Cristiano Ronaldo na shirin tsawaita zamansa a Al Nassr yayin da yake dab da kulla sabuwar yarjejeniya da kulob din dake buga gasar Saudi Pro League.
Babban dan Jarida da ke sharhi akan wasanni, Fabrizio Romano ne ya bayyana haka a shafinsa na X inda ya rubuta: “Cristiano Ronaldo na shirin sanya hannu kan sabuwar yarjejeniya da Al Nassr.
- Liverpool Za Ta Kece Raini Da Bournemouth, Arsena Za Ta Bakunci Man Utd A Wasan Mako Na Firimiya Ta Baɗi
- Messi, Ronaldo, Lookman Na Cikin ‘Yan Wasan Da Ke Takarar Kyautar Globe Soccer Awards Ta Bana
Akwai yiwuwar Ronaldo ya saka hannu akan yarjejeniyar shekara daya ko biyu, wanda hakan zai sa ya tsaya a Saudiyya har zuwa watan Yuni na shekarar 2027, duk da rade-radin da ake yi na cewa yana shirin zuwa daya daga cikin kungiyoyin dake buga gasar kofin Duniya da ake bugawa yanzu haka, Ronaldo ya tabbatar a farkon wannan watan cewa ba zai shiga gasar ba.
Dan wasan mai shekaru 40 ya zura kwallaye 93 sannan ya taimaka wajen zura 19 a wasanni 105 da ya buga a dukkanin wasannin da ya buga a kungiyar ta Saudiyya, amma har yanzu bai samu nasarar lashe kofi a gasar ba, a kakar wasan da aka kammala kwanan nan, Al Nassr ta kare a matsayi na uku a teburin, inda ta rasa gurbi a gasar cin kofin zakarun yankin Asia na shekara mai zuwa kuma a maimakon haka za ta buga gasar AFC Champions League 2.
Bugu da kari, Al Nassr a halin yanzu ba ta da koci tun bayan da ta raba gari da babban kocinta Stefano Pioli a ranar Laraba, wanda ya zama koci na uku da ya bar kungiyar tun bayan zuwan Ronaldo daga Manchester United.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp