• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cire Tallafin Mai: NIS Ta Samar Da Motoci Kyauta Don Sufurin Ma’aikatanta

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Cire Tallafin Mai: NIS Ta Samar Da Motoci Kyauta Don Sufurin Ma’aikatanta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mukaddashiyar Kwanturola Janar ta Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS), Caroline Wura-Ola Adepoju, ta samar wa ma’aikatan hukumar motocin sufuri don rage musu radadin karin kudin sufuri da aka samu.

Wannan na zuwa ne bayan karin farashin sufuri da aka yi a baya-bayan nan sakamakon cire tallafin man fetur.

  • Ministar Ghana Ta Yi Murabus Bayan Sace Makudaden Kudade A Gidanta
  • ‘Yansanda Sun Cafke ‘Yan Boko Haram Kan Zargin Shirin Kai Hari Gidan Atiku

Wannan na dauke ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun kakakin hukumar, Kenneth Kure da ya fitar a ranar Litinin.

Ta dauki wani ne mataki don saukaka wa ma’aikatan NIS ta hanyar gabatar da jerin motocin bas don bukatunsu na sufuri.

Wannan wani bangare ne na tsare-tsarenta don walwala da kuma nufin inganta rayuwar ma’aikatan hukumar.

Labarai Masu Nasaba

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

A wani takaitaccen biki da aka gudanar a hedikwatar NIS da ke Abuja, a ranar Litinin 24 ga watan Yuli, 2023, mukaddashiyar ta mika motocin bas din a hukumance ga jami’an hukumar.

A yayin jawabinta, ta jaddada muhimmancin tallafawa da inganta walwalar ma’aikata, inda ta nuna muhimmancin aikinsu da kuma sadaukarwar da suke yi wa wannan kasa.

“Ana sa ran samar da wadannan motocin bas din zai gyara kalubalen kudi da aka samu sakamakon karin kudin sufuri da aka samu a baya-bayan nan da kuma tabbatar da samar da sauki ga ma’aikatanmu,” in ji ta.

Mukaddashiyar ta bayyana cewa an riga an sayo karin motocin bas da za su ke bi manyan hanyoyin Abuja don jigilar ma’aikatan hukumar.

Ta kuma bayyana kudurinta na fadada wannan tsari ga sauran hukumomin jihohin kasar nan.

Caroline Wura-Ola Adepoju, ta shawarci direbobin motocin da su nuna kwazo wajen gudanar da ayyukansu.

Ta kuma jaddada muhimmancin bin ka’idojin tuki na tafiya a kan kilomita 60 duk cikin sa’a guda, tare da tabbatar da tsaron ma’aikatan yayin jigilarsu.

Har wa yau, ta yi kira ga daukacin jami’an hukumar da su dauki nauyin kula da bas din da aka tanadar domim su yadda ya kamata.

Ta kara da cewa “Wannan kokarin hadin gwiwa zai tabbatar da dadewar motocin tare da bai wa NIS damar dorewar wannan shiri mai.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BasCire Tallafin MaiJami'aiMotocin SufuriNIS
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Cafke ‘Yan Boko Haram Kan Zargin Shirin Kai Hari Gidan Atiku

Next Post

An Gurfanar Da Emefiele A Kotu Kan Mallakar Makamai Ba Bisa Ka’ida Ba

Related

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

4 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

9 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

10 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da ÆŠansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

11 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da ÆŠansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

12 hours ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

13 hours ago
Next Post
An Gurfanar Da Emefiele A Kotu Kan Mallakar Makamai Ba Bisa Ka’ida Ba

An Gurfanar Da Emefiele A Kotu Kan Mallakar Makamai Ba Bisa Ka'ida Ba

LABARAI MASU NASABA

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.