ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Kano: Ba Mu Yarda A Karya ‘Yancin Dimokuradiyya Ba – Kungiya

by Sulaiman
3 years ago
Kano

Gamayyar Ƙungiyoyin Kare ‘Yancin Dimokuraɗiyya (CDR) a Jihar Bauchi, sun nuna rashin amincewa da kuma yin tsokaci kan yadda Kotun Shari’ar Zaɓen Gwamnan Kano ta yanke hukuncin da ya haifar da shakku da zargin yunƙurin danne haƙƙin zaɓen da ɗimbin jama’a su ka yi, bisa kyakkyawan tsarin dimokuraɗiyya.

CDR ta hasala ne dangane da hukuncin da kotun a Kano ta yanke, cewa, jam’iyyar mai mulki a ƙasa, APC ce da ɗan takarar a zaɓen gwamna a Kano su ka yi nasara, ba Gwamna Abba Kabir Yusuf na NNPP ba, wanda INEC ta tabbatar.

  • Kotun Zaben Gwamnan Taraba: Cikin Matsi INEC Ta Ayyana Sakamako, A Sake Bitar Zaben – NNPP
  • Mun Dauki Darasi A Zaben 2023 – Shugaban INEC

“Akwai matuƙar buƙatar mu tunatar wa majiɓinta wannan al’amari da dukkan masu ruwa da tsaki cewa, Kano ita ce cibiya kuma ginshiƙin tattalin arzikin Nijeriya. “Don haka ƙoƙarin bijirowa ko cimma hargitsi na siyasa yanzu a Kano, abu ne da ka iya dagula wa ko tarwatsa jihohin Arewa.”

ADVERTISEMENT

 

“A matsayin mu na gamayyar ƙungiyoyin yaɗa dimokuraɗiyya da kishinta da kuma kare martabarta, mun ga ya kamata mu fito don a ji muryoyinmu don ganin cewa ba mu sa-ido an yi wa al’umma ƙwacen abin da su ka zaɓa ba, lamarin da ka iya haifar wa Kano da Arewa baki ɗaya mummunan sakamakon za a yi da-na-sanin afkuwar sa daga baya.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

 

“Mu na ƙara nuni da cewa, mu fa ba mambobin NNPP ba ne, kuma ba ‘yan asalin Jihar Kano ba ne, amma dai akwai haƙƙi a kan mu da wajibcin fitowa mu yi gargaɗi ga dukkan masu hannu kan shirin wannan lamari”

A lokacin da ya ke jawabi yayin wani jerin-gwanon lumana ɗauke da kwalaye a ‘Tafawa Ɓalewa Tomb’, Daraktan Tsare-tsaren CDR mai suna Ibrahim Babayo, ya ce, “Kyakkyawan tsarin dimokraɗiyya shi ne ginshiƙin ɗorewar ƙasa. Kuma abu muhimmi shi ne a kare darajar kowace ƙuri’ar da jama’a suka kaɗa bisa adalci.”

 

Ya ce babban adalci ga kotun zaɓe shi ne ta yi ƙwaƙƙwaran binciken duk wani zargin aikata ba daidai ba a lokacin zaɓe.

Kano
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

MASU ALAKA

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano
Siyasa

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

April 25, 2026
Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

March 18, 2025
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

November 10, 2024
Next Post
Xi Ya Jaddada Bukatar Bunkasa Tattalin Arzikin Kogin Yangtze Mai Inganci

Xi Ya Jaddada Bukatar Bunkasa Tattalin Arzikin Kogin Yangtze Mai Inganci

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.