• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buƙatar Rijistar Sabbin Jam’iyyu Ta Kai 144 — INEC

by Abubakar Sulaiman
2 months ago
in Labarai
0
Buƙatar Rijistar Sabbin Jam’iyyu Ta Kai 144 — INEC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta bayyana cewa ta karɓi ƙarin buƙatu guda 10 daga ƙungiyoyin da ke neman rijista a matsayin jam’iyyun siyasa, wanda hakan ya kai yawan buƙatun da ke gabanta zuwa 144.

Kwamishinan INEC na ƙasa kuma Shugaban kwamitin bayar da bayani da Ilimantar da masu zaɓe, Sam Olumekun, ne ya bayyana hakan a Abuja ranar Alhamis. Ya ce hukumar na nazarin dukkan wasiƙun sha’awa zama jam’iyya da ta karɓa domin tantance waɗanda suka cika sharuɗɗan da za su ba su damar ci gaba zuwa matakin neman rijista.

  • INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12
  • Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

Olumekun ya kuma bayyana cewa adadin mutanen da suka yi rijista a ƙarƙashin ci gaba da rajistar masu kaɗa ƙuri’a (CVR) a jihar Anambra ya kai 168,187. Cikin waɗannan, 97,832 (kashi 58%) mata ne, yayin da 70,355 (kashi 42%) maza ne. Masu shekaru 18 zuwa 34 sun kai 90,763 (kashi 53.97%); ‘yan kasuwa da masu sana’a sun kai 62,157 (kashi 36.92%) sannan ɗalibai sun kai 44,243 (kashi 26.31%).

Dangane da mutane masu buƙata ta musamman (PWDs), 303 (kashi 24.92%) na fama da nakasa ta jiki, sai kuma 207 (kashi 17.02%) Zabiya (albinism). Olumekun ya ce mataki na gaba da hukumar za ta ɗauka shi ne bayyana jerin sunayen sabbin masu rijistar domin bayar da dama ga ‘yan ƙasa su yi iƙirari ko ƙin amincewa da sunaye, domin su ne ainihin masu wannan rijista.

A cewar sa, za a gudanar da wannan aiki ne a dukkan mazabu 326 da ke jihar Anambra daga ranar Asabar, 26 ga Yuli, 2025. Bayan kammala wannan aiki da kuma amfani da na’urar tantance bayyanar mutum ta hanyar fasahar hoto da yatsa (ABIS), za a haɗa sabbin rijistoci da na baya sannan a wallafa su bisa rumfar zabe. Daga nan sai hukumar ta bayyana kwanaki da wuraren da za a fara rabon katin zaɓe na dindindin (PVC) ga sabbin masu rijista da kuma waɗanda suka nemi sauya rumfa ko maye gurbin katin da ya ɓace ko ya lalace.

Labarai Masu Nasaba

Ta Yaya Zan Yi Tattalin Mijina?

Ajali: Wasu Ƴan Ƙauye Sun Gujewa Ƴan Bindiga Sun Nutse A Ruwa

Olumekun ya ƙara da cewa, katunan zaɓe na rijistar da ta gabata ma za su kasance a shirye don karɓa. Ya ce da saura kwanaki 105 zuwa zaɓe, INEC ta san lokaci ya matse, amma tana tabbatar da cewa sabbin masu rijista a jihar Anambra za su samu damar karɓar katunansu kafin zaɓen.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: INEC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI 

Next Post

Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da EU Karo Na 25 Tare Da Shugaban Majalisar EU Da Shugabar Hukumar EU

Related

Ta Yaya Zan Yi Tattalin Mijina?
Labarai

Ta Yaya Zan Yi Tattalin Mijina?

5 minutes ago
Ajali: Wasu Ƴan Ƙauye Sun Gujewa Ƴan Bindiga Sun Nutse A Ruwa
Labarai

Ajali: Wasu Ƴan Ƙauye Sun Gujewa Ƴan Bindiga Sun Nutse A Ruwa

1 hour ago
Tinubu Ya Halarci Ɗaurin Auren Ɗan Yari, Ya Kai Ziyara Gidan Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari
Labarai

Tinubu Ya Halarci Ɗaurin Auren Ɗan Yari, Ya Kai Ziyara Gidan Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari

2 hours ago
Sabon Kakin Ƴansanda Ya Ziyarci Cibiyar Ƙungiyar Ƴan Jarida A FCT
Labarai

Sabon Kakin Ƴansanda Ya Ziyarci Cibiyar Ƙungiyar Ƴan Jarida A FCT

2 hours ago
Magoya Bayan Aiyedatiwa Sun Ɓarke Da Sowa Bayan Nasara A Kotun Ƙoli
Manyan Labarai

Magoya Bayan Aiyedatiwa Sun Ɓarke Da Sowa Bayan Nasara A Kotun Ƙoli

5 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunƙurin Kawar Da Shanu Daga Titunan Abuja
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunƙurin Kawar Da Shanu Daga Titunan Abuja

6 hours ago
Next Post
Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da EU Karo Na 25 Tare Da Shugaban Majalisar EU Da Shugabar Hukumar EU

Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da EU Karo Na 25 Tare Da Shugaban Majalisar EU Da Shugabar Hukumar EU

LABARAI MASU NASABA

Ta Yaya Zan Yi Tattalin Mijina?

Ta Yaya Zan Yi Tattalin Mijina?

September 20, 2025
Ajali: Wasu Ƴan Ƙauye Sun Gujewa Ƴan Bindiga Sun Nutse A Ruwa

Ajali: Wasu Ƴan Ƙauye Sun Gujewa Ƴan Bindiga Sun Nutse A Ruwa

September 20, 2025
Tinubu Ya Halarci Ɗaurin Auren Ɗan Yari, Ya Kai Ziyara Gidan Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari

Tinubu Ya Halarci Ɗaurin Auren Ɗan Yari, Ya Kai Ziyara Gidan Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari

September 20, 2025
Sabon Kakin Ƴansanda Ya Ziyarci Cibiyar Ƙungiyar Ƴan Jarida A FCT

Sabon Kakin Ƴansanda Ya Ziyarci Cibiyar Ƙungiyar Ƴan Jarida A FCT

September 20, 2025
Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi

Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi

September 20, 2025
Makarantun Da Ba Ƙwararrun Malamai Za Su Rasa Zama Cibiyar Rubuta Jarrabawar NECO

Makarantun Da Ba Ƙwararrun Malamai Za Su Rasa Zama Cibiyar Rubuta Jarrabawar NECO

September 20, 2025
Magoya Bayan Aiyedatiwa Sun Ɓarke Da Sowa Bayan Nasara A Kotun Ƙoli

Magoya Bayan Aiyedatiwa Sun Ɓarke Da Sowa Bayan Nasara A Kotun Ƙoli

September 20, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunƙurin Kawar Da Shanu Daga Titunan Abuja

Gwamnatin Tarayya Na Yunƙurin Kawar Da Shanu Daga Titunan Abuja

September 20, 2025
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Sulhu Da Ƴan Bindiga A Katsina

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Sulhu Da Ƴan Bindiga A Katsina

September 20, 2025
INEC

Yadda Ɗantsoho Ya Mayar Da Hankali Wajen Farafaɗo Da Martaba Da Ƙimar NPA

September 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.