ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Ɗumi-ɗuminsa: ‘Yan Bindiga Sun Afka Gidan Sarkin Kagarko A Kudancin Kaduna, Sun Tafi Da Iyalansa

by yahuzajere
3 years ago
yan bindiga

Labarin da muke samu da ɗumi-ɗuminsa ya bayyana cewa a jiya da dare da misalin ƙarfe 10, ‘yan bindiga sun auka gidan Sarkin Kagarko mai daraja ta biyu da ke Kudancin Kaduna, inda suka yi awon gaba da wasu iyalansa.

Majiyarmu daga garin na Kagarko ta bayyana mana cewa, daga cikin waɗanda aka tafi da su akwai matar sarkin guda ɗaya, sai kuma matan ‘ya’yansa da jikoki.

  • Yanzu-yanzu: Jirgin Max Air Ya Yi Hatsari A Filin Jirgin Saman Abuja

Majiyar ta ƙara da cewa, sun yi yunƙurin tafiya da mai martaba sarkin, “suka ce masa ya tashi su tafi, sai ya ce musu ba shi da ƙoshin lafiya, sai suka ce za su kashe shi, sai ya ce musu ai dama abin da yake jira kenan. To, daga nan ne suka ƙyale shi.” In ji majiyar.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, majiyar ta ce an ɗauki tsawon lokaci ‘yan bindigar suna cin karensu ba babbaka a gidan sarkin ba tare da an kawo ɗauki ba daga jami’an tsaro.

Mun yi ƙoƙarin jin ta bakin Sakataren Masarautar Kagarko, Malam Yahaya Ibrahim, sai dai ya ce suna shirin fitar da sanarwar manema labarai dangane da lamarin.

LABARAI MASU NASABA

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

Zuwa lokacin haɗa wannan rahoto dai babu wata sanarwa game da lamarin daga Rundunar ‘Yansandan Jihar Kaduna.

A kwanan nan dai ‘yan bindiga na ƙara zafafa hare-haren da suke kaiwa a yankin Ƙaramar Hukumar Kagarko da ke Kudancin Jihar Kaduna, inda ko a ‘yan kwanakin da suka gabata, sun tarwatsa wasu ƙauyuka da ke gabashin garin Kagarko musamman ƙauyen Janjala.

Kana sojoji sun yi dirar mikiya a garin na Kagarko a makon da ya gabata inda suka damƙe wasu da ake zargin masu yi wa ‘yan bindigar leƙen asiri ne.

Waɗanda aka kaman, sun jagoranci sojojin zuwa cafke ƙarin wasu masu yi wa ‘yan bindigar leƙen asiri a ƙauyen Janjala ciki har da Madakin Janjala inda ake ci gaba da bincike a kansu.

Wannan ya sa wasu ke hasashen ‘yan bindigar sun kai farmaki gidan Sarkin na Kagarko ne domin ɗaukar fansa. Amma dai sakamakon bincike ne zai tantance hakan.

 

yan bindiga
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa
Da ɗumi-ɗuminsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa
Manyan Labarai

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

July 10, 2026
An Kama Tsohon Minista Uche Nnaji Kan Zargin Amfani Da Takardun Bogi
Da ɗumi-ɗuminsa

An Kama Tsohon Minista Uche Nnaji Kan Zargin Amfani Da Takardun Bogi

July 1, 2026
Next Post
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.