ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Zai Kaddamar Da Ayyuka 7 A Ranar Talata –Fadar Shugaban Kasa

by Sadiq
3 years ago
Buhari

A ranar Talata ne shugaban kasa Muhammadu Buhari zai kaddamar da wasu ayyuka guda bakwai da ma’aikatar ayyuka da gidaje ta tarayya ta kammala a fadin kasar nan.

Mista Femi Adesina, mai magana da yawun shugaban kasa, wanda ya tabbatar da wannan ci gaban a wata sanarwa a ranar Litinin a Abuja, ya ce ayyukan sun yi daidai da kudurin gwamnatin Buhari na inganta da fadada kayayyakin more rayuwa.

  • Majalisar Lafiya Ta Duniya Ta Sake Yin Watsi Da Shawarar Dake Shafar Taiwan
  • Shugabancin Majalisa Ta 10: Katsalandan Din Gwamnati Ya Janyo Turka-Turka –  Hon. Bello

Ayyukan a cewar Adesina, sun kunshi manyan gadaje uku, sakatariyar gwamnatin tarayya guda uku da kuma hanya daya, yana mai cewa taron mai dimbin tarihi zai gudana ne a kan gadar Neja ta Biyu da aka fara a 2005.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, a shekarar 2014, an yi yunkurin fara aikin ta hanyar hadin gwiwar kamfanoni masu zaman kansu (PPP) amma hakan bai yi nasara ba.

Sai dai ya bayyana cewa an fara aikin ne a shekarar 2016 da asusun bunkasa ababen more rayuwa na shugaban kasa (PIDF).

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

Mai taimaka wa shugaban kasar ya bayyana cewa sauran ayyukan da shugaban zai kaddamar sun hada da; gadar Loko-Oweto wadda ta ratsa kogin Benuwai domin hada Benuwai da Nasarawa da gadar Ikom da ke Kuros Riba.

“Aikin titin shi ne da aka kammala sashen sama da kilomita 200 na babbar hanyar Kano zuwa Kaduna da kuma sabbin sakatarorin gwamnatin tarayya guda uku.

“Babban Sakatarorin Gwamnatin Tarayya da ke Awka na nan, a karamar Hukumar Awka ta Kudu, a Anambra kuma yana kan fili mai fadin Hekta 5.106.”

Ya bayyana cewa an fara bayar da aikin ne a ranar 9 ga watan Disamba, 2011 amma a zahiri an kammala shi kuma ma’aikatar ayyuka da gidaje ta karbe shi a ranar 14 ga watan Yuli, 2022.

Sakatariyar tana da jimillar ofishi 498, zauren taro, dakunan kwamitoci guda hudu, ofishin gidan waya da sauransu.

Bugu da kari, Sakatariyar ta na da wuraren ajiye motoci da magudanan ruwa, kantin ma’aikata, injin kashe gobara da sauran muhimman wurare.

Na biyu, sakatariyar Gusau da ke Unguwan Dan Lawan a Jihar Zamfara.

Aikin yana kan fili mai fadin hekta 7.5 kuma ma’aikatar ta kammala shi a kusan 30 ga watan Nuwamba, 2022.

A cewar Adesina, na uku da za a kaddamar shi ne sakatariyar gwamnatin tarayya Yenagoa, wadda ke kan titin Alamieyeseigha, a Bayelsa.

“Yana kan fili mai fadin hekta 7.5 kuma an bayar da shi ne a ranar 9 ga watan Disamba 2011 amma kusan an kammala shi kuma ma’aikatar ta karbe shi a ranar 30 ga watan Nuwamba, 2022.”

Idan dai za a iya tunawa, shugaba Buhari ya kaddamar da na hudu, wato Sakatariyar gwamnatin tarayya da ke garin Bukar Sidi da ke kan titin Jos, Lafia, Nasarawa a watan Fabrairun wannan shekara.

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
NAHCON Ta Nemi Alhazai Su Biya Kashi 40 Na Dala 250 Na Jigilarsu

NAHCON Ta Nemi Alhazai Su Biya Kashi 40 Na Dala 250 Na Jigilarsu

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.