• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Ɗumi-ɗuminsa: ‘Yan Bindiga Sun Afka Gidan Sarkin Kagarko A Kudancin Kaduna, Sun Tafi Da Iyalansa

by yahuzajere
2 years ago
yan bindiga

Labarin da muke samu da ɗumi-ɗuminsa ya bayyana cewa a jiya da dare da misalin ƙarfe 10, ‘yan bindiga sun auka gidan Sarkin Kagarko mai daraja ta biyu da ke Kudancin Kaduna, inda suka yi awon gaba da wasu iyalansa.

Majiyarmu daga garin na Kagarko ta bayyana mana cewa, daga cikin waɗanda aka tafi da su akwai matar sarkin guda ɗaya, sai kuma matan ‘ya’yansa da jikoki.

  • Yanzu-yanzu: Jirgin Max Air Ya Yi Hatsari A Filin Jirgin Saman Abuja

Majiyar ta ƙara da cewa, sun yi yunƙurin tafiya da mai martaba sarkin, “suka ce masa ya tashi su tafi, sai ya ce musu ba shi da ƙoshin lafiya, sai suka ce za su kashe shi, sai ya ce musu ai dama abin da yake jira kenan. To, daga nan ne suka ƙyale shi.” In ji majiyar.

Har ila yau, majiyar ta ce an ɗauki tsawon lokaci ‘yan bindigar suna cin karensu ba babbaka a gidan sarkin ba tare da an kawo ɗauki ba daga jami’an tsaro.

Mun yi ƙoƙarin jin ta bakin Sakataren Masarautar Kagarko, Malam Yahaya Ibrahim, sai dai ya ce suna shirin fitar da sanarwar manema labarai dangane da lamarin.

LABARAI MASU NASABA

Kwamitin Shura Na Kano Ya Dakatar Da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

Zuwa lokacin haɗa wannan rahoto dai babu wata sanarwa game da lamarin daga Rundunar ‘Yansandan Jihar Kaduna.

A kwanan nan dai ‘yan bindiga na ƙara zafafa hare-haren da suke kaiwa a yankin Ƙaramar Hukumar Kagarko da ke Kudancin Jihar Kaduna, inda ko a ‘yan kwanakin da suka gabata, sun tarwatsa wasu ƙauyuka da ke gabashin garin Kagarko musamman ƙauyen Janjala.

Kana sojoji sun yi dirar mikiya a garin na Kagarko a makon da ya gabata inda suka damƙe wasu da ake zargin masu yi wa ‘yan bindigar leƙen asiri ne.

Waɗanda aka kaman, sun jagoranci sojojin zuwa cafke ƙarin wasu masu yi wa ‘yan bindigar leƙen asiri a ƙauyen Janjala ciki har da Madakin Janjala inda ake ci gaba da bincike a kansu.

Wannan ya sa wasu ke hasashen ‘yan bindigar sun kai farmaki gidan Sarkin na Kagarko ne domin ɗaukar fansa. Amma dai sakamakon bincike ne zai tantance hakan.

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwamitin Shura Na Kano Ya Dakatar Da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwamitin Shura Na Kano Ya Dakatar Da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

October 1, 2025
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
Da ɗumi-ɗuminsa

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

September 16, 2025
Next Post
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

LABARAI MASU NASABA

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.