Shugaba Muhammadu Buhari ya bi sahun ‘yan uwa da abokan arziki wajen miki ta’aziyyarsa na rashuwar tsohon Sufeton ‘Yansandan Nijeriya, Mustapha Balogun.
A sakon ta’aziyyar wanda mai ba shi shawara a bangaren watsa labarai, Mista Femi Adesina, ya sanya wa hannun ranar Juma’a aka kuma raba wa maneam labarai a Abuja, ya kuma mika ta’aziyyar ga rundunar ‘yansandan Nijeriya.
Buhari ya ce a Balogun, ya inganta aikin ‘yansanda a lokacin yana shugabantar rundunar ta yadda suka gudanar da aikinsu kamar yadda tsarin dimoikradiyya ya tanada.
Ya kuma yi addu’ar Allah ya gafarta masa, ya yafe masa kurakuransa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp