ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Chelsea Za Ta Fafata Da Real Madrid Da Manchester City A Amurka

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Chelsea

Kungiyar kwallon kafa ta Chelsea za ta fafata wasannin sada zumunta da Manchester City da kuma Real Madrid a kasar Amurka a wasannin shirin tunkarar kakar badi ta 2024 zuwa 2025. Kawo yanzu dai Chelsea tana ta 11 a teburin Premier League da maki 39, wadda saura wasanni 11 ya rage mata a kakar nan a gasar firimiya ta Ingila wanda za a iya cewa kakar wasa ce wadda magoya bayan kungiyar ba za su taba mantawa da ita ba saboda rashin kokari.

Sauran wasan da kungiyar ta Chelsea za ta fafata a Amurka har da wasa da kungiyar Wredham da Celtic da kuma Club America duka a kokarin kungiyar na ganin ta koma kan ganiyarta a kakar wasa mai zuwa. Chelsea mai buga gasar Premier League za ta yi tata burza da Manchester City ranar Asabar 3 ga watan Agusta sannan za kuma ta kece raini da Celtic a college football arens wato a Ohio Stadium a Columbus a birnin Ohio.

  • Azumi Lokaci Zafi: Yadda ‘Yan Kasuwar Kankara Ke Camamarsu A Yobe Da Zamfara
  • Rundunar ‘Yansandan Bauchi Ta Fara Cafko Masu Garkuwa Ta Amfani Da Fasahar Zamani

Ranar Talata 6 ga watan Agusta, Chelsea za ta fuskanci Real Madrid a Bank of America Stadium, Char-lotte a Carolina – filin da ta buga wasa a shekarar 2015 da kuma 2022. Jerin wasannin da Chelsea za ta buga a Amurka Chelsea da Wredham – Laraba 24 ga Yuli a Lebi Stadium a Santa Clara, Chelsea da Celtic – Asabar 27 ga Yuli a Notre Dame Stadium, Notre Dame, Indiana.

ADVERTISEMENT

Chelsea da Club America – Laraba 31 ga Juli a Mercedes-Benz Stadium a Atlanta, Georgia. Chelsea da Manchester City – Asabar 3 ga August a Ohio Stadium a Columbus, Ohio. Wasan da aka fafata a bayan nan tsakanin Chelsea da Manchester City.

Kakar wasa ta 2023 zuwa 2024
Premier League Asabar 17 ga watan Fabrairun 2024 Man City 1 – 1 Chelsea Premier League Lahadi 12 ga watan Nuwambar 2023 Chelsea 4 – 4 Man City Chelsea da Real Madrid – Talata 6 ga Agusta a Bank of America Stadium, Charlotte, Aewacin Carolina. Wasan da Chelsea da Real Madrid suka kara a baya bayan nan Champions League Talata 18 ga watan Afirilun 2023.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

Chelsea 0 – 2 Real Madrid Champions League Laraba 12 ga watan Afirilun We 2023 Real Madrid 2 – 0 Chelsea Wasan Chelsea da Man City daya ne daga tsarin gurmurzu tsakanin fitattun kungiyoyin tamaula da aka shirya mai suna 2024 FC Series. Haka kuma Chelsea da Real Madrid za su kece raini a daya daga gumurzun Soccer Champions Tour da ake yi tsakanin manyan kungiyoyi da ake buga a Amurka.

Filayen da Chelsea za ta buga wasa a Amurka

Filin wasa da ke Ohio mai dumbin tarihi zai bai wa magoya bayan Chelsea damar ganin ‘yan wasa da shirin da take na tunkarar kakar wasa ta badi – wadda kaka ta biyu kenan da ba za ta buga gasar zakarun Turai ba – a filin ne za ta fafata da Manchester City. Sai kuma filin was ana Bank of America Stadium yana daga cikin filin da Chelsea za ta gwada ‘yan kwallon da za ta yi amfani da su a badi – a nan ne za a kece raini tsakanin Chelsea da Real Madrid.

Chelsea
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Yaushe Za A Fara Kofin Zakarun Turai
  • Abba Ibrahim Wada
    Messi Ya Yi Ritaya A Argentina: Da Me Za Mu Iya Tuna Gwarzon Duniyar?
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye ‘Yan wasan Nijeriya Da Za Su Buga Gasar Firimiyar Ingila Ta Bana?
  • Abba Ibrahim Wada
    Chelsea A Ƙarƙashin Xavi Alonso

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
Wasanni

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

September 8, 2026
Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
Wasanni

Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain

September 7, 2026
Next Post
Sin Da EU Sun Gudanar Da Taron Tattaunawa Domin Inganta Musaya Tsakanin Jama’arsu

Sin Da EU Sun Gudanar Da Taron Tattaunawa Domin Inganta Musaya Tsakanin Jama’arsu

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.