• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaban Kasar Sin Dama Ce Ba Kalubale Ba

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ci Gaban Kasar Sin Dama Ce Ba Kalubale Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kalaman shugaban kasar Sin Xi Jinping, yayin da yake zantawa da sakataren harkokin wajen Amurka dake ziyara a kasar Sin Anthony Blinke, sun bayyana wasu muhimman batutuwan jan hankali ga Amurka.

Zan iya cewa kalaman wata manuniya ce ga Amurka cewa, hanyar da ta dauka ba za ta bulle ba, kana jan hankali ne gare ta ta gyara kura-kuranta.

  • Aiwatar Da Alkawain Da Aka Yi Yana Da Muhimmanci

A cewar Shugaba Xi, takarar manyan kasashen duniya ba ta wakiltar yanayin da ake ciki, hakan kuma ba zai taba iya magance matsalolin Amurka ko kalubalen da duniya ke fuskanta ba. Tabbas bai kamata yayin da ake fuskantar kalubale masu tsanani a duniya, babbar kasa kamar Amurka ta rika mayar da hankali kan takara ko yada jita-jita ba. Babu abun da wadannan abubuwa za su haifar face kara tada hankalin duniya da ta’azzara matsalolin da ake fuskanta.

Amurka ta kasance mai yin amai, kuma ta lashe. Ta kan nace cewa ba ta neman takara da kasar Sin ko kuma ba ta goyon bayan ’yancin yankin Taiwan na kasar, sai dai ayyukanta na yin hannun riga da abubuwan da take furtawa. A halin da ake ciki, duniya na bukatar Amurka mai sanin ya kamata da cika alkawarin da ta dauka da dakatar da kirkiro matsaloli ko ma kokarin karkatar da hankalin duniya daga yanayin da ake ciki.

A kalaman shugaba Xi, ya kamata kasashen su girmama muradun kowannensu, haka kuma, nasarorin da za su samu, dama ce maimakon barazana. Har kullum burin kasar Sin shi ne ganin ci gaban kasashe, yayin da Amurka ke daukar hakan a matsayin barazana.

Labarai Masu Nasaba

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Doka ta ba kowacce kasa damar samun ci gaba, don haka, bai kamata wata kasa taya tilo ta kasance mai babakere ko bayar da izinin samun ci gaba ga sauran kasashe ba. Misali, kasar Sin ta samu ci gaba ne bisa jajircewarta, da hikimomi da basirar al’ummarta da ma tsarin shugabanci na kwarai, don haka babu wata kasa dake da izini ko damar iyakancewa ko kayyade ci gabanta. Ya dace Amurka da kawayenta su sakar ma Sin da ma sauran kasashe mara, su raya kansu ta yadda suke ganin ya fi dacewa da yanayinsu. Wannan a ganina, shi zai kai duniya ga samun ci gaba har ma da zaman lafiya. Kai ya riga ya waye, manufofin kasar Sin sun bambanta da na kasashen yamma, karfin kasar Sin ba ya nufin za ta yi wa duniya babakere. Har ila yau, ci gaban kasar Sin na zama dama ne ga kasashe masu burin raya kansu, Amurka da kanta na iya amfana daga hakan idan ta sauke girman kai da neman babakere.

Duk da kalubalen dake akwai da ma dimbin banbance-bambance, a matsayinsu na manyan kasashe dake zama abun koyi ga kasashe masu tasowa, har yanzu lokaci bai kurewa Sin da Amurka ba na lalubo hanyoyin inganta dangankarsu ko da kuwa za su yi hakan ne a hankali.

Duniya na bukatar hadin kansu, duba da kasancewarsu manya, dama tasirin da Sin ke da shi tsakanin kasashe masu tasowa mafi rinjaye, don haka ya dace su yi la’akari da hakan don tabbatar da zaman lafiya da dunkulewar da ake muradi a duniya. (Faeza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ronaldo Ya Kafa Tarihin Zama Ɗan Wasan Da Ya Fi Kowa Buga Wasannin Ƙasa Da Ƙasa

Next Post

Gwamnatin Kano Ta Fara Bincike Kan Zaftare Wa Ma’aikata Albashi

Related

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

3 hours ago
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

4 hours ago
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700
Daga Birnin Sin

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

5 hours ago
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

6 hours ago
Hanya Mai Salon Musamman Da Kasar Sin Take Bi Wajen Raya Harkokin Kudi
Daga Birnin Sin

Hanya Mai Salon Musamman Da Kasar Sin Take Bi Wajen Raya Harkokin Kudi

7 hours ago
Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025

17 hours ago
Next Post
Gwamnatin Kano Ta Fara Bincike Kan Zaftare Wa Ma’aikata Albashi

Gwamnatin Kano Ta Fara Bincike Kan Zaftare Wa Ma'aikata Albashi

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.