ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Dumi-Dumi: ASUU Ta Musanta Shirin Sake Shiga Yajin Aiki 

by Sadiq
4 years ago
ASUU

Kungiyar malaman jami’o’i ta kasa (ASUU), ta kawo karshen taronta na kwamitin zartarwa na kasa (NEC) da kudirinta na sake shiga wani sabon yajin aiki. 

Sai dai kungiyar ta yi Allah-wadai da yunkurin gwamnatin tarayya na mayar da malaman jami’o’i zaman banza ta hanyar biyansu albashinkwanaki 18.

  • An Rufe Kasuwar Dutsen Alhaji Saboda Kazanta A Abuja
  • Shugaban Kasar Sin Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Cikar Kungiyar INBAR Shekaru 25 Da Kafuwa

A wata sanarwa da ta raba wa manema labarai a ranar Talata, bayan kammala taron NEC, shugaban ASUU na kasa, Farfesa Emmanuel Osodeke, ya bayyana cewa malaman jami’o’i hazikai ne ba gama-garin ma’aikata ba.

ADVERTISEMENT

Ya ce kungiyar ta dakatar da yajin aikin na watanni takwas a ranar 14 ga Oktoba, 2022 bisa bin umarnin kotun masana’antu ta kasa da kuma la’akari da kokarin tsoma bakin ‘yan Nijeriya masu kishin kasa, ciki har da Kakakin Majalisar Wakilai, Hon. Femi Gbajabiamila.

Osodeke ya yi nuni da cewa, matakin da kungiyar ta dauka na nuna amincewa da bangaren shari’a da sauran cibiyoyi da ma’aikatun gwamnati a ko da yaushe su sanya maslahar kasa gaba da duk wani abu.

LABARAI MASU NASABA

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

Shugaban ASUU, ya koka da yadda gwamnati ta mayar da martani ta hanyar biyansu kudin kwanaki 18 a matsayin albashin malaman jami’o’i na watan Oktoba 2022.

Ya ce, “Wannan mun yi imanin, a matsayinmu na kungiya masu tunani, ’yan boko, da masu kishin kasa, ba wai kawai za ta taimaka wajen warware rikicin cikin ruwan sanyi ba, har ma zai kafa hanyar samar da alakar masana’antu tsakanin gwamnati da ma’aikatan Nijeriya baki daya.

“Abin takaici, martanin da gwamnati ta mayar kan yadda ASUU ta nuna amana shi ne biyanmu kudin tsawon kwanaki goma sha takwas a matsayin albashin malaman jami’o’i na Oktoba 2022 ta yadda ake bayyana su a matsayin ma’aikata da ake biyansu a kullum!

“Wannan ba wai kawai rugujewa ba ne, amma ya saba wa duk wasu sanannun ka’idojin aiki a kowace kwangilar aiki ga masana a duniya.

“A taron gaggawa na kungiyar ASUU ta kasa (NEC), wanda aka gudanar a ranar Litinin, 7 ga watan Nuwamba, 2022, kungiyar ta tattauna kan abubuwan da suka faru tun bayan dakatar da yajin aikin.

“NEC ta lura da takaicin cewa biyan malaman jami’o’i, kamar ma’aikatan wucin gadi, ba a taba yin irinsa ba a tarihin dangantakar da ke tsakanin jami’o’i, don haka mun yi Allah-wadai da wannan yunkuri na mayar da malaman Nijeriya kamar sauran ma’aikata.

“NEC ta yaba wa kungiyar ASUU bisa jajircewa da suka yi wajen fuskantar wahalhalu daga wasu jiga-jigan masu fada a ji.”

Don haka kungiyar ASUU ta yi kira da a fahimci daliban Nijeriya, iyaye da sauran daidaikun mutane da kungiyoyin da abin ya shafa, a yayin da kungiyar ke ci gaba da bin diddigin wannan rikici da za a iya kaucewa daga doron kasa ba tare da tauye muradun jin dadin masanan Najeriya ba.

MASU ALAKA

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa
Da ɗumi-ɗuminsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa
Manyan Labarai

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

July 10, 2026
An Kama Tsohon Minista Uche Nnaji Kan Zargin Amfani Da Takardun Bogi
Da ɗumi-ɗuminsa

An Kama Tsohon Minista Uche Nnaji Kan Zargin Amfani Da Takardun Bogi

July 1, 2026
Next Post
Dan Takarar Majalisar Wakilai A Jam’iyyar APC A Enugu Ya Rasu A Hatsarin Mota 

Dan Takarar Majalisar Wakilai A Jam'iyyar APC A Enugu Ya Rasu A Hatsarin Mota 

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.