• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cire Tallafin Mai: Gwamnan Bauchi Ya Kaddamar Da Rabon Tallafin Rage Radadi

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Cire Tallafin Mai: Gwamnan Bauchi Ya Kaddamar Da Rabon Tallafin Rage Radadi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad ya kaddamar da rabon buhun shinkafa guda 88,889 mai nauyin kilo 25 da sauran nau’ikan tallafi daban-daban domin raba wa  masu kananan karfi da cire tallafin man fetur ya jefa cikin mawuyaciyar rayuwa a jihar.

An kaddamar da rabon ne a ranar Asabar a filin wasanni na Abubakar Tafawa Balewa da ke birnin jihar, Gwamna Bala ya gargadi dukkanin jami’an da aka bai wa alhakin rabon da su tabbatar da sun rike amana da yin rabon bisa yadda aka tsara domin tabbatar da kwalliya ta biya kudin sabulu.

  • An Yi Nasarar Ceto Mutum 30 Da Aka Sace Su A Jihar Bauchi

Sarkin Bauchi, Dakta Rilwanu Sulaiman Adamu, shi ne shugaban babban kwamitin rabon, yayin da mataimakin gwamnan jihar, Muhammad Auwal Jatau ya kasance shugaban kwamitin ayyuka da tsara rabon tallafin domin ganin ya shiga lunguna da sako na jihar.

Gwamnan ya kuma sanar da cewa, a karkashin rabon kudin tallafin da aka tsara, za a kashe Naira Miliyan 800 wajen biyan kudaden fansho na jiha da na kananan hukumomi inda kuma gwamnatin jihar za ta kara naira biliyan uku wajen biyan kudaden giratuti na jiha da na kananan hukumomin a kokarin gwamnatin na tausaya wa jama’a kan halin da aka shiga na matsi sakamakon cire tallafin mai din.

Bauchi

Labarai Masu Nasaba

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

Dukka a cikin tsarin tallafin, gwamna Bala Muhammad, ya sanar da cewa naira miliyan N680,000,000 za a kashe ta ne wajen biyan kudin hutu ga ma’aikata, wato (LTG), sai kuma aka ware naira miliyan N110 domin tallafa wa Mata da Matasa da nufin su tsayu da kafafunsu.

Kazalika, an ware Naira Miliyan N300,000,000 da za a rabar wa marasa karfi ta cikin shirin ‘conditional cash transfer’ (CCT), bugu da kari, za a dauki ma’aikatan sa-kai har su 1,000 a cibiyoyin kiwon lafiya da za a ke biyansu naira N10,000 kowace wata na tsawon watanni shida da hakan zai lakume Naira Miliyan N60,000,000.

Ya cigaba da cewa, “Mutane masu fama da nakasa ta musamman za su samu naira miliyan 10, ma’aikatan da ke shara don tsaftace muhallin cikin gari za su samu naira miliyan N37, jami’an tsaron sa kai na Zabgai za a basu naira miliyan N42, jami’an tsaron Spider kuma naira miliyan 21.”

Dangane da tsarin rabon shinkafar kuwa, gwamna Bala ya ce, kungiyoyin fararen hula, kungiyoyin addinai na musulmai da kirista, ‘yan banga, tsoffin sojoji, masu ruwa da tsaki, talakawa da marasa galihu ne za su ci gajiyar shirin.

Kazalika, ya bayyana cewar tun kafin wannan ranar a kokarinsa na ganin an samar da sauki ga al’umma tun bayan cire tallafin mai din, gwamnatinsa ta sayo motocin sufuri na zamani guda 30 kana ta zuba su cikin sha’anin sufuri a rahusa mai sauki domin taimaka wa jama’a.

Bauchi

Tun da farko a nasa jawabin, shugaban kwamitin tsare-tsaren rabon tallafin wanda shi ne mataimakin gwamnan jihar, Hon. Auwal Mohammed Jatau, ya fara ne da jinjina wa kokakin gwamna Bala Muhammad wajen tsayuwar daka domin nema wa al’ummarsa sauyin rayuwa.

Ya yi tilawar cewa gwamna Bala tun a farkon mulkinsa ya kaddamar da wani shirin samar da abubuwan dogaro da kai ga al’ummar jihar ta cikin (KEEP) da ya lakume sama da biliyan 3 wanda a cewarsa an ga natijar hakan domin da dama sun fita daga cikin matsalar talauci.

Babban shugaban kwamitin rabon tallafi, Sarkin Bauchi, Dakta Rilwanu Sulaiman Adamu, ya nuna farin cikinsa da ganin ranar da za a kaddamar da fara rabon, yana mai cewa tabbas hakan zai rage wa jama’a matsatsin da ake ciki a halin yanzu.

Bauchi

Sarkin ya yaba wa Gwamna Bala Muhammad bisa kokarinsa wajen samar da tallafi da agaji ga al’ummar jihar, ya nuna cewa zai sanya ido wajen ganin al’umma sun mari tallafin da aka ware dominsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BauchiKuncin rayuwaTallafin Man Fetur
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yin Li Ya Gana Da Shugabar Majalissar Dokokin Angola

Next Post

Tashar Sararin Samaniya Ta Sin Ta Nuna Zane-Zane Guda 10 Da Matasan Kasashen Afirka Suka Zana

Related

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

2 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

10 hours ago
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro
Tsaro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

12 hours ago
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu
Labarai

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

13 hours ago
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

14 hours ago
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

17 hours ago
Next Post
Tashar Sararin Samaniya Ta Sin Ta Nuna Zane-Zane Guda 10 Da Matasan Kasashen Afirka Suka Zana

Tashar Sararin Samaniya Ta Sin Ta Nuna Zane-Zane Guda 10 Da Matasan Kasashen Afirka Suka Zana

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.