ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaban Kasar Sin Dama Ce Ba Kalubale Ba

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

Kalaman shugaban kasar Sin Xi Jinping, yayin da yake zantawa da sakataren harkokin wajen Amurka dake ziyara a kasar Sin Anthony Blinke, sun bayyana wasu muhimman batutuwan jan hankali ga Amurka.

Zan iya cewa kalaman wata manuniya ce ga Amurka cewa, hanyar da ta dauka ba za ta bulle ba, kana jan hankali ne gare ta ta gyara kura-kuranta.

  • Aiwatar Da Alkawain Da Aka Yi Yana Da Muhimmanci

A cewar Shugaba Xi, takarar manyan kasashen duniya ba ta wakiltar yanayin da ake ciki, hakan kuma ba zai taba iya magance matsalolin Amurka ko kalubalen da duniya ke fuskanta ba. Tabbas bai kamata yayin da ake fuskantar kalubale masu tsanani a duniya, babbar kasa kamar Amurka ta rika mayar da hankali kan takara ko yada jita-jita ba. Babu abun da wadannan abubuwa za su haifar face kara tada hankalin duniya da ta’azzara matsalolin da ake fuskanta.

ADVERTISEMENT

Amurka ta kasance mai yin amai, kuma ta lashe. Ta kan nace cewa ba ta neman takara da kasar Sin ko kuma ba ta goyon bayan ’yancin yankin Taiwan na kasar, sai dai ayyukanta na yin hannun riga da abubuwan da take furtawa. A halin da ake ciki, duniya na bukatar Amurka mai sanin ya kamata da cika alkawarin da ta dauka da dakatar da kirkiro matsaloli ko ma kokarin karkatar da hankalin duniya daga yanayin da ake ciki.

A kalaman shugaba Xi, ya kamata kasashen su girmama muradun kowannensu, haka kuma, nasarorin da za su samu, dama ce maimakon barazana. Har kullum burin kasar Sin shi ne ganin ci gaban kasashe, yayin da Amurka ke daukar hakan a matsayin barazana.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Doka ta ba kowacce kasa damar samun ci gaba, don haka, bai kamata wata kasa taya tilo ta kasance mai babakere ko bayar da izinin samun ci gaba ga sauran kasashe ba. Misali, kasar Sin ta samu ci gaba ne bisa jajircewarta, da hikimomi da basirar al’ummarta da ma tsarin shugabanci na kwarai, don haka babu wata kasa dake da izini ko damar iyakancewa ko kayyade ci gabanta. Ya dace Amurka da kawayenta su sakar ma Sin da ma sauran kasashe mara, su raya kansu ta yadda suke ganin ya fi dacewa da yanayinsu. Wannan a ganina, shi zai kai duniya ga samun ci gaba har ma da zaman lafiya. Kai ya riga ya waye, manufofin kasar Sin sun bambanta da na kasashen yamma, karfin kasar Sin ba ya nufin za ta yi wa duniya babakere. Har ila yau, ci gaban kasar Sin na zama dama ne ga kasashe masu burin raya kansu, Amurka da kanta na iya amfana daga hakan idan ta sauke girman kai da neman babakere.

Duk da kalubalen dake akwai da ma dimbin banbance-bambance, a matsayinsu na manyan kasashe dake zama abun koyi ga kasashe masu tasowa, har yanzu lokaci bai kurewa Sin da Amurka ba na lalubo hanyoyin inganta dangankarsu ko da kuwa za su yi hakan ne a hankali.

Duniya na bukatar hadin kansu, duba da kasancewarsu manya, dama tasirin da Sin ke da shi tsakanin kasashe masu tasowa mafi rinjaye, don haka ya dace su yi la’akari da hakan don tabbatar da zaman lafiya da dunkulewar da ake muradi a duniya. (Faeza Mustapha)

Kasar Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Gwamnatin Kano Ta Fara Bincike Kan Zaftare Wa Ma’aikata Albashi

Gwamnatin Kano Ta Fara Bincike Kan Zaftare Wa Ma'aikata Albashi

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.