• English
  • Business News
Monday, October 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Dumi-Dumi: ASUU Ta Musanta Shirin Sake Shiga Yajin Aiki 

by Sadiq
3 years ago
ASUU

Kungiyar malaman jami’o’i ta kasa (ASUU), ta kawo karshen taronta na kwamitin zartarwa na kasa (NEC) da kudirinta na sake shiga wani sabon yajin aiki. 

Sai dai kungiyar ta yi Allah-wadai da yunkurin gwamnatin tarayya na mayar da malaman jami’o’i zaman banza ta hanyar biyansu albashinkwanaki 18.

  • An Rufe Kasuwar Dutsen Alhaji Saboda Kazanta A Abuja
  • Shugaban Kasar Sin Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Cikar Kungiyar INBAR Shekaru 25 Da Kafuwa

A wata sanarwa da ta raba wa manema labarai a ranar Talata, bayan kammala taron NEC, shugaban ASUU na kasa, Farfesa Emmanuel Osodeke, ya bayyana cewa malaman jami’o’i hazikai ne ba gama-garin ma’aikata ba.

Ya ce kungiyar ta dakatar da yajin aikin na watanni takwas a ranar 14 ga Oktoba, 2022 bisa bin umarnin kotun masana’antu ta kasa da kuma la’akari da kokarin tsoma bakin ‘yan Nijeriya masu kishin kasa, ciki har da Kakakin Majalisar Wakilai, Hon. Femi Gbajabiamila.

Osodeke ya yi nuni da cewa, matakin da kungiyar ta dauka na nuna amincewa da bangaren shari’a da sauran cibiyoyi da ma’aikatun gwamnati a ko da yaushe su sanya maslahar kasa gaba da duk wani abu.

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

Shugaban ASUU, ya koka da yadda gwamnati ta mayar da martani ta hanyar biyansu kudin kwanaki 18 a matsayin albashin malaman jami’o’i na watan Oktoba 2022.

Ya ce, “Wannan mun yi imanin, a matsayinmu na kungiya masu tunani, ’yan boko, da masu kishin kasa, ba wai kawai za ta taimaka wajen warware rikicin cikin ruwan sanyi ba, har ma zai kafa hanyar samar da alakar masana’antu tsakanin gwamnati da ma’aikatan Nijeriya baki daya.

“Abin takaici, martanin da gwamnati ta mayar kan yadda ASUU ta nuna amana shi ne biyanmu kudin tsawon kwanaki goma sha takwas a matsayin albashin malaman jami’o’i na Oktoba 2022 ta yadda ake bayyana su a matsayin ma’aikata da ake biyansu a kullum!

“Wannan ba wai kawai rugujewa ba ne, amma ya saba wa duk wasu sanannun ka’idojin aiki a kowace kwangilar aiki ga masana a duniya.

“A taron gaggawa na kungiyar ASUU ta kasa (NEC), wanda aka gudanar a ranar Litinin, 7 ga watan Nuwamba, 2022, kungiyar ta tattauna kan abubuwan da suka faru tun bayan dakatar da yajin aikin.

“NEC ta lura da takaicin cewa biyan malaman jami’o’i, kamar ma’aikatan wucin gadi, ba a taba yin irinsa ba a tarihin dangantakar da ke tsakanin jami’o’i, don haka mun yi Allah-wadai da wannan yunkuri na mayar da malaman Nijeriya kamar sauran ma’aikata.

“NEC ta yaba wa kungiyar ASUU bisa jajircewa da suka yi wajen fuskantar wahalhalu daga wasu jiga-jigan masu fada a ji.”

Don haka kungiyar ASUU ta yi kira da a fahimci daliban Nijeriya, iyaye da sauran daidaikun mutane da kungiyoyin da abin ya shafa, a yayin da kungiyar ke ci gaba da bin diddigin wannan rikici da za a iya kaucewa daga doron kasa ba tare da tauye muradun jin dadin masanan Najeriya ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta
Da ɗumi-ɗuminsa

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

October 22, 2025
Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas
Da ɗumi-ɗuminsa

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

October 22, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Next Post
Dan Takarar Majalisar Wakilai A Jam’iyyar APC A Enugu Ya Rasu A Hatsarin Mota 

Dan Takarar Majalisar Wakilai A Jam'iyyar APC A Enugu Ya Rasu A Hatsarin Mota 

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

October 27, 2025
Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

October 27, 2025
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Ba Za A Samu Ƙarancin Man Fetur A Lokutan Bukukuwan Ƙarshen Shekara Ba – Dangote 

October 27, 2025
An Zaɓi Birgediya Janar Yake A Matsayin Sarkin Sayawa Na Farko Duk Da Zanga-zanga 

An Zaɓi Birgediya Janar Yake A Matsayin Sarkin Sayawa Na Farko Duk Da Zanga-zanga 

October 27, 2025
ASUU

Tsohon Gwamnan Jigawa, Lamido Ya Bayyana Aniyar Takarar Shugabancin Jam’iyyar PDP Na Ƙasa

October 27, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno

October 27, 2025
Hatsarin Jiragen Ruwa

Matasa 5 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Gombe

October 27, 2025
Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

October 26, 2025
Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

October 26, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.