• English
  • Business News
Friday, October 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Ɗumi-ɗumi: Kotu Ta Gargaɗi  Bayero Kan Bayyana Kansa A Matsayin Sarkin Kano

by Sulaiman
1 year ago
masarautar kano

Wata babbar kotun jihar Kano karkashin jagorancin mai shari’a Amina Adamu Aliyu ta dakatar da Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero da wasu sarakuna hudu da aka tsige a jihar daga bayyana kansu a matsayin sarakuna.

Hukuncin dai ya haramtawa Bayero tare da Sarakunan Bichi, Rano, Gaya, da Karaye, daga yin ikirari ko zartar da wani hukunci a matsayin sarakuna.

  • Har Yanzu Tukunyar Rikicin Masarautar Kano Na Tafarfasa
  • Kanana Hukumomin Kano Da Jigawa 23 Na Kan Gaba Wajen Fuskantar Ambaliyar Ruwa – NEMA

LEADERSHIP ta ruwaito cewa, a ranar 27 ga watan Mayun 2024 ne gwamnatin jihar Kano, ta bakin lauyanta, Ibrahim Isah-Wangida, ta nemi a dakatar da Bayero da sauran sarakunan hudu da aka tsige daga ikirari ko bayyana kansu a matsayin Sarakuna a Jihar.

Wadanda ake karar acikin shari’ar sun hada da Alhaji Aminu Ado Bayero (Sarkin Kano na 15), da Alhaji Nasiru Ado Bayero (Sarkin Bichi na biyu), da Dakta Ibrahim Abubakar II (Sarkin Karaye), da Alhaji Kabiru Muhammad-Inuwa (Sarkin Rano) da Aliyu Ibrahim-Gaya (Sarkin Gaya).

Sauran su ne sufeto janar na ‘yansanda, da daraktan hukumar tsaro ta farin kaya a jihar (DSS), da hukumar tsaro ta farin kaya (NSCDC), da kuma rundunar sojojin Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

Afuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka: Ta Bar Baya Da Ƙura

Shari’ar dai ta biyo bayan dambarwar matakin da gwamnatin jihar Kano ta dauka ne na tsige sarakunan jihar guda biyar, wadanda tsohuwar gwamnatin Gwamna Abdullahi Ganduje ta nada.

Matakin soke masarautun hudu daga cikin biyar din da gwamnatin baya ta kirkiro ya haifar da cece-kuce a jihar, inda Sarkin Kano na 15, Bayero ya ke zaman fada a karamar fadar Nasarawa da ke Kano yayin da Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II da aka mayar ke zaman fada a babbar fadar gidan sarkin Kano.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja
Manyan Labarai

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

October 17, 2025
Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja
Manyan Labarai

Afuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka: Ta Bar Baya Da Ƙura

October 17, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

October 16, 2025
Next Post
Gdpn Sin Ya Karu Da Kashi 5% A Watanni Shida Na Farkon Bana

Gdpn Sin Ya Karu Da Kashi 5% A Watanni Shida Na Farkon Bana

LABARAI MASU NASABA

A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Zan Tabbatar Ana Tafiyar Da Ayyuka A Tashoshin Jiragen Ruwa A Afrika Ta Yamma —Dantsoho

October 17, 2025
Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

October 17, 2025
peter

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
Ƙungiyar NNYLF Ta Gargaɗi Atiku Da Sowore Kan Cinna Wutar Rikici A Nijeriya

Ƙungiyar NNYLF Ta Gargaɗi Atiku Da Sowore Kan Cinna Wutar Rikici A Nijeriya

October 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilin Karyewar Farashin Kayan Abinci

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilin Karyewar Farashin Kayan Abinci

October 17, 2025
Tinubu

Batun Yin Afuwa Ga ‘Yan Yankin Ogoni Huɗu

October 17, 2025
Shettima

‘Yan Nijeriya Na Dab Da Fita Daga Halin Kuncin Talauci – Shettima 

October 17, 2025
Manzon Allah

Manzon Allah (SAW) Ne Ya Kafa Tushen Wayewar Kai A Duniya

October 17, 2025
An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai

Yadda ‘Yan Bindiga Ke Zafafa Hare-hare A Jihohin Arewa Maso Yamma

October 17, 2025
Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

Afuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka: Ta Bar Baya Da Ƙura

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.