• English
  • Business News
Saturday, May 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cutar Da Ke Yi Wa Tumatir Illa Ta Sake Addabar Gonakan Tumatir A Jihar Kano

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Cutar Da Ke Yi Wa Tumatir Illa Ta  Sake Addabar Gonakan Tumatir A Jihar Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar manoman Tumatir reshen jihar kano TOGAN ta bayyana cewa, cutar da ke yiwa Tumatir Illa ta sake afkawa a wasu gonakan manona da ke a cikin jihar.

Shugaban kungiyar reshen jihar Alhaji Sani Danladi Yadakwari ne ya bayyana hakan a hirarsa da manema labarai inda ya ce, sun zargin cutar ta Tuta ce da ke lalata Tumatir.

  • Dubi Ga Shirin Nijeriya Na Yaki Da Talauci A Duniya

A cewar shugaban, kungiyar ta dauki kwararan matakai domin mu kare yaduwar cutar zuwa sauran gonakan manoman na Tumatir da ke a daukacin fadin jihar.
Shugaban ya ci gaba da cewa, idan ba yi hankali ba, a kakar noman sa ta bana za a iya samun karancin sa.

” Mun dauki kwararan matakai domin mu kare yaduwar cutar zuwa sauran gonakan manoman na Tumatir da ke a daukacin fadin jihar.”

Yadakwari ya bayyana cewa, mun lura da bullar wannan cutar ta tuta a wasu kananan hukumin Jihar kamar a Garun Mallam da Bunkure da kuma a wasu gurare da ke a cikin jihar.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi

Shugaban ya bayyana cewa, a kungiyance mun yi iya namu kokarin, inda muka rubuta wasiku domin sanar da ma’aikatar aikin noma ta jihar.

Ya sanar da cewa, wannan cutar ba karamar koma baya za ta janyo wa manoman na Tumatir da ke a cikin jihar ba.

Shugaban ya bayyana cewa, ya zama wajibi gwamnatin jihar ta kawo mana daukin gaggawa domin gudun kar manoman na Tumatir da ke a cikin jihar su tabka asara da kuma magance karancin sa a daukacin fadin jihar.

” Ya zama wajibi gwamnatin jihar ta kawo mana daukin gaggawa domin gudun kar manoman na Tumatir da ke a cikin jihar su tabka asara da kuma magance karancin sa a daukacin fadin jihar. ”

Bisa wani bincike da aka gudanar ya nuna cewa, cutar na tafiya ne sai kuma ta sake dawo wa, tum bayan lokacin da ta bulla a shekarar 2016.

” Ya zama wajibi gwamnatin jihar ta kawo mana daukin gaggawa domin gudun kar manoman na Tumatir da ke a cikin jihar su tabka asara da kuma magance karancin sa a daukacin fadin jihar. ”

Da aka tuntubi daraktan ma’aikatar aikin noma da raya karkara na tarayya da ke a cikin jihar Alhaji Baba Gana akan maganar ya bayyana cewa, kungiyar ta tuntubi ma’aikatar kan maganar kuma da zarar sun samu cikakkun bayanai za su dauki matakan da suka kamata akan matsalar, musamman domin a dakile yaduwar cutar zuwa sauran gonakan manoman na noma Tumatir da ke a cikin jihar.

“ Kungiyar ta tuntubi ma’aikatar kan maganar kuma da zarar sun samu cikakkun bayanai za su dauki matakan da suka kamata akan matsalar, musamman domin a dakile yaduwar cutar zuwa sauran gonakan manoman na noma Tumatir da ke a cikin jihar. ”

A wata sabuwa kuwa, wasu daga cikin masana a fannin noman masara a kasar nan, sun sanar da cewa, kokarin manoman ta a kasar nan bai kai ga yanda za’a iya yayatawa ba ba, domin kuwa a ganin su da ace ana aiwatar da abubuwan da ake fada a baki to da yanzu kasar ta tara da takwarorinta da suka yi mata nisa wajen noman rani irin su Masar.

A cewar masanan, Nijeriya za ta iya shiga gaban Masar wajen noman tumatir, saboda idan ka duba , kashi saba’in cikin dari na kasar Masar Sahara ce, inda kuma Nijeriya Allah ya albarkace ta da kasar noma mai inganci, amma bama bin hanyoyin da suka dace.

Masana dai na da ra’ayin cewa da hukumomi a Nijeriya har yanzu ba su fargaba ganin yadda suke yiwa fannin na noma rikon Sakanaira Kashi.

Duk da cewa kasar na daga manyan masu noman tumatur a duniya, har yanzu kasar na shigo da Tumatur daga kasashen waje domin amfanin ‘yan kasar.

Alhaji Abdulrahim Ali wani manomi a karamar hukumar kura a jihar Kano ya sanar da cewa, suna noman tumatir, amma idan masu siya basu zoba, dole ne mu dauka su kai kasuwa mu siyar da araha domin kada ya lallace.

Shi kuwa Malam Dan Lami Umar sakatare na Kungiyar masu sai da kayan gwari ta jihar Kano ya sanar da cewa, wannan shine lokacin da ake asara, saboda ko ta ina akwai kayan miya.

Ya kara da cewa, wani manomin idan kaje gonarsa za ka samu kwando guda dubu biyu zuwa dari biyar ko kuma dari, inda ya kara da cewa, ko kuma idan an kawowa kasuwa, da gwamnatin tana talafawa ba zaa dinga samun irin wannan yanayi ba.

Kwamishinan noma na jihar Kano Alhaji Musa Sulaiman Shanono ya ce gwamnatin ta na iyakacin kokarinta domin magance wanan matsala.

Alhaji Musa ya kara da cewa, gwamnati ta na sane kuma ta damu kwarai, gwamnatin kano ta kulla yarjejeniya domin samarda kamfanin da zai dinga sarrafa tumatir domin taimakawa manoma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bukatar Tinubu Ya Kafa Kakkarfar Gwamnati

Next Post

Kano, Borno Da Benuwe Ne A Baya Wajen Bayyana Yadda Suke Kashe Kudadensu – Rahoto

Related

Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

12 hours ago
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi

13 hours ago
Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

1 week ago
Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

2 weeks ago
Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

2 weeks ago
Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet
Noma Da Kiwo

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

2 weeks ago
Next Post
Kano, Borno Da Benuwe  Ne A Baya Wajen  Bayyana Yadda Suke Kashe Kudadensu – Rahoto

Kano, Borno Da Benuwe Ne A Baya Wajen Bayyana Yadda Suke Kashe Kudadensu - Rahoto

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 

Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 

May 24, 2025
Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF

Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF

May 24, 2025
CHINADA Ta Nuna Matukar Adawa Da Gasar Wasannin Da Aka Amince Da Kwayoyin Kara Kuzari

CHINADA Ta Nuna Matukar Adawa Da Gasar Wasannin Da Aka Amince Da Kwayoyin Kara Kuzari

May 24, 2025

Tsokaci Kan Yadda Wasu Matasa Ke Yin Aure Ba Tare Da Sana’a Ba

May 24, 2025
Sin Ta Jaddada Da Muhimmancin Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza

Sin Ta Jaddada Da Muhimmancin Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza

May 24, 2025
An Kaddamar Da Bikin Baje Kolin Aikin Gona Na Kasa Da Kasa Na Cote d’Ivoire

An Kaddamar Da Bikin Baje Kolin Aikin Gona Na Kasa Da Kasa Na Cote d’Ivoire

May 24, 2025
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

May 24, 2025
Hunan Ya Ruwaito Samuwar Karin 6.3% Na Kayayyakin Da Ake Fitarwa Zuwa Afirka Tsakanin Janairu Da Afrilu

Hunan Ya Ruwaito Samuwar Karin 6.3% Na Kayayyakin Da Ake Fitarwa Zuwa Afirka Tsakanin Janairu Da Afrilu

May 24, 2025
Mohamed Salah Ya Zama Gwarzon ÆŠan Wasan Firimiyar Ingila Na Bana

Mohamed Salah Ya Zama Gwarzon ÆŠan Wasan Firimiyar Ingila Na Bana

May 24, 2025
Tsokaci Kan Yadda Wasu Matasa Ke Yin Aure Ba Tare Da Sana’a Ba

Tsokaci Kan Yadda Wasu Matasa Ke Yin Aure Ba Tare Da Sana’a Ba

May 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.