• English
  • Business News
Wednesday, July 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Ɗumi-ɗuminsa: ‘Yan Bindiga Sun Afka Gidan Sarkin Kagarko A Kudancin Kaduna, Sun Tafi Da Iyalansa

by yahuzajere
2 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa
0
Da Ɗumi-ɗuminsa: ‘Yan Bindiga Sun Afka Gidan Sarkin Kagarko A Kudancin Kaduna, Sun Tafi Da Iyalansa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarin da muke samu da ɗumi-ɗuminsa ya bayyana cewa a jiya da dare da misalin ƙarfe 10, ‘yan bindiga sun auka gidan Sarkin Kagarko mai daraja ta biyu da ke Kudancin Kaduna, inda suka yi awon gaba da wasu iyalansa.

Majiyarmu daga garin na Kagarko ta bayyana mana cewa, daga cikin waɗanda aka tafi da su akwai matar sarkin guda ɗaya, sai kuma matan ‘ya’yansa da jikoki.

  • Yanzu-yanzu: Jirgin Max Air Ya Yi Hatsari A Filin Jirgin Saman Abuja

Majiyar ta ƙara da cewa, sun yi yunƙurin tafiya da mai martaba sarkin, “suka ce masa ya tashi su tafi, sai ya ce musu ba shi da ƙoshin lafiya, sai suka ce za su kashe shi, sai ya ce musu ai dama abin da yake jira kenan. To, daga nan ne suka ƙyale shi.” In ji majiyar.

Har ila yau, majiyar ta ce an ɗauki tsawon lokaci ‘yan bindigar suna cin karensu ba babbaka a gidan sarkin ba tare da an kawo ɗauki ba daga jami’an tsaro.

Mun yi ƙoƙarin jin ta bakin Sakataren Masarautar Kagarko, Malam Yahaya Ibrahim, sai dai ya ce suna shirin fitar da sanarwar manema labarai dangane da lamarin.

Labarai Masu Nasaba

Da Ɗumi-Ɗumi: Shettima Ya Isa Katsina Da Gawar Buhari

Sojoji Sun Kama Mutane 50 Masu Fasa-ƙwaurin Mai Da Lalata Haramtattun Matatun Mai A Neja-Delta

Zuwa lokacin haɗa wannan rahoto dai babu wata sanarwa game da lamarin daga Rundunar ‘Yansandan Jihar Kaduna.

A kwanan nan dai ‘yan bindiga na ƙara zafafa hare-haren da suke kaiwa a yankin Ƙaramar Hukumar Kagarko da ke Kudancin Jihar Kaduna, inda ko a ‘yan kwanakin da suka gabata, sun tarwatsa wasu ƙauyuka da ke gabashin garin Kagarko musamman ƙauyen Janjala.

Kana sojoji sun yi dirar mikiya a garin na Kagarko a makon da ya gabata inda suka damƙe wasu da ake zargin masu yi wa ‘yan bindigar leƙen asiri ne.

Waɗanda aka kaman, sun jagoranci sojojin zuwa cafke ƙarin wasu masu yi wa ‘yan bindigar leƙen asiri a ƙauyen Janjala ciki har da Madakin Janjala inda ake ci gaba da bincike a kansu.

Wannan ya sa wasu ke hasashen ‘yan bindigar sun kai farmaki gidan Sarkin na Kagarko ne domin ɗaukar fansa. Amma dai sakamakon bincike ne zai tantance hakan.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Garkuwa Da Shugaban Karamar Hukuma A Taraba, An Kashe Mai Tsaronsa

Next Post

Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

Related

Da Ɗumi-Ɗumi: Shettima Ya Isa Katsina Da Gawar Buhari
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-Ɗumi: Shettima Ya Isa Katsina Da Gawar Buhari

18 hours ago
An Tsaurara Matakan Tsaro A Daura Gabanin Jana’izar Buhari A Gobe Talata
Da ɗumi-ɗuminsa

Sojoji Sun Kama Mutane 50 Masu Fasa-ƙwaurin Mai Da Lalata Haramtattun Matatun Mai A Neja-Delta

2 days ago
An Tsaurara Matakan Tsaro A Daura Gabanin Jana’izar Buhari A Gobe Talata
Da ɗumi-ɗuminsa

An Tsaurara Matakan Tsaro A Daura Gabanin Jana’izar Buhari A Gobe Talata

2 days ago
DA ƊUMI-ƊUMI: An Ɗage Jana’izar Buhari Zuwa Gobe Talata A Mahaifarsa Ta Daura, Jihar Katsina
Da ɗumi-ɗuminsa

DA ƊUMI-ƊUMI: An Ɗage Jana’izar Buhari Zuwa Gobe Talata A Mahaifarsa Ta Daura, Jihar Katsina

2 days ago
DA ƊUMI-ƊUMI: Wani Gidan Bene Mai Hawa Uku Ya Rufto, Ya Kashe Mutum 4, Da Jikkata 7 A Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

DA ƊUMI-ƊUMI: Wani Gidan Bene Mai Hawa Uku Ya Rufto, Ya Kashe Mutum 4, Da Jikkata 7 A Kano

2 days ago
Wakilan Gwamnati Sun Isa Birnin Landan Don Rako Gawar Buhari Zuwa Gida Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Wakilan Gwamnati Sun Isa Birnin Landan Don Rako Gawar Buhari Zuwa Gida Nijeriya

2 days ago
Next Post
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

LABARAI MASU NASABA

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Yara 2 Sun Kuɓuta Bayan Shafe Shekaru 6 A Hannun Boko Haram A Borno

July 16, 2025
Kasa Da Wata Biyu Ya Bar Mulki, Shin Ko Buhari Ya Cika Wa ‘Yan Nijeriya Alkawarin Da Ya Yi Mu Su?

EU, Turkiyya Da Sauran Ƙasashe Sun Yi Ta’aziyyar Rasuwar Buhari

July 16, 2025
Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

July 15, 2025
Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

July 15, 2025
VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

July 15, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

July 15, 2025
An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

July 15, 2025
Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

July 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

July 15, 2025
Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

July 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.