• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Kawo Karshen Karin Kudin Kiran Waya Da Na Data

byBello Hamza and Sulaiman
7 months ago
NCC

A kwanan baya ne, Hukumar Sadarwa ta Kasa NCC ta sahalewa Kamfanonin Sadarwa na Kasar nan yin karin kaso 50 na kudin Data da kuma na kiran wayar tafi da gidan, inda lamarin ya haifar da cecekuce a tsakain ‘yan Nijeriya, musamman talakawa da ke amfani da kafar sadarwa.

Wannan karin ya zo ne, daidai lokacin da akasarin talakawan kasar, ke ci gaba da fuskantar matsin tattalin arziki, biyo bayan tsauraran tsare-tsaren da Gwamnatin Tarayya mai ci ta kirkiro da su.

  • Zargin Kisan Kiristoci A Nijeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Rahoton Amurka
  • Sin Ta Mika Tallafin Wasu Jirage Marasa Matuka Na Inganta Noma Ga Kasar Zambia

Sai dai, batun ba boyayye ba ne, duba da yadda shekara da shekaru, masana’antun sadarwa a kasar, ba su iya gudanar da ayyukansu, yadda ya dace.

Duk da wannan karin na farashin Data da na kiran wayar da Kamfanonin suka yi, har yanzu ba su iya gamsar da ‘yan kasar da ayyukansu, wanda hakan ke kara sanyawa ‘yan Nigeriya ke fitar da rai daga ayyukan masana’antun.

A yayin da masu kamfanonin sadawar suka hakikance cewa, dole ne ya sanya suka yi karin, musamman domin su inganta gudanar da ayyukansu da samar da kayan aiki, amma ‘yan Nijeriya da dama suna kwan-kwanton kan yadda masu kamfanonin za su yi amfani da karin kudin shigarsu, domin ainganta ayyukansu.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

A Daina Gaggawar Murnar Samun Nasara Kan Ta’addanci A Nijeriya

Sai dai, idan za a yiwa wadannan Kamfanonin adalci, sun jima suna yin cajin farashinsu da sauki, musamman idan aka kwatanta da sauran fannonin.

Bugu da kari, matsin tattalin azrkin kasa, hauhawan farashin kaya, cire tallafin man fetur, karin farashin makamashi, karin farashin kudin wutar lantarki,sun kara zamowa Kamfanonin sadarwar matsala wajen ci gaba da samun riba.

Kazalika, wadannan matsalolin sun kai ga har sun shafi ma’aikatan da ke aiki a wadannan Kamfanonin, duba da yadda Kamfanonin suka gaza karawa ma’aikatansu albashi.

Sai dai, Kamfanonin sadawarwa MTN, Glo, Airtelda kuma 9mobile, suna hakilon lalubo da mafita kan yanewar kiran waya da rashin gudun da Data da rashin samun sadarwa.
Masu Kamfanonin sun bayyana cewa, ‘yan Nijeriya za su ci gaba da fuskantar ingancin ayyukan Kamfanonin, matukar za a ci gaba da fuskantar matsalar wutar lantarki da lalata masu kayan aikinsu.

Kungiyr da ke bai wa Kafanonin Sadawar Lasisi ta Kasa ALTON, ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta kawo dauki, domin a magance rashin ingancin ayyukan Kamfanonin a kasar.

Hukumar ta NCC ta alakanta rashin ignacin ayyukan Kamfanonin kan yadda ake lalata masu na’urorinsu a fadin kasar, musamman duba da cewa, gudanar da ingantaccen aikin Kamfanonin shi ne, ginshikin samar da sadarwa.

Kamfanonin sadawar a kasar nan na bukatar ayi masu garanbawul, kuma ya zama wajibi Hukumar NCC ta zargi Kamfanonin sadarwar, kan gazawar su ta rashin samar da ingantaccen aiki, musamman domin masu amfani da kakafen sadarwar, sun san da cewa, suna morar kudadensu.

Bugu da kari, ya zama wajibi Hukumar NCC ta mayar da hankali wajen tabbatar da cewa, ana bai wa masu amfani da kamfaninin sadarwar kariyar da ta kamata da kuma tabbatar da cewa, suna amfana da ayyukan Kamfanonin ba tare da fuskantar wata tangarda daga ayyukansu ba.

Kazaliaka, ya kamata Hukumar ta NCC ta kara mayar da hankaili wajen sanya gasa a masana’antar Sadarwar da kuma sanar da wata sabuwar kasuwa, wanda hakan zai sanya masu amfanin da Kamfanonin sadarwa a kasar za su zabi Kamfanonin sadarwar da suke ganin, za su biya masu bukatarasu, ba tare da fuskantar wata matsala.

Lokaci ya yi da Kamfanonin sadawar da ke a kasar nan, su tabbatar da cewa, suna mayarda hankali wajen bai wa masu amfani da layukan sadarwa a kasar kariyar da ta kamata, Kamfanonin su kuma tabatar da cewa, suna zuba hannun jari wajen kara inganta ayyukansu, musamman domin amfanin daukacin ‘yan Nijeriya.

Bugu da kari, yana da kyau, Kamfanonin sadarwar da ke a kasar nan, su tashi tsaye wajen lalubo da mafita kan kalubalen da masa’antar ke fuskanta, musamman domin masana;antar, ta ci gaba da dorewa.

Idan har a kasar nan, ba a dauku matakan inganta masana’antar ba, to tabbas wata rana, za ta zama sai dai Buzunta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Fyade
Ra'ayinmu

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

September 7, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Ra'ayinmu

A Daina Gaggawar Murnar Samun Nasara Kan Ta’addanci A Nijeriya

August 29, 2025
Ra'ayinmu

Bukatar Hukunta Masu Jagorantar Kashe-kashe A Nijeriya

July 25, 2025
Next Post
Yadda Azumi Yake Sa Tsoron Allah

Azumi Ya Dara Wa Sauran Ibadu

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version