• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Ɗumi-ɗuminsa: ‘Yan Bindiga Sun Afka Gidan Sarkin Kagarko A Kudancin Kaduna, Sun Tafi Da Iyalansa

by yahuzajere
2 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa
0
Da Ɗumi-ɗuminsa: ‘Yan Bindiga Sun Afka Gidan Sarkin Kagarko A Kudancin Kaduna, Sun Tafi Da Iyalansa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarin da muke samu da ɗumi-ɗuminsa ya bayyana cewa a jiya da dare da misalin ƙarfe 10, ‘yan bindiga sun auka gidan Sarkin Kagarko mai daraja ta biyu da ke Kudancin Kaduna, inda suka yi awon gaba da wasu iyalansa.

Majiyarmu daga garin na Kagarko ta bayyana mana cewa, daga cikin waɗanda aka tafi da su akwai matar sarkin guda ɗaya, sai kuma matan ‘ya’yansa da jikoki.

  • Yanzu-yanzu: Jirgin Max Air Ya Yi Hatsari A Filin Jirgin Saman Abuja

Majiyar ta ƙara da cewa, sun yi yunƙurin tafiya da mai martaba sarkin, “suka ce masa ya tashi su tafi, sai ya ce musu ba shi da ƙoshin lafiya, sai suka ce za su kashe shi, sai ya ce musu ai dama abin da yake jira kenan. To, daga nan ne suka ƙyale shi.” In ji majiyar.

Har ila yau, majiyar ta ce an ɗauki tsawon lokaci ‘yan bindigar suna cin karensu ba babbaka a gidan sarkin ba tare da an kawo ɗauki ba daga jami’an tsaro.

Mun yi ƙoƙarin jin ta bakin Sakataren Masarautar Kagarko, Malam Yahaya Ibrahim, sai dai ya ce suna shirin fitar da sanarwar manema labarai dangane da lamarin.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Soke Ziyarar Kaduna, Zai Tafi Benuwe Saboda Rikice-Rikice

An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya

Zuwa lokacin haɗa wannan rahoto dai babu wata sanarwa game da lamarin daga Rundunar ‘Yansandan Jihar Kaduna.

A kwanan nan dai ‘yan bindiga na ƙara zafafa hare-haren da suke kaiwa a yankin Ƙaramar Hukumar Kagarko da ke Kudancin Jihar Kaduna, inda ko a ‘yan kwanakin da suka gabata, sun tarwatsa wasu ƙauyuka da ke gabashin garin Kagarko musamman ƙauyen Janjala.

Kana sojoji sun yi dirar mikiya a garin na Kagarko a makon da ya gabata inda suka damƙe wasu da ake zargin masu yi wa ‘yan bindigar leƙen asiri ne.

Waɗanda aka kaman, sun jagoranci sojojin zuwa cafke ƙarin wasu masu yi wa ‘yan bindigar leƙen asiri a ƙauyen Janjala ciki har da Madakin Janjala inda ake ci gaba da bincike a kansu.

Wannan ya sa wasu ke hasashen ‘yan bindigar sun kai farmaki gidan Sarkin na Kagarko ne domin ɗaukar fansa. Amma dai sakamakon bincike ne zai tantance hakan.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Garkuwa Da Shugaban Karamar Hukuma A Taraba, An Kashe Mai Tsaronsa

Next Post

Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

Related

Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Soke Ziyarar Kaduna, Zai Tafi Benuwe Saboda Rikice-Rikice

2 weeks ago
An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya
Da ɗumi-ɗuminsa

An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya

1 month ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

2 months ago
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

2 months ago
Gobara Ta Tashi A Barikin Sojoji A Borno, Bama-bamai Sun Fashe
Da ɗumi-ɗuminsa

Gobara Ta Tashi A Barikin Sojoji A Borno, Bama-bamai Sun Fashe

2 months ago
Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N835 Kan Kowace Lita
Da ɗumi-ɗuminsa

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N835 Kan Kowace Lita

3 months ago
Next Post
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.