ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cire Tallafin Mai: Gwamnan Bauchi Ya Kaddamar Da Rabon Tallafin Rage Radadi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Bauchi

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad ya kaddamar da rabon buhun shinkafa guda 88,889 mai nauyin kilo 25 da sauran nau’ikan tallafi daban-daban domin raba wa  masu kananan karfi da cire tallafin man fetur ya jefa cikin mawuyaciyar rayuwa a jihar.

An kaddamar da rabon ne a ranar Asabar a filin wasanni na Abubakar Tafawa Balewa da ke birnin jihar, Gwamna Bala ya gargadi dukkanin jami’an da aka bai wa alhakin rabon da su tabbatar da sun rike amana da yin rabon bisa yadda aka tsara domin tabbatar da kwalliya ta biya kudin sabulu.

  • An Yi Nasarar Ceto Mutum 30 Da Aka Sace Su A Jihar Bauchi

Sarkin Bauchi, Dakta Rilwanu Sulaiman Adamu, shi ne shugaban babban kwamitin rabon, yayin da mataimakin gwamnan jihar, Muhammad Auwal Jatau ya kasance shugaban kwamitin ayyuka da tsara rabon tallafin domin ganin ya shiga lunguna da sako na jihar.

ADVERTISEMENT

Gwamnan ya kuma sanar da cewa, a karkashin rabon kudin tallafin da aka tsara, za a kashe Naira Miliyan 800 wajen biyan kudaden fansho na jiha da na kananan hukumomi inda kuma gwamnatin jihar za ta kara naira biliyan uku wajen biyan kudaden giratuti na jiha da na kananan hukumomin a kokarin gwamnatin na tausaya wa jama’a kan halin da aka shiga na matsi sakamakon cire tallafin mai din.

Bauchi

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Dukka a cikin tsarin tallafin, gwamna Bala Muhammad, ya sanar da cewa naira miliyan N680,000,000 za a kashe ta ne wajen biyan kudin hutu ga ma’aikata, wato (LTG), sai kuma aka ware naira miliyan N110 domin tallafa wa Mata da Matasa da nufin su tsayu da kafafunsu.

Kazalika, an ware Naira Miliyan N300,000,000 da za a rabar wa marasa karfi ta cikin shirin ‘conditional cash transfer’ (CCT), bugu da kari, za a dauki ma’aikatan sa-kai har su 1,000 a cibiyoyin kiwon lafiya da za a ke biyansu naira N10,000 kowace wata na tsawon watanni shida da hakan zai lakume Naira Miliyan N60,000,000.

Ya cigaba da cewa, “Mutane masu fama da nakasa ta musamman za su samu naira miliyan 10, ma’aikatan da ke shara don tsaftace muhallin cikin gari za su samu naira miliyan N37, jami’an tsaron sa kai na Zabgai za a basu naira miliyan N42, jami’an tsaron Spider kuma naira miliyan 21.”

Dangane da tsarin rabon shinkafar kuwa, gwamna Bala ya ce, kungiyoyin fararen hula, kungiyoyin addinai na musulmai da kirista, ‘yan banga, tsoffin sojoji, masu ruwa da tsaki, talakawa da marasa galihu ne za su ci gajiyar shirin.

Kazalika, ya bayyana cewar tun kafin wannan ranar a kokarinsa na ganin an samar da sauki ga al’umma tun bayan cire tallafin mai din, gwamnatinsa ta sayo motocin sufuri na zamani guda 30 kana ta zuba su cikin sha’anin sufuri a rahusa mai sauki domin taimaka wa jama’a.

Bauchi

Tun da farko a nasa jawabin, shugaban kwamitin tsare-tsaren rabon tallafin wanda shi ne mataimakin gwamnan jihar, Hon. Auwal Mohammed Jatau, ya fara ne da jinjina wa kokakin gwamna Bala Muhammad wajen tsayuwar daka domin nema wa al’ummarsa sauyin rayuwa.

Ya yi tilawar cewa gwamna Bala tun a farkon mulkinsa ya kaddamar da wani shirin samar da abubuwan dogaro da kai ga al’ummar jihar ta cikin (KEEP) da ya lakume sama da biliyan 3 wanda a cewarsa an ga natijar hakan domin da dama sun fita daga cikin matsalar talauci.

Babban shugaban kwamitin rabon tallafi, Sarkin Bauchi, Dakta Rilwanu Sulaiman Adamu, ya nuna farin cikinsa da ganin ranar da za a kaddamar da fara rabon, yana mai cewa tabbas hakan zai rage wa jama’a matsatsin da ake ciki a halin yanzu.

Bauchi

Sarkin ya yaba wa Gwamna Bala Muhammad bisa kokarinsa wajen samar da tallafi da agaji ga al’ummar jihar, ya nuna cewa zai sanya ido wajen ganin al’umma sun mari tallafin da aka ware dominsu.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Tashar Sararin Samaniya Ta Sin Ta Nuna Zane-Zane Guda 10 Da Matasan Kasashen Afirka Suka Zana

Tashar Sararin Samaniya Ta Sin Ta Nuna Zane-Zane Guda 10 Da Matasan Kasashen Afirka Suka Zana

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.