ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NAHCON Ta Nemi Alhazai Su Biya Kashi 40 Na Dala 250 Na Jigilarsu

by Sadiq
3 years ago
NAHCON

Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta yi amai ta lashe kan alkawarin da ta yi na cewa maniyyata ba za su biya karin kudi ba kan karin dala 250 da aka yi na jigilar jiragen sama.

An bayyana cewa, kamfanonin jiragen sama na cikin gida da ke gudanar da aikin Hajji sun bukaci a kara kudin aikin Hajji da dala 250, sakamakon rikicin da ake fama da shi a kasar Sudan, wanda zai bukaci karin lokacin zuwa kasar Saudiyya.

  • Buhari Zai Kaddamar Da Ayyuka 7 A Ranar Talata –Fadar Shugaban Kasa
  • An Ci Tarar Kamfanin Facebook $1.3 Biliyan

An rufe sararin samaniyar Sudan tun bayan barkewar rikici a watan Afrilu.

ADVERTISEMENT

Sai dai da yake jawabi a Abuja yayin wani atisayen da aka shirya wa ma’aikatan NAHCON da hukumar alhazai ta jiha da masu gudanar da yawon bude ido masu zaman kansu, Zikrullah Hassan shugaban hukumar NAHCON ya bada tabbacin cewa ba za a bukaci maniyyatan su biya karin kudin ba.

“Kamfanonin jiragenmu na cikin gida bayan tattaunawa da dama sun amince da dala $250 a matsayin karin kudin tikitin jirgi domin gudanar da aikin na bana. Har yanzu muna neman duk hanyoyin da za mu warware wannan tsaiko. Har yanzu muna ba da gudummawa sosai don ganin an gaggauta warware rikicin Sudan ta yadda sararin samaniya zai ya bude kuma a daina kashe-kashen da ake yi wa al’ummar Sudan.”

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

“A NAHCON, muna neman dukkan hanyoyin da za mu tabbatar mun warware matsalar wannan karin kudin. Mun yanke shawarar cewa, ba za a bukaci maniyyata su biya karin kudade a hannun hukumomin alhazai na jiharsu ba. Ba za su bukaci karin kudi ba, ”in ji shi.

Sai dai a wata sanarwa a ranar Litinin, mataimakin daraktan yada labarai na NAHCON, Moisa Ubandawaki, ya ce hukumar ta yanke shawarar cewa maniyyatan za su biya kashi 40 cikin 100 na karin kudin jirgi bayan gwamnatin tarayya ta tallafa wa kamfanonin jiragen sama don yin jigilarsu.

“Hakan zai kara rage tsadar kudin jigilar maniyyatan Nijeriya. A baya dai gwamnati ta yi watsi da kashi 65% na kudin jiragen sama domin rage farashin aikin Hajji. Tare da wannan ci gaban, Karin dala 250 da aka tattauna da kamfanonin jiragen sama za a rage dala 55, ”in ji sanarwar.

“An kiyasta kowane mahajjaci zai biya dala 117, Hukumar ta yanke shawarar rage alawus na alhazai na 2023.”

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Arsenal Na Zawarcin Declan Rice

Arsenal Na Zawarcin Declan Rice

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.