ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cire Tallafin Mai: Gwamnan Bauchi Ya Kaddamar Da Rabon Tallafin Rage Radadi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Bauchi

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad ya kaddamar da rabon buhun shinkafa guda 88,889 mai nauyin kilo 25 da sauran nau’ikan tallafi daban-daban domin raba wa  masu kananan karfi da cire tallafin man fetur ya jefa cikin mawuyaciyar rayuwa a jihar.

An kaddamar da rabon ne a ranar Asabar a filin wasanni na Abubakar Tafawa Balewa da ke birnin jihar, Gwamna Bala ya gargadi dukkanin jami’an da aka bai wa alhakin rabon da su tabbatar da sun rike amana da yin rabon bisa yadda aka tsara domin tabbatar da kwalliya ta biya kudin sabulu.

  • An Yi Nasarar Ceto Mutum 30 Da Aka Sace Su A Jihar Bauchi

Sarkin Bauchi, Dakta Rilwanu Sulaiman Adamu, shi ne shugaban babban kwamitin rabon, yayin da mataimakin gwamnan jihar, Muhammad Auwal Jatau ya kasance shugaban kwamitin ayyuka da tsara rabon tallafin domin ganin ya shiga lunguna da sako na jihar.

ADVERTISEMENT

Gwamnan ya kuma sanar da cewa, a karkashin rabon kudin tallafin da aka tsara, za a kashe Naira Miliyan 800 wajen biyan kudaden fansho na jiha da na kananan hukumomi inda kuma gwamnatin jihar za ta kara naira biliyan uku wajen biyan kudaden giratuti na jiha da na kananan hukumomin a kokarin gwamnatin na tausaya wa jama’a kan halin da aka shiga na matsi sakamakon cire tallafin mai din.

Bauchi

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

Dukka a cikin tsarin tallafin, gwamna Bala Muhammad, ya sanar da cewa naira miliyan N680,000,000 za a kashe ta ne wajen biyan kudin hutu ga ma’aikata, wato (LTG), sai kuma aka ware naira miliyan N110 domin tallafa wa Mata da Matasa da nufin su tsayu da kafafunsu.

Kazalika, an ware Naira Miliyan N300,000,000 da za a rabar wa marasa karfi ta cikin shirin ‘conditional cash transfer’ (CCT), bugu da kari, za a dauki ma’aikatan sa-kai har su 1,000 a cibiyoyin kiwon lafiya da za a ke biyansu naira N10,000 kowace wata na tsawon watanni shida da hakan zai lakume Naira Miliyan N60,000,000.

Ya cigaba da cewa, “Mutane masu fama da nakasa ta musamman za su samu naira miliyan 10, ma’aikatan da ke shara don tsaftace muhallin cikin gari za su samu naira miliyan N37, jami’an tsaron sa kai na Zabgai za a basu naira miliyan N42, jami’an tsaron Spider kuma naira miliyan 21.”

Dangane da tsarin rabon shinkafar kuwa, gwamna Bala ya ce, kungiyoyin fararen hula, kungiyoyin addinai na musulmai da kirista, ‘yan banga, tsoffin sojoji, masu ruwa da tsaki, talakawa da marasa galihu ne za su ci gajiyar shirin.

Kazalika, ya bayyana cewar tun kafin wannan ranar a kokarinsa na ganin an samar da sauki ga al’umma tun bayan cire tallafin mai din, gwamnatinsa ta sayo motocin sufuri na zamani guda 30 kana ta zuba su cikin sha’anin sufuri a rahusa mai sauki domin taimaka wa jama’a.

Bauchi

Tun da farko a nasa jawabin, shugaban kwamitin tsare-tsaren rabon tallafin wanda shi ne mataimakin gwamnan jihar, Hon. Auwal Mohammed Jatau, ya fara ne da jinjina wa kokakin gwamna Bala Muhammad wajen tsayuwar daka domin nema wa al’ummarsa sauyin rayuwa.

Ya yi tilawar cewa gwamna Bala tun a farkon mulkinsa ya kaddamar da wani shirin samar da abubuwan dogaro da kai ga al’ummar jihar ta cikin (KEEP) da ya lakume sama da biliyan 3 wanda a cewarsa an ga natijar hakan domin da dama sun fita daga cikin matsalar talauci.

Babban shugaban kwamitin rabon tallafi, Sarkin Bauchi, Dakta Rilwanu Sulaiman Adamu, ya nuna farin cikinsa da ganin ranar da za a kaddamar da fara rabon, yana mai cewa tabbas hakan zai rage wa jama’a matsatsin da ake ciki a halin yanzu.

Bauchi

Sarkin ya yaba wa Gwamna Bala Muhammad bisa kokarinsa wajen samar da tallafi da agaji ga al’ummar jihar, ya nuna cewa zai sanya ido wajen ganin al’umma sun mari tallafin da aka ware dominsu.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Next Post
Tashar Sararin Samaniya Ta Sin Ta Nuna Zane-Zane Guda 10 Da Matasan Kasashen Afirka Suka Zana

Tashar Sararin Samaniya Ta Sin Ta Nuna Zane-Zane Guda 10 Da Matasan Kasashen Afirka Suka Zana

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.