• Leadership Hausa
Wednesday, September 27, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cikar Nijeriya Shekara 62 Da ‘Yancin Kai

by Bello Hamza
12 months ago
in Manyan Labarai
0
Cikar Nijeriya Shekara 62 Da ‘Yancin Kai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Asabar 1 ga watan Oktoba ne Nijeriya ke bikin cika shekara 62 da samun ‘yancin kai daga turawan mulkin mallaka na Birtaniya.

Fafutukar kaiwa ga wannan matsayin ya samu gudumawa da sadaukarwa daga zakakuran ‘yan Nijeriya da dama da suka figto daga sassan kasar nan daban-daban, wadanda suka yi tsayin daka suka fuskanci Turawan Mulkiin mallaka na wancan lokaci, suka bukaci lallai sai Nijeriya ta samu ‘yancin gudanar da harkokinta da kanta ba tare dabkatsakandan daga ‘yan mulkiin mallaka ba.

  • Sin Ta Yi Kira A Daidaita Batun Ukraine Ta Hanyar Siyasa
  • Ummita: Mista Geng Ya Bukaci Kotu Ta Bashi Damar Daukar Lauya

Wadannan zakakurai da suka bayar da gudummawa akwai na bayyana, kana akwai wasu kuma da suka taka muhimmiyar rawa wadanda da dama sunayensu bai yi yawo kamar na sauran ba. Wannan ya sa domin murnar wannan rana mai dimbin tarihi, muka yi nazari a kan wasu zakakuran ‘yan Nijeriya bakwai da suka yi fice a wannan fafutukar ta ganin an samun ‘yancin tare da kawo muku dan takaitaccen taririnsu da irin rawar da suka taka.

Sir Ahmadu Bello, Sardaunan Sokoto (Yuni 12, 1910 – Janairu 15, 1966)

Nijeriya
Sir Ahmadu Bello, Sardaunan Sokoto

An dai haifi Sir Ahmadu Bello a garin Rabbah na Jihar Sakkwato da ke Arewacin Nijeriya. Sardauna na daya daga cikin jagororin Nijeriya da suka yi fice a duniya.
Ahmadu Bello ya rike sarautar Sardaunan Sakkwato kuma ya jagoranci jam’iyyar Northern People’s Congress, NPC, inda ya mamaye harkar siyasar kasar a jamhuriya ta daya. Sir Ahmadu Bello ya yi fafutuka wajen nema wa Nijeriya ‘yanci, inda bayan dawowarsa daga wani bulaguro da ya yi zuwa Birtaniya, aka nada shi a matsayin dan majalisa mai wakiltar lardin Sakkwato. A yau hoton Sardauna ne a kan kudin Nijeriya na Naira 200.
Wasu daga cikin abubuwan da ake tunawa da Sardauna sun hada da Jami’ar Ahmadu Bello Unibersity (ABU) da ke Zariya a Jihar Kaduna wadda aka sanya mata sunansa da kuma rawar da ya taka wajen ci gaban arewacin kasar.

Labarai Masu Nasaba

NLC Da TUC Sun Shirya Tsunduma Yajin Aiki Mai Dogon Zango Ranar Talata 3 Ga Oktoba 2023

Bikin Kafuwar Daular Saudiyya Shekara 93: Abubuwan Da Suka Kamata A Sani

Chief Anthony Enahoro (22 Yuli 1923 – 15 Disamba 2010)

Nijeriya
Chief Anthony Enahoro

Cif Anthony Eromosele Enahoro na daya daga cikin fitattun ‘yan gwawarmayar kin jinin mulkin mallaka kuma mai rajin kafa tsarin dimokradiyya.

Mista Enahoro ya zama Editan jaridar ‘Southern Nigerian Defender’ wadda Nnamdi Azikiwe kafa, inda ya zama editan jarida mafi karancin shekaru a Nijeriya. Enahoro ne mutum na farko da ya fara mika bukatar neman ‘yancin kan Nijeriya a shekara 1953. Hakan ne ya sa ake yi masa lakabi da “Uban Nijeriya”. Cif Enahoro masani ne kuma ya yi ta fafutuka kan Nijeriya har lokacin da ya mutu a 2010.

Herbert Macaulay (14 Nuwamba 1864 – 7 Mayu 1946)

Nijeriya
Herbert Macaulay

Asalin sunansa shi ne, Olayinka Herbert Samuel Heelas Badmus. Ya kasance dan kishin kasa, dan siyasa, Injiniya, mai ilimin tsara gine-gine kuma dan jarida ne kuma mawaki. ‘Yan Nijeriya da dama na bayyana shi da jagoran masu kishin kasa.
Mista Macaulay ya yi suna wajen hamayya da mulkin turawan mulkin mallaka. A shekarar 1919, ya tsaya wa masu sarauta a Landan wadanda aka kwace wa gonaki inda ya tilasta wa gwamnatin turawan mallaka da ta biya sarakunnan diyya.
Hakan ne ya fusata Majalisar Birtaniya ta ‘British Council’ inda har ta kai ga ta daure shi har sau biyu. Macaulay ya shahara inda a ranar 24 ga watan Yuni 1923 ya kafa jam’iyyar siyasa ta farko a Nijeriya ta ‘Nigerian National Democratic Party (NNDP)’. Herbert Macaulay ya mutu a shekarar 1946 to amma hotonsa ne a tsohuwar Naira 1.

Chif Obafemi Awolowo (6 Maris 1909 – 9 Mayu 1987)

Nijeriya
Chif Obafemi Awolowo

Chif Obafemi Jeremiah Oyeniyi Awolowo dan kishin kasa ne kuma dattijo wanda ya taka muhimmiyar rawa a gwagwarmayar neman ‘yancin kan Nijeriya. Shi ne firimiyan yankin kudu maso yammacin Nijeriya na farko sannan ya yi kwamishinan kudi a gwamnatin tarayya. Chif Obafemi ya zama mataimakin shugaban kasa na majalisar zartarwa a lokacin yakin basasa.
Awolowo ya jagoranci masu hamayya na jam’iyyar Action Group a majalisar dokokin tarayya. Duk da cewa bai ci takarar shugabancin Nijeriya a jamhuriya ta biyu ba, Cif Awolowo ya kasance dan takara na biyu mai yawan kuri’a bayan Alhaji Shehu Shagari. Hoton Obafemi ne a jikin Naira 100 na kudin Nijeriya.

Funmilayo Ransom Kuti (25 Oktoba 1900 – 13 Afrilu 1978)

Nijeriya
Funmilayo Ransom Kuti

Funmilayo Ransom Kuti ta kasance mace daya tilo a jerin sunayen ‘yan gwagwarmayar neman ‘yancin kan Nijeriya. Fumilayo ta kasance malamar makaranta, ‘yar siyasa, mai fafutukar kare ‘yancin mata sannan kuma mai rike da sarautar gargajiya. Ita ce mahaifiya ga shahararren mawakin nan na Nijeriya, Femi Kuti. Funmilayo ce mace ta farko da ta fara tuka mota a Nijeriya. An zabe ta a majalisar sarakunan gargajiya, inda ta kasance wata wakiliya ta al’ummar Yarabawa. Fafutukar da ta yi ta janyo wa ‘ya’yanta bakin jini musamman lokacin gwamnatocin soji.

Nnamdi Azikwe (16 Nuwamba 1904 -11 Mayu 1996)

Nijeriya
Nnamdi Azikwe

Chif Benjamin Nnamdi Azikiwe ne jagoran ‘yan gwagwarmayar masu kishin kasa na zamani. Nnamdi wanda ake yi wa lakabi da mai kishin kasa ya rike Editan jaridar African Morning Post. Shi ne mutum farko dan Nijeriya da sunansa ya shiga Majalisar Tuntuba ta Amurka. Bayan ayyana Nijeriya a matsayin Jamhuriya, Dakta Nnamdi Azikwe ya yi bakin kokarinsa wajen ganin ya hada kan kasar. Dakta Zik ya zamo shugaban Nijeriya na farko.

Tafawa Balewa (Disamba 1912 – 15 Janairu 1966)

Nijeriya
Abubakar Tafawa Balewa

Alhaji Sir Abubakar Tafawa Balewa ne fira ministan Nijeriya na farko na bayan da aasar ta samu ‘yancin kai a 1960. An zabi Sir Abubakar Balewa a matsayin dan majalisar dokokin lardin arewa a 1946, sannan ya je majalisar dokoki ta tarayya a 1947.
Tafawa Balewa ya zamo dan majalisa mai rajin kare arewacin Nijeriya. Alhaji Abubakar Tafawa Balewa tare da Sardaunan Sakkwato sun kafa jam’iyyar Northern People’s Congress (NPC).
Tabbas akwai ‘yan Nijeriya da dama da suka bayar da gudummawa daban-daban a wajen kokarin ganin Nijeriya ta samu ‘yanci kai daga Turawar Mulkin Mallaka, muna jinjina a garesu da addu’ar Allah ya gafarta musu, wadanda suke raye a halin yanzu muna addu’ar Allah ya kara musu lafiya.

Tags: 'Yancin KaiIngilaSardaunaShekara 62Tafawa Balewa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Inganta Hadin Gwiwa Da Sauran Kasashe A Bangaren Kimiyya Da Fasaha Da Kirkire-kirkire Da Kara Bude Kofa

Next Post

Cikar Nijeriya Shekara 62: Matsalar Tsaro Ta Inganta A Mulkin Buhari – Lai Mohammed

Related

Kungiyar Kwadago (NLC) Na Shirin Tsunduma Wani Sabon Yajin Aiki Mai Dogon Zango
Manyan Labarai

NLC Da TUC Sun Shirya Tsunduma Yajin Aiki Mai Dogon Zango Ranar Talata 3 Ga Oktoba 2023

7 hours ago
Saudiyya
Manyan Labarai

Bikin Kafuwar Daular Saudiyya Shekara 93: Abubuwan Da Suka Kamata A Sani

19 hours ago
Sulhu Da ‘Yan Bindiga: Gwamna Lawal Ya Mai Da Martani Ga Ministan Labarai
Manyan Labarai

Sulhu Da ‘Yan Bindiga: Gwamna Lawal Ya Mai Da Martani Ga Ministan Labarai

19 hours ago
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Wasu Mutane 15 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Zamfara

1 day ago
Sojoji Sun Ceto Wasu Karin Dalibai Mata 7 Na Jami’ar Tarayya Da Ke Gusau Jihar Zamfara
Da ɗumi-ɗuminsa

Sojoji Sun Ceto Wasu Karin Dalibai Mata 7 Na Jami’ar Tarayya Da Ke Gusau Jihar Zamfara

2 days ago
Bello Matawalle Ya Wawashe Kudi Da Motocin Gwamnati — Gwamnatin Zamfara
Manyan Labarai

Dauda Ya Kalubalanci Ganawar Sirri Da Gwamnatin Tarayya Ke Yi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara

2 days ago
Next Post
Cikar Nijeriya Shekara 62: Matsalar Tsaro Ta Inganta A Mulkin Buhari – Lai Mohammed

Cikar Nijeriya Shekara 62: Matsalar Tsaro Ta Inganta A Mulkin Buhari - Lai Mohammed

LABARAI MASU NASABA

Hatsaniya Ta Kaure Kan Zargin Cirewa Wata Gawa Ido Daya A Asibitin Kwararru Da Ke Gombe

Hatsaniya Ta Kaure Kan Zargin Cirewa Wata Gawa Ido Daya A Asibitin Kwararru Da Ke Gombe

September 26, 2023
NNPP Ta Yi Watsi Da Hukuncin Kotun Sauraren Karar Zaben Gwamnan Kano Da Ta Ba Gawuna Nasara

NNPP Ta Kai Korafinta Ga Hukumar NJC Kan Kalaman Daya Da Cikin Alkalan Kotun Zaben Kano

September 26, 2023
Duniya

Ra’ayin Gina Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ta Bai Daya Na Tattaro Karfin Sauya Duniya

September 26, 2023
‘Yansanda Sun Dakile Harin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Kan Wasu Rukunin Gidaje A Katsina

‘Yansandan Jihar Nasarawa Ta Tabbatar Da Sace Wasu Daliba A Jihar

September 26, 2023
JKS

Babban Jami’in JKS: Kasar Sin Za Ta Karfafa Hadin Gwiwa Da Amincewa Da Juna Da Kasar Masar

September 26, 2023
Kungiyar Kwadago (NLC) Na Shirin Tsunduma Wani Sabon Yajin Aiki Mai Dogon Zango

NLC Da TUC Sun Shirya Tsunduma Yajin Aiki Mai Dogon Zango Ranar Talata 3 Ga Oktoba 2023

September 26, 2023
Kasar Sin Mai Burin Ganin Ci Gaban Kowa

Kasar Sin Mai Burin Ganin Ci Gaban Kowa

September 26, 2023
Da Alamun SAKA Ba Zai Buga Wasa Biyu Ba Saboda Raunin Da Ya Samu Arteta

Da Alamun SAKA Ba Zai Buga Wasa Biyu Ba Saboda Raunin Da Ya Samu Arteta

September 26, 2023
Kimiyya

Masana Kimiyya Na Kasashen Kenya Da Sin Sun Kaddamar Da Kundin Farko Game Da Nau’ikan Tsirran Da Kenya Ta Wallafa

September 26, 2023
Libya

Me Ya Haifar Da Ambaliya A Libya?

September 26, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.