• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaban Kasar Sin Dama Ce Ba Kalubale Ba

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ci Gaban Kasar Sin Dama Ce Ba Kalubale Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kalaman shugaban kasar Sin Xi Jinping, yayin da yake zantawa da sakataren harkokin wajen Amurka dake ziyara a kasar Sin Anthony Blinke, sun bayyana wasu muhimman batutuwan jan hankali ga Amurka.

Zan iya cewa kalaman wata manuniya ce ga Amurka cewa, hanyar da ta dauka ba za ta bulle ba, kana jan hankali ne gare ta ta gyara kura-kuranta.

  • Aiwatar Da Alkawain Da Aka Yi Yana Da Muhimmanci

A cewar Shugaba Xi, takarar manyan kasashen duniya ba ta wakiltar yanayin da ake ciki, hakan kuma ba zai taba iya magance matsalolin Amurka ko kalubalen da duniya ke fuskanta ba. Tabbas bai kamata yayin da ake fuskantar kalubale masu tsanani a duniya, babbar kasa kamar Amurka ta rika mayar da hankali kan takara ko yada jita-jita ba. Babu abun da wadannan abubuwa za su haifar face kara tada hankalin duniya da ta’azzara matsalolin da ake fuskanta.

Amurka ta kasance mai yin amai, kuma ta lashe. Ta kan nace cewa ba ta neman takara da kasar Sin ko kuma ba ta goyon bayan ’yancin yankin Taiwan na kasar, sai dai ayyukanta na yin hannun riga da abubuwan da take furtawa. A halin da ake ciki, duniya na bukatar Amurka mai sanin ya kamata da cika alkawarin da ta dauka da dakatar da kirkiro matsaloli ko ma kokarin karkatar da hankalin duniya daga yanayin da ake ciki.

A kalaman shugaba Xi, ya kamata kasashen su girmama muradun kowannensu, haka kuma, nasarorin da za su samu, dama ce maimakon barazana. Har kullum burin kasar Sin shi ne ganin ci gaban kasashe, yayin da Amurka ke daukar hakan a matsayin barazana.

Labarai Masu Nasaba

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

Doka ta ba kowacce kasa damar samun ci gaba, don haka, bai kamata wata kasa taya tilo ta kasance mai babakere ko bayar da izinin samun ci gaba ga sauran kasashe ba. Misali, kasar Sin ta samu ci gaba ne bisa jajircewarta, da hikimomi da basirar al’ummarta da ma tsarin shugabanci na kwarai, don haka babu wata kasa dake da izini ko damar iyakancewa ko kayyade ci gabanta. Ya dace Amurka da kawayenta su sakar ma Sin da ma sauran kasashe mara, su raya kansu ta yadda suke ganin ya fi dacewa da yanayinsu. Wannan a ganina, shi zai kai duniya ga samun ci gaba har ma da zaman lafiya. Kai ya riga ya waye, manufofin kasar Sin sun bambanta da na kasashen yamma, karfin kasar Sin ba ya nufin za ta yi wa duniya babakere. Har ila yau, ci gaban kasar Sin na zama dama ne ga kasashe masu burin raya kansu, Amurka da kanta na iya amfana daga hakan idan ta sauke girman kai da neman babakere.

Duk da kalubalen dake akwai da ma dimbin banbance-bambance, a matsayinsu na manyan kasashe dake zama abun koyi ga kasashe masu tasowa, har yanzu lokaci bai kurewa Sin da Amurka ba na lalubo hanyoyin inganta dangankarsu ko da kuwa za su yi hakan ne a hankali.

Duniya na bukatar hadin kansu, duba da kasancewarsu manya, dama tasirin da Sin ke da shi tsakanin kasashe masu tasowa mafi rinjaye, don haka ya dace su yi la’akari da hakan don tabbatar da zaman lafiya da dunkulewar da ake muradi a duniya. (Faeza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ronaldo Ya Kafa Tarihin Zama Ɗan Wasan Da Ya Fi Kowa Buga Wasannin Ƙasa Da Ƙasa

Next Post

Gwamnatin Kano Ta Fara Bincike Kan Zaftare Wa Ma’aikata Albashi

Related

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya
Daga Birnin Sin

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

1 hour ago
Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC
Daga Birnin Sin

Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

3 hours ago
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harbar Rukunonin Taurarin Dan Adam 10 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harbar Rukunonin Taurarin Dan Adam 10 

3 hours ago
An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

20 hours ago
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

20 hours ago
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II
Daga Birnin Sin

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

21 hours ago
Next Post
Gwamnatin Kano Ta Fara Bincike Kan Zaftare Wa Ma’aikata Albashi

Gwamnatin Kano Ta Fara Bincike Kan Zaftare Wa Ma'aikata Albashi

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

August 26, 2025
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

August 26, 2025
Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

August 26, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harbar Rukunonin Taurarin Dan Adam 10 

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harbar Rukunonin Taurarin Dan Adam 10 

August 26, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

August 26, 2025
Saka Zai Yi Jinyar Makonni 4 Sakamakon Rauni Da Ya Samu A Wasan Leeds

Saka Zai Yi Jinyar Makonni 4 Sakamakon Rauni Da Ya Samu A Wasan Leeds

August 26, 2025
‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

August 26, 2025
ÆŠaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

ÆŠaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

August 26, 2025
Yajin Aikin ASUU Na Barazana Ga Ci Gaban Kasa

ASUU Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Rashin Cika Mata Alƙawura

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.