ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kowa Ya Yi Da Kyau Zai Ga Da Kyau

by CMG Hausa
4 years ago
Tattalin Arziki

Yayin da tattalin arzikin wasu kasashen duniya ke kara fuskantar matsin lamba da tangal-tangal sakamakon manufofin marasa dacewa da tasirin annobar covid-19 da makamantansu, a hannu guda kuma wani rahoto da hukumar kididdiga ta kasar Sin (NBS) ta fitar ya nuna cewa, a cikin shekaru 10 da suka gabata, tattalin arzikin kasar Sin yana cikin yanayi na daidaito da bunkasuwa yadda ya kamata, kana baki dayan karfin kasar ma ya ingantu matuka, haka kuma tasirinsa a duniya yana karuwa a kai a kai.

Wannan ya kara tabbatar da ingancin matakan da mahukuntan kasar ke dauka game da raya tattalin arziki da ma sauran fannoni na ci gaban kasa.

  • Neman Illata Kasar Sin Ya Haifar Da Matsalar Tattalin Arziki Ga Amurka

Alkaluma na nuna cewa, daga shekarar 2013 zuwa 2021, GDPn kasar Sin ya karu da kashi 6.6 bisa dari a duk shekara, wanda ya zarce matsakaicin karuwar kashi 2.6 cikin 100 a duniya, da kashi 3.7 cikin 100 na kasashe masu tasowa a makamancin wannan lokaci, sabanin yadda wasu kasashen yamma ke fama da matsaloli na hauhawar farashin kaya da rashin aikin yi.

ADVERTISEMENT

Kasar Sin dai ta nace kan inganta ci gaba mai inganci, da bude kofa ga ketare, da sassauta hanyoyin shiga kasuwanninta a bangaren samar da hidima, da bude harkokin cinikayya tsakanin kasashe, da fadada aikin dandalin bude kofa ga waje, baya ga kokarin da take yi na kafa ingantaccen tsarin fadada sashin samar da hidima.

A baya-bayan nan ma firaministan kasar Sin Li Keqiang, ya jaddada bukatar aiwatar da manufofin daidaita tattalin arziki, da farashin kayayyaki, da samar da guraben ayyukan yi. Matakan da masana ke cewa, kyakkyawar dabara ce da za ta haifar da da mai ido.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Duk da cewa daidaituwar tattalin arziki ya danganta da yanayin hada-hadar kasuwanni, akwai bukatar a kara azama, wajen rage wahalhalun da sashen hada hadar kasuwannin ke fuskanta, yayin da ake kara fadada harkokin zuba jari, har a kai ga samar da damammakin bunkasa kasuwanni, da karfafa kwarin gwiwarsu.

Idan har ana fatan cimma burin raya tattalin arziki da zai faranta ran al’umma da ma farfado da tattalin arzikin duniya baki daya, ya dace a kara azama wajen kammala manyan ayyuka, da fadada hada-hadar kudade bisa tsare-tsare da aka tanada gwargwadon bukatun cikin gida.

Kana martaba dokokin hadin gwiwar kasa da kasa da muradun juna da sahihin hadin gwiwa, na daga cikin abubuwa da za su taimaka wajen samun farfadowar tattalin arzikin duniya, wanda daga karshe zai taba rayuwar bil-Adama baki daya daga dukkan fannoni. Don haka, duk wanda ya yi da kyau shi ma zai ga da kyau. (Ibrahim Yaya)

Tattalin Arziki
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
An Yanke Wa Mutane Biyu Hukuncin Daurin Shekara 50 A Saudiyya

An Yanke Wa Mutane Biyu Hukuncin Daurin Shekara 50 A Saudiyya

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.