• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cinikin Waje Na Kasar Sin Yana Inganta

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Cinikin Waje Na Kasar Sin Yana Inganta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ‘yan kwanakin da suka gabata ne, jirgin kasan dakon kaya na farko tsakanin Sin da Turai, ya isa birnin Shanghai dauke da kayayyakin da za a baje a bikin baje kolin kasa da kasa na kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin CIIE karo na shida. Shi dai wannan jirgi ya taso ne daga birnin Duisburg na kasar Jamus dauke da TEU 70 na kwantenoni, wadanda darajarsu ta kai sama da kudin Euro miliyan 16. 

Wannan na nufin cewa, bikin CIIE karo na shida da aka dade ana jira yana kara karatowa, wanda hakan zai kara sanya sabbin kuzari ga bunkasuwar cinikin waje na kasar Sin.

  • Tinubu Ya Karya Doka Kan Nada Olukoyede A Shugabancin Hukumar EFCC –Kwararru
  • Zaben Kano: Ba Mu Yarda A Karya ‘Yancin Dimokuradiyya Ba – Kungiya

Alkaluman hukuma da aka fitar jiya Jumma’a na nuna cewa, darajar kayayyakin shige da fice na kasar Sin a rubu’i uku na farkon shekara, ta kai kudin Sin RMB yuan tiriliyan 30.8, wanda saurin karuwarta ya kusan yi daidai da na makamancin lokaci na shekarar bara. Tun daga farkon wannan shekara, farfadowar tattalin arzikin duniya ke fuskantar koma baya, kuma ci gaban kasuwancin duniya ya fuskanci matsi da dama. A cikin wannan yanayi, cinikayyar waje ta kasar Sin “mai inganci” ba ta zo cikin sauki ba.

A halin yanzu, “sabbin abubuwa guda uku” da motoci masu amfani da wutar lantarki, da batirin lithium da kuma na’urorin tattara hasken rana ke wakilta, sun zama sabbin alamun cinikin waje na kasar Sin.

A rubu’i uku na farkon shekarar bana, darajar sabbin kayayyakin uku da kasar Sin ta fitar, ta kai yuan biliyan 798.99, wanda ya karu da kashi 41.7 bisa 100 kan na shekarar bara, kuma yawansu da ke cikin jimillar kayayyakin da kasar Sin take fitarwa zuwa ketare, ya karu da kashi 1.3 cikin 100 kan na shekarar bara, har ya kai kashi 4.5 bisa 100. Hakan ya kara sanya sabon kuzari a cinikin waje na kasar Sin.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Yayin da tattalin arzikin kasar Sin ke ci gaba da farfadowa da ma inganta, baya ga aiwatar da wasu tsare-tsare da matakai yadda ya kamata, ana saran shigowa da fitar da kayayyaki za su ci gaba da karfafa kyakkyawan yanayin da ake ciki, da ci gaba da sanya kwanciyar hankali a harkokin cinikayyar duniya. (Ibrahim)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaBunkasa Tattalin ArzikiKasar Sin
ShareTweetSendShare
Previous Post

CMG Ya Gudanar Da Taron Bita Yayin Cika Shekara Daya Da Watsa Shirin Leaders Talk

Next Post

Wang Yi: Sin Tana Goyon Bayan Zaman Lafiya Da Adalci Da Lamirin Da Ya Shafi Dan Adam Kan Batun Falasdinu

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

14 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

14 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

16 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

19 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

21 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

22 hours ago
Next Post
Wang Yi: Sin Tana Goyon Bayan Zaman Lafiya Da Adalci Da Lamirin Da Ya Shafi Dan Adam Kan Batun Falasdinu

Wang Yi: Sin Tana Goyon Bayan Zaman Lafiya Da Adalci Da Lamirin Da Ya Shafi Dan Adam Kan Batun Falasdinu

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.