• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Dumi-Dumi: ASUU Ta Musanta Shirin Sake Shiga Yajin Aiki 

by Sadiq
3 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa
0
Da Dumi-Dumi: ASUU Ta Musanta Shirin Sake Shiga Yajin Aiki 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar malaman jami’o’i ta kasa (ASUU), ta kawo karshen taronta na kwamitin zartarwa na kasa (NEC) da kudirinta na sake shiga wani sabon yajin aiki. 

Sai dai kungiyar ta yi Allah-wadai da yunkurin gwamnatin tarayya na mayar da malaman jami’o’i zaman banza ta hanyar biyansu albashinkwanaki 18.

  • An Rufe Kasuwar Dutsen Alhaji Saboda Kazanta A Abuja
  • Shugaban Kasar Sin Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Cikar Kungiyar INBAR Shekaru 25 Da Kafuwa

A wata sanarwa da ta raba wa manema labarai a ranar Talata, bayan kammala taron NEC, shugaban ASUU na kasa, Farfesa Emmanuel Osodeke, ya bayyana cewa malaman jami’o’i hazikai ne ba gama-garin ma’aikata ba.

Ya ce kungiyar ta dakatar da yajin aikin na watanni takwas a ranar 14 ga Oktoba, 2022 bisa bin umarnin kotun masana’antu ta kasa da kuma la’akari da kokarin tsoma bakin ‘yan Nijeriya masu kishin kasa, ciki har da Kakakin Majalisar Wakilai, Hon. Femi Gbajabiamila.

Osodeke ya yi nuni da cewa, matakin da kungiyar ta dauka na nuna amincewa da bangaren shari’a da sauran cibiyoyi da ma’aikatun gwamnati a ko da yaushe su sanya maslahar kasa gaba da duk wani abu.

Labarai Masu Nasaba

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

Shugaban ASUU, ya koka da yadda gwamnati ta mayar da martani ta hanyar biyansu kudin kwanaki 18 a matsayin albashin malaman jami’o’i na watan Oktoba 2022.

Ya ce, “Wannan mun yi imanin, a matsayinmu na kungiya masu tunani, ’yan boko, da masu kishin kasa, ba wai kawai za ta taimaka wajen warware rikicin cikin ruwan sanyi ba, har ma zai kafa hanyar samar da alakar masana’antu tsakanin gwamnati da ma’aikatan Nijeriya baki daya.

“Abin takaici, martanin da gwamnati ta mayar kan yadda ASUU ta nuna amana shi ne biyanmu kudin tsawon kwanaki goma sha takwas a matsayin albashin malaman jami’o’i na Oktoba 2022 ta yadda ake bayyana su a matsayin ma’aikata da ake biyansu a kullum!

“Wannan ba wai kawai rugujewa ba ne, amma ya saba wa duk wasu sanannun ka’idojin aiki a kowace kwangilar aiki ga masana a duniya.

“A taron gaggawa na kungiyar ASUU ta kasa (NEC), wanda aka gudanar a ranar Litinin, 7 ga watan Nuwamba, 2022, kungiyar ta tattauna kan abubuwan da suka faru tun bayan dakatar da yajin aikin.

“NEC ta lura da takaicin cewa biyan malaman jami’o’i, kamar ma’aikatan wucin gadi, ba a taba yin irinsa ba a tarihin dangantakar da ke tsakanin jami’o’i, don haka mun yi Allah-wadai da wannan yunkuri na mayar da malaman Nijeriya kamar sauran ma’aikata.

“NEC ta yaba wa kungiyar ASUU bisa jajircewa da suka yi wajen fuskantar wahalhalu daga wasu jiga-jigan masu fada a ji.”

Don haka kungiyar ASUU ta yi kira da a fahimci daliban Nijeriya, iyaye da sauran daidaikun mutane da kungiyoyin da abin ya shafa, a yayin da kungiyar ke ci gaba da bin diddigin wannan rikici da za a iya kaucewa daga doron kasa ba tare da tauye muradun jin dadin masanan Najeriya ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlbashiASUUDalibaiMalamaiYajin Aiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Rufe Kasuwar Dutsen Alhaji Saboda Kazanta A Abuja

Next Post

Dan Takarar Majalisar Wakilai A Jam’iyyar APC A Enugu Ya Rasu A Hatsarin Mota 

Related

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

1 day ago
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba
Da ɗumi-ɗuminsa

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

2 weeks ago
Da Ɗumi-Ɗumi: Jami’an Tsaro Sun Kama Manyan Shugabannin Ƙungiyar Ansaru 2
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-Ɗumi: Jami’an Tsaro Sun Kama Manyan Shugabannin Ƙungiyar Ansaru 2

3 weeks ago
Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

1 month ago
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 
Da ɗumi-ɗuminsa

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

1 month ago
Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
Da ɗumi-ɗuminsa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

1 month ago
Next Post
Dan Takarar Majalisar Wakilai A Jam’iyyar APC A Enugu Ya Rasu A Hatsarin Mota 

Dan Takarar Majalisar Wakilai A Jam'iyyar APC A Enugu Ya Rasu A Hatsarin Mota 

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

September 6, 2025

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

September 6, 2025
NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

September 6, 2025
Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

September 6, 2025
Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

September 5, 2025
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

September 5, 2025
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

September 5, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.