• English
  • Business News
Thursday, July 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cinikin Waje Na Kasar Sin Yana Inganta

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Cinikin Waje Na Kasar Sin Yana Inganta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ‘yan kwanakin da suka gabata ne, jirgin kasan dakon kaya na farko tsakanin Sin da Turai, ya isa birnin Shanghai dauke da kayayyakin da za a baje a bikin baje kolin kasa da kasa na kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin CIIE karo na shida. Shi dai wannan jirgi ya taso ne daga birnin Duisburg na kasar Jamus dauke da TEU 70 na kwantenoni, wadanda darajarsu ta kai sama da kudin Euro miliyan 16. 

Wannan na nufin cewa, bikin CIIE karo na shida da aka dade ana jira yana kara karatowa, wanda hakan zai kara sanya sabbin kuzari ga bunkasuwar cinikin waje na kasar Sin.

  • Tinubu Ya Karya Doka Kan Nada Olukoyede A Shugabancin Hukumar EFCC –Kwararru
  • Zaben Kano: Ba Mu Yarda A Karya ‘Yancin Dimokuradiyya Ba – Kungiya

Alkaluman hukuma da aka fitar jiya Jumma’a na nuna cewa, darajar kayayyakin shige da fice na kasar Sin a rubu’i uku na farkon shekara, ta kai kudin Sin RMB yuan tiriliyan 30.8, wanda saurin karuwarta ya kusan yi daidai da na makamancin lokaci na shekarar bara. Tun daga farkon wannan shekara, farfadowar tattalin arzikin duniya ke fuskantar koma baya, kuma ci gaban kasuwancin duniya ya fuskanci matsi da dama. A cikin wannan yanayi, cinikayyar waje ta kasar Sin “mai inganci” ba ta zo cikin sauki ba.

A halin yanzu, “sabbin abubuwa guda uku” da motoci masu amfani da wutar lantarki, da batirin lithium da kuma na’urorin tattara hasken rana ke wakilta, sun zama sabbin alamun cinikin waje na kasar Sin.

A rubu’i uku na farkon shekarar bana, darajar sabbin kayayyakin uku da kasar Sin ta fitar, ta kai yuan biliyan 798.99, wanda ya karu da kashi 41.7 bisa 100 kan na shekarar bara, kuma yawansu da ke cikin jimillar kayayyakin da kasar Sin take fitarwa zuwa ketare, ya karu da kashi 1.3 cikin 100 kan na shekarar bara, har ya kai kashi 4.5 bisa 100. Hakan ya kara sanya sabon kuzari a cinikin waje na kasar Sin.

Labarai Masu Nasaba

Alkaluman Tattalin Arzikin Sin A Rabin Farkon Bana Sun Zarce Hasashen Da Aka Yi

Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kafa Makomar Halittun Duniya Ta Bai Daya

Yayin da tattalin arzikin kasar Sin ke ci gaba da farfadowa da ma inganta, baya ga aiwatar da wasu tsare-tsare da matakai yadda ya kamata, ana saran shigowa da fitar da kayayyaki za su ci gaba da karfafa kyakkyawan yanayin da ake ciki, da ci gaba da sanya kwanciyar hankali a harkokin cinikayyar duniya. (Ibrahim)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaBunkasa Tattalin ArzikiKasar Sin
ShareTweetSendShare
Previous Post

CMG Ya Gudanar Da Taron Bita Yayin Cika Shekara Daya Da Watsa Shirin Leaders Talk

Next Post

Wang Yi: Sin Tana Goyon Bayan Zaman Lafiya Da Adalci Da Lamirin Da Ya Shafi Dan Adam Kan Batun Falasdinu

Related

Alkaluman Tattalin Arzikin Sin A Rabin Farkon Bana Sun Zarce Hasashen Da Aka Yi
Daga Birnin Sin

Alkaluman Tattalin Arzikin Sin A Rabin Farkon Bana Sun Zarce Hasashen Da Aka Yi

9 hours ago
Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kafa Makomar Halittun Duniya Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kafa Makomar Halittun Duniya Ta Bai Daya

17 hours ago
Zambia Na Maraba Da Tawaga Ta 26 Ta Jami’an Lafiya Ta Sin
Daga Birnin Sin

Zambia Na Maraba Da Tawaga Ta 26 Ta Jami’an Lafiya Ta Sin

18 hours ago
Jarin Kasar Sin Ya Bada Gudunmawa Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Zimbabwe
Daga Birnin Sin

Jarin Kasar Sin Ya Bada Gudunmawa Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Zimbabwe

19 hours ago
An Gudanar Da Taron Ministocin Wajen Kasashe Mambobin SCO A Tianjin
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Ministocin Wajen Kasashe Mambobin SCO A Tianjin

20 hours ago
Fasahar Amfani Da ’Yan Sandan Mutum-Mutumi Ta Kasar Sin Na Iya Taimaka Wa Tsaro A Afirka
Daga Birnin Sin

Fasahar Amfani Da ’Yan Sandan Mutum-Mutumi Ta Kasar Sin Na Iya Taimaka Wa Tsaro A Afirka

21 hours ago
Next Post
Wang Yi: Sin Tana Goyon Bayan Zaman Lafiya Da Adalci Da Lamirin Da Ya Shafi Dan Adam Kan Batun Falasdinu

Wang Yi: Sin Tana Goyon Bayan Zaman Lafiya Da Adalci Da Lamirin Da Ya Shafi Dan Adam Kan Batun Falasdinu

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato

Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato

July 17, 2025
Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa

Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa

July 17, 2025
Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

July 17, 2025
Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara

July 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet

July 17, 2025
Alkaluman Tattalin Arzikin Sin A Rabin Farkon Bana Sun Zarce Hasashen Da Aka Yi

Alkaluman Tattalin Arzikin Sin A Rabin Farkon Bana Sun Zarce Hasashen Da Aka Yi

July 17, 2025
Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila

Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila

July 17, 2025
Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu

Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu

July 17, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kafa Makomar Halittun Duniya Ta Bai Daya

Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kafa Makomar Halittun Duniya Ta Bai Daya

July 16, 2025
Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi

July 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.