• English
  • Business News
Wednesday, September 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Zai Halarci Taron Tattaunawa Da Kungiyar Tuntuba Ta Katsina

by El-Zaharadeen Umar
2 years ago
in Labarai
0
Kasa Da Wata Biyu Ya Bar Mulki, Shin Ko Buhari Ya Cika Wa ‘Yan Nijeriya Alkawarin Da Ya Yi Mu Su?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar tuntuba ta “Katsina Consultative Forum” za ta shirya wani taron tattaunawa a kan matsalar shaye-shaye da suke yi wa zaman lafiya Jihar Katsina da Kasa barazana wanda kuma ake sa ran cewa tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari na daga cikin manyan baki da za su halarci wannan taro a Katsina.

Shugaban Kungiyar Tuntuba na Jihar Katsina, Alhaji Aliyu Abubakar Danmusa ya bayyana haka a lokacin wani taron manema labarai wanda ya yi karin haske kan yadda taron zai kasance da kuma dalilin da ya sa suka sauki matsalar shaye-shaye a matsayin batun da za su tattauna a kansa.

  • Gwamna Bago Ya Yi Watsi Da Rahoton Haramta Sayar Da Giya A Neja
  • Gwamnatin Zamfara Ta Rufe Kasuwannin Shanu 11 Saboda Matsalar ‘Yan Bindiga A Jihar

Ya kara da cewa an gayyato masana daga kowane bangare domin baje kolin hanyoyin da za a yi amfani da su domin sannin hanyar da za a tunkari wannan annoba ta sha da fataucin miyagun kwayoyi da suke haifar da abubuwa marasa kyau a cikin al’umma.

Haka kuma ya yi bayanin cewa ba harkar shan kwayoyi ba ce kadai matsala ba, yana mai cewa sannu a hankali za su rika daukar matsalolin daya bayan daya domin tattaunawa akan su tare da lalubu hanyoyin da gwamnatin da kuma masu ruwa da tsaki za su bada gudunmawa domin magance su.

“Mun lura cewa matsalar kwaya, ita ce ke jagoranci zuwa ga aikata manyan laifufuka da suka hada shiga harkar ‘yan bindiga da fashi da makami da fyade da sauran manyan laifufuka, saboda haka dole mu hada hannu domin tunkarar wannan matsala baki dayanmu” in ji shugaban.

Labarai Masu Nasaba

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

Gwamna Yusuf Zai Kaddamar Da Majalisar Shurah Ta Jihar Kano

Alhaji Aliyu Abubakar ya kara da cewa wannan taron zai samu tagomashi daga masana da masu ruwa da tsaki da za su baje kolin basirarsu a kan wannan matsala, mutane irin su Dakta Usman Bugaje masanin magunguna da siyasa da shugabar hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta jihar Katsina, Dakta Asma’u Abdulkadir da kuma mai baiwa gwamnan Katsina shawara akan hana sha da fataucin kwayoyi na da cikin manyan baki a wajen taron

A cewarsa halartar manyan baki irin su tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari da gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umar Radda da Sarakunan Katsina da Daura na daga cikin abubuwan da za su karawa taron armashi da fatan cewa za a yi abainda ya kamata akan wannan matsala.

Haka kuma ya yi bayanin cewa an gayyaci matasa wadanda sune wannan matsala ta shafa kai tsaye musamman daliban jami’o’i da matasa masu yi wa kasa hidima da kungiyoyin da ba na gwamnati ba.

Wannan taro kamar yadda shugaban wannan kungiya ya bayyana za a gudunar da shi a ranar 31 ga watan Disamba, 2023 a baban dakin taron na masaukin shugaban kasa da ke fadar gwamnatin Jihar Katsina.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Bago Ya Yi Watsi Da Rahoton Haramta Sayar Da Giya A Neja

Next Post

Yadda Aka Shirya Wa ACG James Sunday Bikin Taya Murnar Karin Girma A Gombe

Related

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya
Ra'ayi Riga

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

2 hours ago
Gwamna Yusuf
Labarai

Gwamna Yusuf Zai Kaddamar Da Majalisar Shurah Ta Jihar Kano

3 hours ago
Da Ɗum-ɗumi: Tinubu Ya Mayar Da Shugabannin NTA Kan Muƙamansu Bayan Dakatar Da Su A Baya
Manyan Labarai

Da Ɗum-ɗumi: Tinubu Ya Mayar Da Shugabannin NTA Kan Muƙamansu Bayan Dakatar Da Su A Baya

5 hours ago
Rashin Shugabanci Nagari Ne Har Yanzu Ƙananan Yara Ke Mutuwa Saboda Zazzaɓin Cizon Sauro
Labarai

Rashin Shugabanci Nagari Ne Har Yanzu Ƙananan Yara Ke Mutuwa Saboda Zazzaɓin Cizon Sauro

7 hours ago
NSCDC Ta Kama Mutane 6 Da Ake Zargin Barayin Wayoyin Wutar Lantarki Ne A Kano
Manyan Labarai

NSCDC Ta Kama Mutane 6 Da Ake Zargin Barayin Wayoyin Wutar Lantarki Ne A Kano

9 hours ago
Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama
Ra'ayi Riga

Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama

9 hours ago
Next Post
Yadda Aka Shirya Wa ACG James Sunday Bikin Taya Murnar Karin Girma A Gombe

Yadda Aka Shirya Wa ACG James Sunday Bikin Taya Murnar Karin Girma A Gombe

LABARAI MASU NASABA

Sabuwar Ajandar Mulkin Duniya Ta Nuna Alhakin Da Kasar Sin Ta Dauka

Sabuwar Ajandar Mulkin Duniya Ta Nuna Alhakin Da Kasar Sin Ta Dauka

September 2, 2025
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

September 2, 2025
Gwamna Dauda Lawal A Shekara 60: Inda Akwai Fata, Akwai Mafita

Gwamna Dauda Lawal A Shekara 60: Inda Akwai Fata, Akwai Mafita

September 2, 2025
Babban Sakataren MDD: Sin Ta Taka Rawar Gani Sosai Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na Biyu

Babban Sakataren MDD: Sin Ta Taka Rawar Gani Sosai Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na Biyu

September 2, 2025
Shugaban Uganda: Jarin Sin Na Taimakawa Wajen Bunkasa Ci Gaban Kasashen Afirka

Shugaban Uganda: Jarin Sin Na Taimakawa Wajen Bunkasa Ci Gaban Kasashen Afirka

September 2, 2025
Gwamna Yusuf

Gwamna Yusuf Zai Kaddamar Da Majalisar Shurah Ta Jihar Kano

September 2, 2025
Xi: Alakar Sin Da Rasha Ta Zama Misali Na Kyakkyawar Dangantakar Manyan Kasashe

Xi: Alakar Sin Da Rasha Ta Zama Misali Na Kyakkyawar Dangantakar Manyan Kasashe

September 2, 2025
Xi Jinping Ya Jagoranci Taro Karo Na Bakwai Tsakanin Shugabannin Kasashen Sin Da Rasha Da Mongoliya

Xi Jinping Ya Jagoranci Taro Karo Na Bakwai Tsakanin Shugabannin Kasashen Sin Da Rasha Da Mongoliya

September 2, 2025
Da Ɗum-ɗumi: Tinubu Ya Mayar Da Shugabannin NTA Kan Muƙamansu Bayan Dakatar Da Su A Baya

Da Ɗum-ɗumi: Tinubu Ya Mayar Da Shugabannin NTA Kan Muƙamansu Bayan Dakatar Da Su A Baya

September 2, 2025
Sabuwar Ajandar Kasar Sin Ta Inganta Magance Gibin Kudi A Duniya

Sabuwar Ajandar Kasar Sin Ta Inganta Magance Gibin Kudi A Duniya

September 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.