ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Chelsea Za Ta Fafata Da Real Madrid Da Manchester City A Amurka

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Chelsea

Kungiyar kwallon kafa ta Chelsea za ta fafata wasannin sada zumunta da Manchester City da kuma Real Madrid a kasar Amurka a wasannin shirin tunkarar kakar badi ta 2024 zuwa 2025. Kawo yanzu dai Chelsea tana ta 11 a teburin Premier League da maki 39, wadda saura wasanni 11 ya rage mata a kakar nan a gasar firimiya ta Ingila wanda za a iya cewa kakar wasa ce wadda magoya bayan kungiyar ba za su taba mantawa da ita ba saboda rashin kokari.

Sauran wasan da kungiyar ta Chelsea za ta fafata a Amurka har da wasa da kungiyar Wredham da Celtic da kuma Club America duka a kokarin kungiyar na ganin ta koma kan ganiyarta a kakar wasa mai zuwa. Chelsea mai buga gasar Premier League za ta yi tata burza da Manchester City ranar Asabar 3 ga watan Agusta sannan za kuma ta kece raini da Celtic a college football arens wato a Ohio Stadium a Columbus a birnin Ohio.

  • Azumi Lokaci Zafi: Yadda ‘Yan Kasuwar Kankara Ke Camamarsu A Yobe Da Zamfara
  • Rundunar ‘Yansandan Bauchi Ta Fara Cafko Masu Garkuwa Ta Amfani Da Fasahar Zamani

Ranar Talata 6 ga watan Agusta, Chelsea za ta fuskanci Real Madrid a Bank of America Stadium, Char-lotte a Carolina – filin da ta buga wasa a shekarar 2015 da kuma 2022. Jerin wasannin da Chelsea za ta buga a Amurka Chelsea da Wredham – Laraba 24 ga Yuli a Lebi Stadium a Santa Clara, Chelsea da Celtic – Asabar 27 ga Yuli a Notre Dame Stadium, Notre Dame, Indiana.

ADVERTISEMENT

Chelsea da Club America – Laraba 31 ga Juli a Mercedes-Benz Stadium a Atlanta, Georgia. Chelsea da Manchester City – Asabar 3 ga August a Ohio Stadium a Columbus, Ohio. Wasan da aka fafata a bayan nan tsakanin Chelsea da Manchester City.

Kakar wasa ta 2023 zuwa 2024
Premier League Asabar 17 ga watan Fabrairun 2024 Man City 1 – 1 Chelsea Premier League Lahadi 12 ga watan Nuwambar 2023 Chelsea 4 – 4 Man City Chelsea da Real Madrid – Talata 6 ga Agusta a Bank of America Stadium, Charlotte, Aewacin Carolina. Wasan da Chelsea da Real Madrid suka kara a baya bayan nan Champions League Talata 18 ga watan Afirilun 2023.

LABARAI MASU NASABA

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25

Chelsea 0 – 2 Real Madrid Champions League Laraba 12 ga watan Afirilun We 2023 Real Madrid 2 – 0 Chelsea Wasan Chelsea da Man City daya ne daga tsarin gurmurzu tsakanin fitattun kungiyoyin tamaula da aka shirya mai suna 2024 FC Series. Haka kuma Chelsea da Real Madrid za su kece raini a daya daga gumurzun Soccer Champions Tour da ake yi tsakanin manyan kungiyoyi da ake buga a Amurka.

Filayen da Chelsea za ta buga wasa a Amurka

Filin wasa da ke Ohio mai dumbin tarihi zai bai wa magoya bayan Chelsea damar ganin ‘yan wasa da shirin da take na tunkarar kakar wasa ta badi – wadda kaka ta biyu kenan da ba za ta buga gasar zakarun Turai ba – a filin ne za ta fafata da Manchester City. Sai kuma filin was ana Bank of America Stadium yana daga cikin filin da Chelsea za ta gwada ‘yan kwallon da za ta yi amfani da su a badi – a nan ne za a kece raini tsakanin Chelsea da Real Madrid.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4
Manyan Labarai

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25
Wasanni

Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25

November 13, 2025
Nijeriya Za Ta Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Gusau
Wasanni

Nijeriya Za Ta Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Gusau

November 13, 2025
Next Post
Sin Da EU Sun Gudanar Da Taron Tattaunawa Domin Inganta Musaya Tsakanin Jama’arsu

Sin Da EU Sun Gudanar Da Taron Tattaunawa Domin Inganta Musaya Tsakanin Jama’arsu

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025
Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

November 13, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

November 13, 2025
Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

November 13, 2025
Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

November 13, 2025
Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025
An Kafa Cibiyar Kiwon Lafiya Ta Hadin Gwiwa Ta Farko Tsakanin Sin Da Afirka A Guinea

An Kafa Cibiyar Kiwon Lafiya Ta Hadin Gwiwa Ta Farko Tsakanin Sin Da Afirka A Guinea

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.