinin zama ‘yan Nijeriya,” in ji shi.

Shugaba Buhari ya kara da cewa gwamnatin tarayya a shekarar 2020 ta dauki tsarin aiki na kasa don kawar da rashin jihadi, don haka ne ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola, ya kaddamar da babban kwamitin gudanarwa na kawar da rashin jiha a Nijeriya nan da shekarar 2024.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kasar WajeKasashen WajeShaidar Zama 'Yan Nijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ambaliyar Ruwa Ta Kashe Mutane Fiye Da 130 Cikin Wata Biyu A Nijar

Next Post

Mata Ta Kai Karar Mijinta Kotu Saboda Ya Daina Cin Abincinta

Related

Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

12 hours ago
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

18 hours ago
An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja
Manyan Labarai

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

19 hours ago
Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa
Manyan Labarai

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

20 hours ago
Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa
Manyan Labarai

Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

21 hours ago
Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano
Manyan Labarai

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

1 day ago
Next Post
Mata Ta Kai Karar Mijinta Kotu Saboda Ya Daina Cin Abincinta

Mata Ta Kai Karar Mijinta Kotu Saboda Ya Daina Cin Abincinta

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 6, 2025
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.