ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ya Bai Wa ‘Yan Kasar Waje 286 Shaidar  Zama ‘Yan Nijeriya

by Sadiq
4 years ago
Kasar Waje

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, ya bai wa wasu ‘yan kasashen waje 286 takardar shaidar zama ‘yan Nijeriya, inda ya bukace su da su kasance ‘yan na gari domin cin gajiyar duk wani hakki da alfarmar da aka ba su.

“Kun yi mubaya’a ga Nijeriya. Lokacin da kuka bai wa Nijeriya soyayya da amincinku, sai ta mayar muku da soyayyar ta da amincinta a gare ku.”

  • Kowa Ya Yi Da Kyau Zai Ga Da Kyau
  • Ya Shiga Hannun ‘Yansanda Bayan Sayan Bindiga Don Kashe Mahaifansa

Shugaban ya shaida wa wadanda suka ci gajiyar shirin a wani taron da aka yi a fadar gwamnatin tarayya a Abuja a yau Alhamis.

ADVERTISEMENT

Shugaba Buhari, ya bayyana cewa daga cikin ‘yan kasashen waje 286 da aka bai wa takardar shaidar zama ‘yan Nijeriya, 208 sun karbi takardar shaidar zama ‘yan kasa, yayin da 78 suka samu takardar shaidar rajista.

A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasa, Femi Adesina ya fitar, Buhari ya bukace su da su bayar da gudumawa mai kyau kuma mai amfani ga ci gaba da jin dadin al’ummomin da suke zaune a kasar nan, inda ya kara da cewa a matsayinsu na ‘yan kasa dole ne su kasance masu bin ka’idojin kasa da kasa da ka’idar aiki.

LABARAI MASU NASABA

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

“Ana sa ran ku kasance masu mutunta dukkan hukumomin da aka kafa.

“Duk wadanda suka shafi al’amuran shige da fice su bai wa sabbin ‘yan kasarmu shaidar doka cikin gaggawa. Haka kuma ya kamata kananan hukumominsu su taimaka wajen hada kansu a cikin al’umma domin su samu damar cin gajiyar duk wani hakki na dan Nijeriya,” in ji Buhari.

Yayin aiwatar da ikon da kundin tsarin mulkin kasar ya ba shi, a babi na uku, sashe na 25-31 na kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya, 1999 (kamar yadda aka yi wa kwaskwarima), shugaban ya shaida wa sabbin ‘yan kasar cewa Nijeriya kasa ce da ta hade da ka’idojin samun dama, daidaito, da ‘yanci kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.

“Ko daga ina kuka fito, ko wace irin imani kuka yi, kasar nan ita ce kasarku. Tarihinmu yanzu ya zama tarihinku, al’adunmu kuma yanzu sun zama al’adunku ne. Nijeriya ita ce gidanku da abin alfahari da farin cikinku.

Ya kara da cewa, “A bisa manufofinmu na kawo sauyi na bin ka’ida da tsare-tsare na gaskiya, Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida ta tabbatar da cewa wadanda suka cancanta ne kawai aka bai wa izinin zama ‘yan Nijeriya,” in ji shi.

Shugaba Buhari ya kara da cewa gwamnatin tarayya a shekarar 2020 ta dauki tsarin aiki na kasa don kawar da rashin jihadi, don haka ne ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola, ya kaddamar da babban kwamitin gudanarwa na kawar da rashin jiha a Nijeriya nan da shekarar 2024.

MASU ALAKA

Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia
Manyan Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato
Manyan Labarai

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Next Post
Mata Ta Kai Karar Mijinta Kotu Saboda Ya Daina Cin Abincinta

Mata Ta Kai Karar Mijinta Kotu Saboda Ya Daina Cin Abincinta

LABARAI MASU NASABA

Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.