ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Zai Kaddamar Da Ayyuka 7 A Ranar Talata –Fadar Shugaban Kasa

by Sadiq
3 years ago
Buhari

A ranar Talata ne shugaban kasa Muhammadu Buhari zai kaddamar da wasu ayyuka guda bakwai da ma’aikatar ayyuka da gidaje ta tarayya ta kammala a fadin kasar nan.

Mista Femi Adesina, mai magana da yawun shugaban kasa, wanda ya tabbatar da wannan ci gaban a wata sanarwa a ranar Litinin a Abuja, ya ce ayyukan sun yi daidai da kudurin gwamnatin Buhari na inganta da fadada kayayyakin more rayuwa.

  • Majalisar Lafiya Ta Duniya Ta Sake Yin Watsi Da Shawarar Dake Shafar Taiwan
  • Shugabancin Majalisa Ta 10: Katsalandan Din Gwamnati Ya Janyo Turka-Turka –  Hon. Bello

Ayyukan a cewar Adesina, sun kunshi manyan gadaje uku, sakatariyar gwamnatin tarayya guda uku da kuma hanya daya, yana mai cewa taron mai dimbin tarihi zai gudana ne a kan gadar Neja ta Biyu da aka fara a 2005.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, a shekarar 2014, an yi yunkurin fara aikin ta hanyar hadin gwiwar kamfanoni masu zaman kansu (PPP) amma hakan bai yi nasara ba.

Sai dai ya bayyana cewa an fara aikin ne a shekarar 2016 da asusun bunkasa ababen more rayuwa na shugaban kasa (PIDF).

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Mai taimaka wa shugaban kasar ya bayyana cewa sauran ayyukan da shugaban zai kaddamar sun hada da; gadar Loko-Oweto wadda ta ratsa kogin Benuwai domin hada Benuwai da Nasarawa da gadar Ikom da ke Kuros Riba.

“Aikin titin shi ne da aka kammala sashen sama da kilomita 200 na babbar hanyar Kano zuwa Kaduna da kuma sabbin sakatarorin gwamnatin tarayya guda uku.

“Babban Sakatarorin Gwamnatin Tarayya da ke Awka na nan, a karamar Hukumar Awka ta Kudu, a Anambra kuma yana kan fili mai fadin Hekta 5.106.”

Ya bayyana cewa an fara bayar da aikin ne a ranar 9 ga watan Disamba, 2011 amma a zahiri an kammala shi kuma ma’aikatar ayyuka da gidaje ta karbe shi a ranar 14 ga watan Yuli, 2022.

Sakatariyar tana da jimillar ofishi 498, zauren taro, dakunan kwamitoci guda hudu, ofishin gidan waya da sauransu.

Bugu da kari, Sakatariyar ta na da wuraren ajiye motoci da magudanan ruwa, kantin ma’aikata, injin kashe gobara da sauran muhimman wurare.

Na biyu, sakatariyar Gusau da ke Unguwan Dan Lawan a Jihar Zamfara.

Aikin yana kan fili mai fadin hekta 7.5 kuma ma’aikatar ta kammala shi a kusan 30 ga watan Nuwamba, 2022.

A cewar Adesina, na uku da za a kaddamar shi ne sakatariyar gwamnatin tarayya Yenagoa, wadda ke kan titin Alamieyeseigha, a Bayelsa.

“Yana kan fili mai fadin hekta 7.5 kuma an bayar da shi ne a ranar 9 ga watan Disamba 2011 amma kusan an kammala shi kuma ma’aikatar ta karbe shi a ranar 30 ga watan Nuwamba, 2022.”

Idan dai za a iya tunawa, shugaba Buhari ya kaddamar da na hudu, wato Sakatariyar gwamnatin tarayya da ke garin Bukar Sidi da ke kan titin Jos, Lafia, Nasarawa a watan Fabrairun wannan shekara.

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
NAHCON Ta Nemi Alhazai Su Biya Kashi 40 Na Dala 250 Na Jigilarsu

NAHCON Ta Nemi Alhazai Su Biya Kashi 40 Na Dala 250 Na Jigilarsu

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.