• Leadership Hausa
Sunday, October 1, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Zai Kaddamar Da Ayyuka 7 A Ranar Talata –Fadar Shugaban Kasa

by Sadiq
4 months ago
in Manyan Labarai
0
Buhari Ya Kafa Tarihi Bayan Shekara 63
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Talata ne shugaban kasa Muhammadu Buhari zai kaddamar da wasu ayyuka guda bakwai da ma’aikatar ayyuka da gidaje ta tarayya ta kammala a fadin kasar nan.

Mista Femi Adesina, mai magana da yawun shugaban kasa, wanda ya tabbatar da wannan ci gaban a wata sanarwa a ranar Litinin a Abuja, ya ce ayyukan sun yi daidai da kudurin gwamnatin Buhari na inganta da fadada kayayyakin more rayuwa.

  • Majalisar Lafiya Ta Duniya Ta Sake Yin Watsi Da Shawarar Dake Shafar Taiwan
  • Shugabancin Majalisa Ta 10: Katsalandan Din Gwamnati Ya Janyo Turka-Turka –  Hon. Bello

Ayyukan a cewar Adesina, sun kunshi manyan gadaje uku, sakatariyar gwamnatin tarayya guda uku da kuma hanya daya, yana mai cewa taron mai dimbin tarihi zai gudana ne a kan gadar Neja ta Biyu da aka fara a 2005.

Ya kara da cewa, a shekarar 2014, an yi yunkurin fara aikin ta hanyar hadin gwiwar kamfanoni masu zaman kansu (PPP) amma hakan bai yi nasara ba.

Sai dai ya bayyana cewa an fara aikin ne a shekarar 2016 da asusun bunkasa ababen more rayuwa na shugaban kasa (PIDF).

Labarai Masu Nasaba

Daga Gobe 2 Ga Oktoba Farashin Buhun Simintin BUA Ya Koma N3,500 – Kamfanin

Shekara 100 Da Kafa IAR: Da Sakamakon Bincikenmu Aka Kafa Ginshikin Tattalin Arzikin Arewacin Nijeriya —Farfesa Ishiyaku

Mai taimaka wa shugaban kasar ya bayyana cewa sauran ayyukan da shugaban zai kaddamar sun hada da; gadar Loko-Oweto wadda ta ratsa kogin Benuwai domin hada Benuwai da Nasarawa da gadar Ikom da ke Kuros Riba.

“Aikin titin shi ne da aka kammala sashen sama da kilomita 200 na babbar hanyar Kano zuwa Kaduna da kuma sabbin sakatarorin gwamnatin tarayya guda uku.

“Babban Sakatarorin Gwamnatin Tarayya da ke Awka na nan, a karamar Hukumar Awka ta Kudu, a Anambra kuma yana kan fili mai fadin Hekta 5.106.”

Ya bayyana cewa an fara bayar da aikin ne a ranar 9 ga watan Disamba, 2011 amma a zahiri an kammala shi kuma ma’aikatar ayyuka da gidaje ta karbe shi a ranar 14 ga watan Yuli, 2022.

Sakatariyar tana da jimillar ofishi 498, zauren taro, dakunan kwamitoci guda hudu, ofishin gidan waya da sauransu.

Bugu da kari, Sakatariyar ta na da wuraren ajiye motoci da magudanan ruwa, kantin ma’aikata, injin kashe gobara da sauran muhimman wurare.

Na biyu, sakatariyar Gusau da ke Unguwan Dan Lawan a Jihar Zamfara.

Aikin yana kan fili mai fadin hekta 7.5 kuma ma’aikatar ta kammala shi a kusan 30 ga watan Nuwamba, 2022.

A cewar Adesina, na uku da za a kaddamar shi ne sakatariyar gwamnatin tarayya Yenagoa, wadda ke kan titin Alamieyeseigha, a Bayelsa.

“Yana kan fili mai fadin hekta 7.5 kuma an bayar da shi ne a ranar 9 ga watan Disamba 2011 amma kusan an kammala shi kuma ma’aikatar ta karbe shi a ranar 30 ga watan Nuwamba, 2022.”

Idan dai za a iya tunawa, shugaba Buhari ya kaddamar da na hudu, wato Sakatariyar gwamnatin tarayya da ke garin Bukar Sidi da ke kan titin Jos, Lafia, Nasarawa a watan Fabrairun wannan shekara.

Tags: BuhariFadar Shugaban KasaKaddamar Da Ayyuka
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Ci Tarar Kamfanin Facebook $1.3 Biliyan

Next Post

NAHCON Ta Nemi Alhazai Su Biya Kashi 40 Na Dala 250 Na Jigilarsu

Related

BUA
Manyan Labarai

Daga Gobe 2 Ga Oktoba Farashin Buhun Simintin BUA Ya Koma N3,500 – Kamfanin

4 hours ago
Shekara 100 Da Kafa IAR: Da Sakamakon Bincikenmu Aka Kafa Ginshikin Tattalin Arzikin Arewacin Nijeriya —Farfesa Ishiyaku
Manyan Labarai

Shekara 100 Da Kafa IAR: Da Sakamakon Bincikenmu Aka Kafa Ginshikin Tattalin Arzikin Arewacin Nijeriya —Farfesa Ishiyaku

11 hours ago
Batun Yadda Samari Ke Barin Taimakon Iyaye Su Kashe Wa ‘Yan Mata Kudi
Madubin Rayuwa

Batun Yadda Samari Ke Barin Taimakon Iyaye Su Kashe Wa ‘Yan Mata Kudi

12 hours ago
Buhari
Manyan Labarai

Jawabin Shugaba Tinubu Kan Cikar Nijeriya Shekaru 63 Da Samun ‘Yancin Kai

14 hours ago
Kungiyar Kwadago Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cire Tallafin Man Fetur
Manyan Labarai

NLC Da TUC Na Hada Kan Ma’aikata Don Tafka Gagarumin Yajin Aiki

1 day ago
Tinubu Ya Jaddada Aniyar Magance Rashin Tsaro Da Talauci A Nijeriya
Manyan Labarai

Tinubu Ya Jaddada Aniyar Magance Rashin Tsaro Da Talauci A Nijeriya

1 day ago
Next Post
NAHCON Ta Nemi Alhazai Su Biya Kashi 40 Na Dala 250 Na Jigilarsu

NAHCON Ta Nemi Alhazai Su Biya Kashi 40 Na Dala 250 Na Jigilarsu

LABARAI MASU NASABA

Kotu A Amurka Ta Umarci Jami’ar Chicago Ta Bai Wa Atiku Bayanan Karatun Tinubu

Kotu A Amurka Ta Umarci Jami’ar Chicago Ta Bai Wa Atiku Bayanan Karatun Tinubu

October 1, 2023
Tinubu

Ranar ‘Yanci: Tinubu Ya Kara Wa Kananan Ma’aikata N25,000 Kan Albashinsu

October 1, 2023
Hangzhou

Birnin Hangzhou Ya Samu Karuwar Masu Yawon Bude Ido Albarkacin Gasar Wasanni Ta Asiya Dake Gudana

October 1, 2023
Syria

Shugaban Syria: Manyan Tsare-tsare Uku Na duniya Su Ne Jagororin Sabuwar Duniya

October 1, 2023
BUA

Daga Gobe 2 Ga Oktoba Farashin Buhun Simintin BUA Ya Koma N3,500 – Kamfanin

October 1, 2023
Kasar Sin

Ofishin Jakadancin Kasar Sin Dake Najeriya Ya Shirya Bikin Murnar Cikar Sin Shekaru 74 Da Kafuwa

October 1, 2023
Yadda ‘Arewa Peace Ambassador Forum’ Ta Nada Sheikh Muhajjadina Jakadan Zaman Lafiya

Yadda ‘Arewa Peace Ambassador Forum’ Ta Nada Sheikh Muhajjadina Jakadan Zaman Lafiya

October 1, 2023
Amurka

Amurka Ita Ce “Daular Karya”Ta Ko Wace Fuska

October 1, 2023
Gwamnatin Tarayya Ta Yaba Da Ayyukan Bello Koko Na Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Kafa Sashi Na Musamman A NPA Don Inganta Ayyukanta

October 1, 2023
Dambe: An Fafata Tsakanin Dan Aliyu Da Rabe Shagon Ebola

Dambe: An Fafata Tsakanin Dan Aliyu Da Rabe Shagon Ebola

October 1, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.