• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Dumi-Dumi: ASUU Ta Musanta Shirin Sake Shiga Yajin Aiki 

by Sadiq
3 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa
0
Da Dumi-Dumi: ASUU Ta Musanta Shirin Sake Shiga Yajin Aiki 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar malaman jami’o’i ta kasa (ASUU), ta kawo karshen taronta na kwamitin zartarwa na kasa (NEC) da kudirinta na sake shiga wani sabon yajin aiki. 

Sai dai kungiyar ta yi Allah-wadai da yunkurin gwamnatin tarayya na mayar da malaman jami’o’i zaman banza ta hanyar biyansu albashinkwanaki 18.

  • An Rufe Kasuwar Dutsen Alhaji Saboda Kazanta A Abuja
  • Shugaban Kasar Sin Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Cikar Kungiyar INBAR Shekaru 25 Da Kafuwa

A wata sanarwa da ta raba wa manema labarai a ranar Talata, bayan kammala taron NEC, shugaban ASUU na kasa, Farfesa Emmanuel Osodeke, ya bayyana cewa malaman jami’o’i hazikai ne ba gama-garin ma’aikata ba.

Ya ce kungiyar ta dakatar da yajin aikin na watanni takwas a ranar 14 ga Oktoba, 2022 bisa bin umarnin kotun masana’antu ta kasa da kuma la’akari da kokarin tsoma bakin ‘yan Nijeriya masu kishin kasa, ciki har da Kakakin Majalisar Wakilai, Hon. Femi Gbajabiamila.

Osodeke ya yi nuni da cewa, matakin da kungiyar ta dauka na nuna amincewa da bangaren shari’a da sauran cibiyoyi da ma’aikatun gwamnati a ko da yaushe su sanya maslahar kasa gaba da duk wani abu.

Labarai Masu Nasaba

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

Shugaban ASUU, ya koka da yadda gwamnati ta mayar da martani ta hanyar biyansu kudin kwanaki 18 a matsayin albashin malaman jami’o’i na watan Oktoba 2022.

Ya ce, “Wannan mun yi imanin, a matsayinmu na kungiya masu tunani, ’yan boko, da masu kishin kasa, ba wai kawai za ta taimaka wajen warware rikicin cikin ruwan sanyi ba, har ma zai kafa hanyar samar da alakar masana’antu tsakanin gwamnati da ma’aikatan Nijeriya baki daya.

“Abin takaici, martanin da gwamnati ta mayar kan yadda ASUU ta nuna amana shi ne biyanmu kudin tsawon kwanaki goma sha takwas a matsayin albashin malaman jami’o’i na Oktoba 2022 ta yadda ake bayyana su a matsayin ma’aikata da ake biyansu a kullum!

“Wannan ba wai kawai rugujewa ba ne, amma ya saba wa duk wasu sanannun ka’idojin aiki a kowace kwangilar aiki ga masana a duniya.

“A taron gaggawa na kungiyar ASUU ta kasa (NEC), wanda aka gudanar a ranar Litinin, 7 ga watan Nuwamba, 2022, kungiyar ta tattauna kan abubuwan da suka faru tun bayan dakatar da yajin aikin.

“NEC ta lura da takaicin cewa biyan malaman jami’o’i, kamar ma’aikatan wucin gadi, ba a taba yin irinsa ba a tarihin dangantakar da ke tsakanin jami’o’i, don haka mun yi Allah-wadai da wannan yunkuri na mayar da malaman Nijeriya kamar sauran ma’aikata.

“NEC ta yaba wa kungiyar ASUU bisa jajircewa da suka yi wajen fuskantar wahalhalu daga wasu jiga-jigan masu fada a ji.”

Don haka kungiyar ASUU ta yi kira da a fahimci daliban Nijeriya, iyaye da sauran daidaikun mutane da kungiyoyin da abin ya shafa, a yayin da kungiyar ke ci gaba da bin diddigin wannan rikici da za a iya kaucewa daga doron kasa ba tare da tauye muradun jin dadin masanan Najeriya ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlbashiASUUDalibaiMalamaiYajin Aiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Rufe Kasuwar Dutsen Alhaji Saboda Kazanta A Abuja

Next Post

Dan Takarar Majalisar Wakilai A Jam’iyyar APC A Enugu Ya Rasu A Hatsarin Mota 

Related

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

4 days ago
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 
Da ɗumi-ɗuminsa

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

1 week ago
Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
Da ɗumi-ɗuminsa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

2 weeks ago
Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

2 weeks ago
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

2 weeks ago
Gwamnatin Sakkwato Ta Ƙaddamar Da Sababbin Motoci 30, Don Bunƙasa Sha’anin Sufuri A Jihar
Da ɗumi-ɗuminsa

Super Falcons Sun Iso Abuja Ɗauke Da Kofin WAFCON

2 weeks ago
Next Post
Dan Takarar Majalisar Wakilai A Jam’iyyar APC A Enugu Ya Rasu A Hatsarin Mota 

Dan Takarar Majalisar Wakilai A Jam'iyyar APC A Enugu Ya Rasu A Hatsarin Mota 

LABARAI MASU NASABA

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

August 9, 2025
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

August 9, 2025
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

August 9, 2025
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

August 9, 2025
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

August 9, 2025
Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

August 9, 2025
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

August 9, 2025
An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

August 9, 2025
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.