• English
  • Business News
Saturday, May 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Kauce Wa Tasirin Kudi A Zabukan 2023 (Ra’ayinmu)

by Sulaiman
3 years ago
in Siyasa
0
kudi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan siyasa sun amince da cewa, kudi na da matukar muhimmanci a wajen samun nasara ko rashinta a yayin da suka tunkari zabuka a Nijeriya. Kawar da kudi a harkokin siyasar Nijeriya wani abu ne da ba zai taba yiwu ba gaba daya, dalilin haka kuma ba shi da wahalar ganewa.

A ‘yan shekarun nan an amince da cewa, ‘yan siyasa masu hannu da shuni sune a kan gaba a fafutukar kama madafun iko, yana iya kasancewa ne ko sun fito ne a matsayin masu takara kai tsaye ko kuma suna daukar nauyin wanda da yake takarar, saboda tsananin tasirin kudi a harkokin sisayar da ake fuskanta a 2023 wanda bashi da kudi ba a sa shi a cikin masu iya lashe zaben.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Bayar Da Umarnin Rufe Gadar Madatsar Ruwa Ta Tiga Dam Da Ke Kano

Tabbas tasirin kudi a harkokin siyasa lamari ne da bai tsaya a iyaka fagen siyasar Nijeriya ba, don ko a kasashen da suka cigaba harkar siyasa abu ne da yake da tsadar gaske kuma kudi na da tasiri kwarai da gaske. Amma bambanci da ake samu a tsakanin yanayin siyasar Nijeriya da ta kasashen da suka cigaba shi ne a can doka ta amince ‘yan jam’iyya da manyan kamfanoni su samarwa jam’iyya kudaden tafiyar da harkokinta na yakin neman zabe amma kuma dokar ta kayyade iyakar kudaden da za a iya kashewa, don kada a wuce gona iri. Amma ba haka abin yake ba a Nijeriya, don kuwa kafin wani dan siyasa ya fara yunkurin fara neman takarar kujerar gwamna ko ta shugaban kasa dole ya zamana yana da karfin samarwa da jam’iyyarsa kudi akalla kashi 80 na kudaden da ake bukata don tafiyar da harkokin da suka shafi jam’iyyar gaba daya, harkoki da suka hada da kudaden yakin neman zabe da sauransu. A wasu wuraren ana kashe kudaden ne ta hanyar daukar nauyin ‘yan jam’iyya masu zirga-zirgar tallata manufofi da akidun jam’iyyar a cikin mazabar mai takarar don jawo hanlakin masu zabe su zabe shi.

Amma ba haka abin yake ba a Nijeriya saboda tsananin talaucin da ake fuskanta yana da matukar sauki a sayi masu kada kuri’a a sassan Nijeriya. Rahoton Bankin Duniya na shekarar 2022 ya nuna cewa, wadanda suke a matsayin talauci sun kai mutum miliyan 95.1. abin da hakan ke nufi shi ne, tasirin kudi a siyasar Nijeriya zai cigaba da karuwa ne ba kakkautawa.

Idan za a iya tunawa a ranar Talata ce shugaban kasa Muhammadu Buhari a taronsa da Gwamnonin Jam’iyyar APC ya bayyana cewa, gwamnati ba za ta bari wasu masu rike da madafun iko su wulakanta ko yen barazana ga ‘yan Nijeriya ba a zabukan da ke tafe a 2023.

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Gwamnatin Kano Na Haramta Shirye-shiryen Siyasa Kai Tsaye

Gwamna Fintiri Ba Zai Bar PDP Ba – Humwashi

“Ba za mu amince wani ya yi amfani da kudadensa ko matsayinsa wajen yi wa al’umma barazana ko wulakanta su ba ta kowacce hanya. Wannan shi ne irin shugabanci da muke bukatar samu don ya cigaba daga inda muka tsaya. Nan da wata shida ‘yan Nijeriya za su tabbatar tare da godewa gwamnatin APC saboda a lokacin za su fahimci yadda muka gudanar da harkokin gwamnati cikin gaskiya da rikon amana,’’ in ji shi.

A halin yanzu ana samun kwarin giwa a kan yadda wasu Malaman addini ke kokarin yaki da yadda ake amfani da kudi a siyasar Nijeriya ta hanyar kin karbar kyautar kudi daga ‘yan siyasa. Kwanaki ne aka yi wani dan ‘yar takaddama a wani cocin Katolita da ke Jihar Kross Ribas inda wani Rabaren Dan Taratsi mai suna Rabaren Dakta John Ebele Ayah, Bisahap na yankin Uyo ya ki karbar kyautar makudan kudade daga Gwamna Ben Ayade.

Lamarin ya faru ne a Cocin St. Patrick da ke Ikot Ansa, Calabar, iyayin bikin nuna godiya a kan nada Maishari’a Emmanuel Agim Akomaye a matsayin Maishari’a a kutun Koli, Ayah ne ke jagorantar zaman addu’ar sai Gwamna Ayade ya sanar da bayar da tallafin Naira Miliyan 25 ga cocin a madadin ‘yalasa da gwamnati, nan take Bishap din ya karbi abin magana ya bayyana wa Gwamnan kin karbar kyautar, ya nemi Gwamnan ya yi amfani da kudaden wajen biyan ma’aikata albashin da suke bin gwamnati, wanna matakin ya samu yabo kwarai da gaske, mutane na ta yabo da Allah san barka”

Haka kuma kwanakin baya ne wani Malamin addnin kirista a garin Nsukka ya yi watsi da kyautar Naira Miliyan 10 da wasu shugabanin jam’iyyuar PDP suka bashi don ya goya musu baya a zaben da ke tafe a 2023.
Haka kuma idan za a iya tunawa wasu kungiyoyin addnin musulunci 2 sun yi watsi da kyautar Dala Miliyan 3 da tsohon Shugaban Kasa Goodluck Jonathan ya basu don su goya masa baya a zaben 2015.

Ra’ayin wannan jaridar shi ne, lallai wannan wasu halaye ne da ya kamata a yi koyi da su, musamman ganin wadannan hali na neman ba Malaman addini kudade wani kokari ne na ruruta wutar rikicin addini da na kabilanci a fadin kasar nan, saboda haka yakamata a nisanci wuraren ibaba da irin wannan kazantar.
A halin yanzu sabbin matakai da hukumar zabe ta (INEC) ta bullo da su, kamar aika sakamakon zabe ta hanyar na’ura mai kwakwalwa da amfani da na’urar BIBAS zai kawo karshen magudin zabe da suka hada da sace-sacen akwatin zabe da dangwala kuri’a barkatai.

Amma kasancewar, yan siyasar Nijeriya da wayon gaske har sun samar da sabbin hanyoyin kaucewa doka, inda a halin yanzu suke sayen kuri’ar gaba daya kai tsaye daga masu kada kuri’ar. Wannan matsalar tana shafar mutuncin Nijeriya saboda haka ya kuma zama dole a dakatar da sayen kuri’a, ya zama dole a hukunta dukkan wadanda aka kama suna sayen kuri’a a zaben da aka yi a Jihar Osun ba tare da bata lokaci ba don ya zama darasi ga sauran masu niyyar aikata irin wannan halin a zabukka na gaba.

A yayin da Nijeriya ke kara dumfara zaben shugaban kasa a 2023 muna kira ga ‘yan Nijeriya su zabi shugabanni masu nagarta wadanda za su iya kai kasar nan tudun muntsira.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Alakar Sarauniya Elizabeth II Da Nijeriya

Next Post

Tsaro: Wainar Da Aka Toya A Taron Gwamnoni Da Sarakunan Arewa A Abuja

Related

Dalilin Gwamnatin Kano Na Haramta Shirye-shiryen Siyasa Kai Tsaye
Siyasa

Dalilin Gwamnatin Kano Na Haramta Shirye-shiryen Siyasa Kai Tsaye

2 days ago
Gwamna Fintiri Ba Zai Bar PDP Ba – Humwashi
Siyasa

Gwamna Fintiri Ba Zai Bar PDP Ba – Humwashi

5 days ago
Gwamna Abba Kabir Ya Mayar Wa Da Bappa Bichi Martani
Siyasa

Gwamna Abba Kabir Ya Mayar Wa Da Bappa Bichi Martani

5 days ago
Atiku Ne Rikitacce Ba Tinubu Ba
Labarai

Atiku Ne Rikitacce Ba Tinubu Ba

1 week ago
Mataimakin Gwamnan Neja Ya Ki Halartar Bikin Ranar Ma’aikata, Ana Zargin Akwai Takun Saka
Siyasa

Mataimakin Gwamnan Neja Ya Ki Halartar Bikin Ranar Ma’aikata, Ana Zargin Akwai Takun Saka

1 week ago
‘Yan Siyasa Na Komawa APC Don Buƙatar Kansu, Ba Don Jama’a Ba – Dalung
Siyasa

‘Yan Siyasa Na Komawa APC Don Buƙatar Kansu, Ba Don Jama’a Ba – Dalung

1 week ago
Next Post
Tsaro: Wainar Da Aka Toya A Taron Gwamnoni Da Sarakunan Arewa A Abuja

Tsaro: Wainar Da Aka Toya A Taron Gwamnoni Da Sarakunan Arewa A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

May 9, 2025
Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

May 9, 2025
Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

May 9, 2025
Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

May 9, 2025
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.