• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cire Tallafin Mai: Gwamnan Bauchi Ya Kaddamar Da Rabon Tallafin Rage Radadi

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Bauchi

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad ya kaddamar da rabon buhun shinkafa guda 88,889 mai nauyin kilo 25 da sauran nau’ikan tallafi daban-daban domin raba wa  masu kananan karfi da cire tallafin man fetur ya jefa cikin mawuyaciyar rayuwa a jihar.

An kaddamar da rabon ne a ranar Asabar a filin wasanni na Abubakar Tafawa Balewa da ke birnin jihar, Gwamna Bala ya gargadi dukkanin jami’an da aka bai wa alhakin rabon da su tabbatar da sun rike amana da yin rabon bisa yadda aka tsara domin tabbatar da kwalliya ta biya kudin sabulu.

  • An Yi Nasarar Ceto Mutum 30 Da Aka Sace Su A Jihar Bauchi

Sarkin Bauchi, Dakta Rilwanu Sulaiman Adamu, shi ne shugaban babban kwamitin rabon, yayin da mataimakin gwamnan jihar, Muhammad Auwal Jatau ya kasance shugaban kwamitin ayyuka da tsara rabon tallafin domin ganin ya shiga lunguna da sako na jihar.

Gwamnan ya kuma sanar da cewa, a karkashin rabon kudin tallafin da aka tsara, za a kashe Naira Miliyan 800 wajen biyan kudaden fansho na jiha da na kananan hukumomi inda kuma gwamnatin jihar za ta kara naira biliyan uku wajen biyan kudaden giratuti na jiha da na kananan hukumomin a kokarin gwamnatin na tausaya wa jama’a kan halin da aka shiga na matsi sakamakon cire tallafin mai din.

Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Dukka a cikin tsarin tallafin, gwamna Bala Muhammad, ya sanar da cewa naira miliyan N680,000,000 za a kashe ta ne wajen biyan kudin hutu ga ma’aikata, wato (LTG), sai kuma aka ware naira miliyan N110 domin tallafa wa Mata da Matasa da nufin su tsayu da kafafunsu.

Kazalika, an ware Naira Miliyan N300,000,000 da za a rabar wa marasa karfi ta cikin shirin ‘conditional cash transfer’ (CCT), bugu da kari, za a dauki ma’aikatan sa-kai har su 1,000 a cibiyoyin kiwon lafiya da za a ke biyansu naira N10,000 kowace wata na tsawon watanni shida da hakan zai lakume Naira Miliyan N60,000,000.

Ya cigaba da cewa, “Mutane masu fama da nakasa ta musamman za su samu naira miliyan 10, ma’aikatan da ke shara don tsaftace muhallin cikin gari za su samu naira miliyan N37, jami’an tsaron sa kai na Zabgai za a basu naira miliyan N42, jami’an tsaron Spider kuma naira miliyan 21.”

Dangane da tsarin rabon shinkafar kuwa, gwamna Bala ya ce, kungiyoyin fararen hula, kungiyoyin addinai na musulmai da kirista, ‘yan banga, tsoffin sojoji, masu ruwa da tsaki, talakawa da marasa galihu ne za su ci gajiyar shirin.

Kazalika, ya bayyana cewar tun kafin wannan ranar a kokarinsa na ganin an samar da sauki ga al’umma tun bayan cire tallafin mai din, gwamnatinsa ta sayo motocin sufuri na zamani guda 30 kana ta zuba su cikin sha’anin sufuri a rahusa mai sauki domin taimaka wa jama’a.

Bauchi

Tun da farko a nasa jawabin, shugaban kwamitin tsare-tsaren rabon tallafin wanda shi ne mataimakin gwamnan jihar, Hon. Auwal Mohammed Jatau, ya fara ne da jinjina wa kokakin gwamna Bala Muhammad wajen tsayuwar daka domin nema wa al’ummarsa sauyin rayuwa.

Ya yi tilawar cewa gwamna Bala tun a farkon mulkinsa ya kaddamar da wani shirin samar da abubuwan dogaro da kai ga al’ummar jihar ta cikin (KEEP) da ya lakume sama da biliyan 3 wanda a cewarsa an ga natijar hakan domin da dama sun fita daga cikin matsalar talauci.

Babban shugaban kwamitin rabon tallafi, Sarkin Bauchi, Dakta Rilwanu Sulaiman Adamu, ya nuna farin cikinsa da ganin ranar da za a kaddamar da fara rabon, yana mai cewa tabbas hakan zai rage wa jama’a matsatsin da ake ciki a halin yanzu.

Bauchi

Sarkin ya yaba wa Gwamna Bala Muhammad bisa kokarinsa wajen samar da tallafi da agaji ga al’ummar jihar, ya nuna cewa zai sanya ido wajen ganin al’umma sun mari tallafin da aka ware dominsu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza
Labarai

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga
Labarai

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025
Next Post
Tashar Sararin Samaniya Ta Sin Ta Nuna Zane-Zane Guda 10 Da Matasan Kasashen Afirka Suka Zana

Tashar Sararin Samaniya Ta Sin Ta Nuna Zane-Zane Guda 10 Da Matasan Kasashen Afirka Suka Zana

LABARAI MASU NASABA

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

November 8, 2025
Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

November 8, 2025
Kamfanoni Masu Jarin Waje Na Samun Kwarin Gwiwa Daga CIIE

Kamfanoni Masu Jarin Waje Na Samun Kwarin Gwiwa Daga CIIE

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.