Hukumar kwallon kafa ta Duniya (FIFA) ta bayyana cewa kasar da ta yi nasara a Gasar Cin Kofin Duniya na shekarar 2026 za su samu tukwuicin dala miliyan 50, wanda yake wani bangare na kudin da aka ware a gasar na dala miliyan 655, wannan ya nuna karuwar kusan kashi 50 cikin 100 idan aka kwatanta da dala miliyan 440 da aka raba wa kasashe a Gasar Cin Kofin Duniya ta shekarar 2022 a Qatar.
Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026, wadda za a yi daga 11 ga watan Yuni zuwa 19 ga Yuli na shekarar 2026, a kasashen Amurka, Mexico, da Kanada, za ta kasance ta farko da za ta kunshi kasashe 48, idan aka kwatanta da 32 da suka buga gasar a baya, a gasar da ta gabata, Hukumar Kwallon Kafa ta Argentina ta sami dala miliyan 42 bayan Lionel Messi ya jagorance su zuwa ga nasara a kan Faransa a bugun fenariti, yayinda Faransa, wacce ta zo ta biyu, ta sami dala miliyan 30.
A shekarar 2026, wadanda suka yi rashin nasara a wasan karshe za su samu dala miliyan 33, wadanda suka zo na uku kuma za su samu dala miliyan 29, sauran wadanda suka zo matakin na kusa da na karshe za su sami dala miliyan 27, kasashen da aka fitar a matakin rukuni za su sami dala miliyan 9, yayin da dukkan kasashe 48 da suka shiga gasar za su sami kyautar dala miliyan 1 da rabi a matsayin kudin shirye shirye.
Sanarwar ta nuna yunkurin hukumar FIFA na sanya gasar cin kofin duniya ta gaba ta zama gasa mafi girma kuma mafi lada a tarihi, wanda hakan zai kara janyowa gasar daukaka a idon Duniya, sannan ta cigaba da zama wasan da yafi kowane daraja a Duniya.














