• English
  • Business News
Wednesday, June 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cire Tallafi: Gwamnan Gombe Ya Raba Kayayyakin Abinci Da Kayan Noma Ga Mutane 450,000

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Cire Tallafi: Gwamnan Gombe Ya Raba Kayayyakin Abinci Da Kayan Noma Ga Mutane 450,000
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya ya kaddamar da rabon kayan abinci da kayan noma don rage matsalolin tattalin arziki da ake fuskanta sakamakon cire tallafin man fetur ga al’ummar jihar. 

 

Da ya ke jawabi a waje bikin rabon kayayyakin wadda aka gudanar a fadar Sarkin Yamaltu da ke Dadinkowa jiya, Gwamnan ya bayyana cewa kaddamar da rabon kayan tallafin wani gagarumin kokari ne na tallafawa fiye da mutane 450,000 da za su ci gajiya a fadin kananan hukumomi 11 na jihar.

  • Lalacewar Hanyar Bauchi Zuwa Gombe Ta Zama Tarkon Mutuwa Ga Matafiya – Gwamna Inuwa

“A kashi na farko da muka kaddamar a yau, za mu tallafawa mutane dubu 30,000 ne inda kowane mutum zai samu buhun shinkafa mai girman Kilogram biyar da katon din macaroni daya da buhunan taki biyu da lita biyu na maganin kashe kwari”.

 

Labarai Masu Nasaba

PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta

Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

“Abin da ya sa wannan shiri ya sha bambam da sauran shirye-shirye shi ne dabarar sanya kayan noma a cikin rabon kayan abinci, wannan shawarar tana da matukar tasiri duba da yadda kaso mai tsoka na al’ummar Jihar Gombe sun dogara ne da noma don gudanar da harkokin rayuwarsu.”

Gombe

A cewarsa, ba da tallafin noman zai taimaka matuka wajen samar da isasshen abinci a lokacin kaka.

 

Da yake bayyana wajibcin cire tallafin man fetur, Gwamna Inuwa ya ce hakan wani mataki ne na tabbatar da dorewar tattalin arziki da ci gaba. Ya kara da cewa, an tsara tallafin ne bayan fahimtar irin kalubale daban-daban da magidanta ke fuskanta a Jihar Gombe sakamakon tabarbarewar tattalin arziki.

 

Baya ga rabon kayayyakin, Gwamna Inuwa ya ce, shirin tallafin yana kuma nuna tausayi da jajircewarsa ga jin dadin kowane dan Jihar Gombe.

 

Don haka ya bukaci al’ummar jihar su sanya dabi’un tausayi da hadin kai a cikin mu’amalarsu, tare da tallafawa mabukata.

 

Gwamnan ya yi kira ga jami’an rabon kayayyakin da ‘yan sa kai su gudanar da ayyukansu cikin gaskiya da rikon amana don tabbatar da gaskiya da adalci.

Gombe

Gwamna Inuwa Yahaya ya tabbatarwa jama’a cewa gwamnatin sa tana kokarin ƙara samar da ayyukan yi ga al’umma don bunkasar harkokin ci gaba, da dakile kalubalen tattalin arzikin da jama’a ke fuskanta.

 

Shugaban kwamitin kula da rabon kayan abinci na jiha Abdullahi Haruna Abdullahi, ya tabbatarwa Gwamnan cewa kwamitin zai gudanar da aikinsa cikin tsantseni da tsoron Allah don amfanar al’umma.

 

Abdullahi wanda kuma shi ne Sakataren zartarwa na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Gombe SEMA, ya bayyana cewa an kafa wasu kananan kwamitoci a matakin kananan hukumomi da gundumomi don tabbatar da cewa kayayyakin sun kai ga marasa galihu a jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Tana Nazarin Rahoton Kwamitin WTO Game Da Matakan Amurka

Next Post

Xi Jinping Zai Halarci Taron Ganawar Shugabannin Kasashen BRICS Karo Na 15

Related

Gwamnatin APC Ta Kara Ingiza ‘Yan NIjeriya Cikin Bakin Talauci – PDP
Manyan Labarai

PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta

1 hour ago
Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida
Labarai

Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

3 hours ago
KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano
Manyan Labarai

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

6 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

8 hours ago
Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano
Manyan Labarai

Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

9 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

17 hours ago
Next Post
Xi Jinping Zai Halarci Taron Ganawar Shugabannin Kasashen BRICS Karo Na 15

Xi Jinping Zai Halarci Taron Ganawar Shugabannin Kasashen BRICS Karo Na 15

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin APC Ta Kara Ingiza ‘Yan NIjeriya Cikin Bakin Talauci – PDP

PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta

June 25, 2025
Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

June 25, 2025
Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

June 25, 2025
KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

June 25, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

June 25, 2025
Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

June 25, 2025
Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

June 24, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

June 24, 2025
Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

June 24, 2025
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

June 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.