ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Zai Halarci Taron Tattaunawa Da Kungiyar Tuntuba Ta Katsina

by El-Zaharadeen Umar
2 years ago
Buhari

Kungiyar tuntuba ta “Katsina Consultative Forum” za ta shirya wani taron tattaunawa a kan matsalar shaye-shaye da suke yi wa zaman lafiya Jihar Katsina da Kasa barazana wanda kuma ake sa ran cewa tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari na daga cikin manyan baki da za su halarci wannan taro a Katsina.

Shugaban Kungiyar Tuntuba na Jihar Katsina, Alhaji Aliyu Abubakar Danmusa ya bayyana haka a lokacin wani taron manema labarai wanda ya yi karin haske kan yadda taron zai kasance da kuma dalilin da ya sa suka sauki matsalar shaye-shaye a matsayin batun da za su tattauna a kansa.

  • Gwamna Bago Ya Yi Watsi Da Rahoton Haramta Sayar Da Giya A Neja
  • Gwamnatin Zamfara Ta Rufe Kasuwannin Shanu 11 Saboda Matsalar ‘Yan Bindiga A Jihar

Ya kara da cewa an gayyato masana daga kowane bangare domin baje kolin hanyoyin da za a yi amfani da su domin sannin hanyar da za a tunkari wannan annoba ta sha da fataucin miyagun kwayoyi da suke haifar da abubuwa marasa kyau a cikin al’umma.

ADVERTISEMENT

Haka kuma ya yi bayanin cewa ba harkar shan kwayoyi ba ce kadai matsala ba, yana mai cewa sannu a hankali za su rika daukar matsalolin daya bayan daya domin tattaunawa akan su tare da lalubu hanyoyin da gwamnatin da kuma masu ruwa da tsaki za su bada gudunmawa domin magance su.

“Mun lura cewa matsalar kwaya, ita ce ke jagoranci zuwa ga aikata manyan laifufuka da suka hada shiga harkar ‘yan bindiga da fashi da makami da fyade da sauran manyan laifufuka, saboda haka dole mu hada hannu domin tunkarar wannan matsala baki dayanmu” in ji shugaban.

LABARAI MASU NASABA

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

Alhaji Aliyu Abubakar ya kara da cewa wannan taron zai samu tagomashi daga masana da masu ruwa da tsaki da za su baje kolin basirarsu a kan wannan matsala, mutane irin su Dakta Usman Bugaje masanin magunguna da siyasa da shugabar hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta jihar Katsina, Dakta Asma’u Abdulkadir da kuma mai baiwa gwamnan Katsina shawara akan hana sha da fataucin kwayoyi na da cikin manyan baki a wajen taron

A cewarsa halartar manyan baki irin su tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari da gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umar Radda da Sarakunan Katsina da Daura na daga cikin abubuwan da za su karawa taron armashi da fatan cewa za a yi abainda ya kamata akan wannan matsala.

Haka kuma ya yi bayanin cewa an gayyaci matasa wadanda sune wannan matsala ta shafa kai tsaye musamman daliban jami’o’i da matasa masu yi wa kasa hidima da kungiyoyin da ba na gwamnati ba.

Wannan taro kamar yadda shugaban wannan kungiya ya bayyana za a gudunar da shi a ranar 31 ga watan Disamba, 2023 a baban dakin taron na masaukin shugaban kasa da ke fadar gwamnatin Jihar Katsina.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe
Labarai

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Kwankwaso
Labarai

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?
Nazari

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Next Post
Yadda Aka Shirya Wa ACG James Sunday Bikin Taya Murnar Karin Girma A Gombe

Yadda Aka Shirya Wa ACG James Sunday Bikin Taya Murnar Karin Girma A Gombe

LABARAI MASU NASABA

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025
Kwankwaso

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025
Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

November 15, 2025
Za A Yi Gwanjon Rigunan Messi Na Gasar Kofin Duniya Ta 2022 Da Kudi Tsagwagwa

Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi

November 15, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

November 15, 2025
Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.