ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Sauya Wuraren Aiki Ga Manyan Jami’ai 69

by Abdulrazaq Yahuza
4 years ago
NIS

Shugaban Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS), CGI Isah Jere Idris, ya amince da sauya wuraren aiki ga manyan jami’ai 69 zuwa manyan ofisoshin hukumar na shiyyoyi da jihohi da ke sassan kasar nan.

Sanarwar da ta fito daga Jami’in hulda da jama’a na hukumar, ACI Amos Okpu ta bayyana cewa daga cikin adadin jami’an da aka sauya wa wuraren aikin akwai masu mukaman Kananan Mataimakan Kwanturola Janar (ACG) guda takwas sai masu mukaman Kwanturololi (CIS) guda 61 da aka rarraba su a sassan manyan ofisoshin hukumar.

  • Hukumar Kwastom Ta Cafke Miyagun Kwayoyi Na Kimanin Biliyan N1.4 A Legas
  • Hukumar NDLEA Ta Kona 560,068kg Na Hodar Iblis Da Wasu Kwayoyi A Legas

Cikin masu mukaman ACG da aka sauya wa wuraren aikin akwai ACG KM Amao wanda a da yake Kwanturolan Jihar Ogun amma yanzu an maida shi Sashen Ayyuka Na Gaba Daya a shalkwatar hukumar da ke Abuja, sa’ilin da ACG KN Nandap wanda a baya yake kula da Babban Filin Jiragen Sama na Murtala Mohammed da ke Legas a yanzu kuma aka sauya masa zuwa Sashen Bayar da Takardu ga Bakin Waje (CERPAC) a shalkwata.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, ACG Abdullahi M Usman a yanzu shi ne Shugaban Sashen Kula da Shige da Fice na Yau da Kullum a shalkwatar hukumar, yayin da ACG BN Alawode ya zama Shugaban Sashen Kula da Walwala da Daidaiton Jinsi, sai kuma ACG EC Esedo da aka mayar zuwa Ofishin Shiyya ta hudu da ke Minna.

Shi kuwa ACG MA Ushie na Sashen Yaki da Damfara an mayar da shi zuwa Sashen Difilomasiyya da Fasfo, sai ACG ES Fagbamigba wanda a da yake kula da Babban ofishin Iyaka na Idi-Iroko da aka tura ya zama shugaban kula da iyakokin kasa na kan-tudu a shalkwata.

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

Daga cikin masu mukaman Kwanturololi da aka sauya wa wuraren aikin kuwa akwai Compt. AO Adesokan da aka mayar zuwa Babban Filin Jiragen Sama na Murtala Mohammed da ke Legas daga Sashen Horaswa da Inganta Kwazon Ma’aikata, yayin da mukaddashin babban jami’in ofoshin Kwanturola Janar, Compt. Ahmed Mustapha ya zama sabon Kwanturolan Kano.

Sauran sun hada da Compt. Shittu Olajire Fatai wanda a yanzu aka mayar da shi Ofishin Kula da Iyaka na Legas; da Compt. Gwama Muhammad wanda a yanzu shi aka ba shugabancin Ofishin kula da iyaka na Idi-Iroko; da Compt. MM Saddik wanda a yanzu aka ba shi matsayin Babban Jami’in Ofishin Kwanturola Janar.

Shi kuwa Compt. AO Bewaji an mayar da shi ne zuwa shalkwatar hukumar yayin da Compt. Michael Dike ya karbi ragama a matsayin Kwanturolan Iyaka na Seme da ke Legas. Shi kuwa Kwanturola mai kula da da’ar aiki an tura shi ya shugabanci yankin Jihar Osun yayin da Compt.

Sabo A Rano da ya kasance Kwamandan Makarantar Horas da Jami’ai ta Kano aka mayar da shi zuwa Jihar Gombe.

Bugu da kari, Compt. FD Dakat na Sashen kula da tasoshin ruwa aka mayar da shi zuwa Jihar Akwa Ibom inda zai karbi ragama daga Compt. GE Didel wanda aka mayar zuwa sashen shige da fice a shalkwata, da dai sauransu.

Shugaban Hukumar ta NIS, Isah Jere ya hori dukkan jami’an da aka sauya wa wuraren aikin su yi amfani da basirar da Allah ya yi musu a wuraren da aka tura su wajen inganta aiki da tsaron kasa. Sauyin aikin dai ya fara aiki ne nan take.

NIS
Abdulrazaq Yahuza
+ postsBio
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Saudiyya Ta Taya Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Wata Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Tsarin Shugabancin Duniya

MASU ALAKA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Rahotonni

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Next Post
Bukatar Tabbatar Da Sabon Kamfanin NNPC Ya Ba Mara da Kunya

Bukatar Tabbatar Da Sabon Kamfanin NNPC Ya Ba Mara da Kunya

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.