ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Zai Kaddamar Da Ayyuka 7 A Ranar Talata –Fadar Shugaban Kasa

by Sadiq
2 years ago
Buhari

A ranar Talata ne shugaban kasa Muhammadu Buhari zai kaddamar da wasu ayyuka guda bakwai da ma’aikatar ayyuka da gidaje ta tarayya ta kammala a fadin kasar nan.

Mista Femi Adesina, mai magana da yawun shugaban kasa, wanda ya tabbatar da wannan ci gaban a wata sanarwa a ranar Litinin a Abuja, ya ce ayyukan sun yi daidai da kudurin gwamnatin Buhari na inganta da fadada kayayyakin more rayuwa.

  • Majalisar Lafiya Ta Duniya Ta Sake Yin Watsi Da Shawarar Dake Shafar Taiwan
  • Shugabancin Majalisa Ta 10: Katsalandan Din Gwamnati Ya Janyo Turka-Turka –  Hon. Bello

Ayyukan a cewar Adesina, sun kunshi manyan gadaje uku, sakatariyar gwamnatin tarayya guda uku da kuma hanya daya, yana mai cewa taron mai dimbin tarihi zai gudana ne a kan gadar Neja ta Biyu da aka fara a 2005.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, a shekarar 2014, an yi yunkurin fara aikin ta hanyar hadin gwiwar kamfanoni masu zaman kansu (PPP) amma hakan bai yi nasara ba.

Sai dai ya bayyana cewa an fara aikin ne a shekarar 2016 da asusun bunkasa ababen more rayuwa na shugaban kasa (PIDF).

LABARAI MASU NASABA

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

Mai taimaka wa shugaban kasar ya bayyana cewa sauran ayyukan da shugaban zai kaddamar sun hada da; gadar Loko-Oweto wadda ta ratsa kogin Benuwai domin hada Benuwai da Nasarawa da gadar Ikom da ke Kuros Riba.

“Aikin titin shi ne da aka kammala sashen sama da kilomita 200 na babbar hanyar Kano zuwa Kaduna da kuma sabbin sakatarorin gwamnatin tarayya guda uku.

“Babban Sakatarorin Gwamnatin Tarayya da ke Awka na nan, a karamar Hukumar Awka ta Kudu, a Anambra kuma yana kan fili mai fadin Hekta 5.106.”

Ya bayyana cewa an fara bayar da aikin ne a ranar 9 ga watan Disamba, 2011 amma a zahiri an kammala shi kuma ma’aikatar ayyuka da gidaje ta karbe shi a ranar 14 ga watan Yuli, 2022.

Sakatariyar tana da jimillar ofishi 498, zauren taro, dakunan kwamitoci guda hudu, ofishin gidan waya da sauransu.

Bugu da kari, Sakatariyar ta na da wuraren ajiye motoci da magudanan ruwa, kantin ma’aikata, injin kashe gobara da sauran muhimman wurare.

Na biyu, sakatariyar Gusau da ke Unguwan Dan Lawan a Jihar Zamfara.

Aikin yana kan fili mai fadin hekta 7.5 kuma ma’aikatar ta kammala shi a kusan 30 ga watan Nuwamba, 2022.

A cewar Adesina, na uku da za a kaddamar shi ne sakatariyar gwamnatin tarayya Yenagoa, wadda ke kan titin Alamieyeseigha, a Bayelsa.

“Yana kan fili mai fadin hekta 7.5 kuma an bayar da shi ne a ranar 9 ga watan Disamba 2011 amma kusan an kammala shi kuma ma’aikatar ta karbe shi a ranar 30 ga watan Nuwamba, 2022.”

Idan dai za a iya tunawa, shugaba Buhari ya kaddamar da na hudu, wato Sakatariyar gwamnatin tarayya da ke garin Bukar Sidi da ke kan titin Jos, Lafia, Nasarawa a watan Fabrairun wannan shekara.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2
Manyan Labarai

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

November 13, 2025
Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

November 13, 2025
Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule
Manyan Labarai

Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

November 13, 2025
Next Post
NAHCON Ta Nemi Alhazai Su Biya Kashi 40 Na Dala 250 Na Jigilarsu

NAHCON Ta Nemi Alhazai Su Biya Kashi 40 Na Dala 250 Na Jigilarsu

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

November 13, 2025
Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

November 13, 2025
Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

November 13, 2025
Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025
An Kafa Cibiyar Kiwon Lafiya Ta Hadin Gwiwa Ta Farko Tsakanin Sin Da Afirka A Guinea

An Kafa Cibiyar Kiwon Lafiya Ta Hadin Gwiwa Ta Farko Tsakanin Sin Da Afirka A Guinea

November 13, 2025
Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

November 13, 2025
NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane

NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane

November 13, 2025
Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25

Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25

November 13, 2025
Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu

Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.