ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Gaske Arsenal Ta Kawo Karfi?

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Arsenal

A shekarun baya idan ana maganar kungiyoyin da za su iya lashe gasar firimiyar Ingila kungiyar Arsenal ba ta shigowa saboda rashin kokarin kungiyar da kuma rashin tsarin shugabanci a lokacin, wanda har ta kai kungiyar ba ta iya zuwa gasar cin kofin Zakarun Turai a jere.

Amma a yanzu ya zama dole ka saka Arsenal a cikin jerin kungiyoyin da za su iya lashe gasar, ko ba don komai ba, domin irin kokarin kungiyar a cikin shekaru biyu, na zamowa daya daga cikin manyan kungiyoyin da suke takarar lashe firimiyar Ingila.

  • Arsenal Ta Sake Tabbatar Da Cancantar Lashe Firimiya
  • Hakuri Ya Zama Dole Ga Magoya Bayan Manchester United, Cewar Ratcliffe

A ranar Lahadi kungiyar kwallon kafa ta Arsenal ta je ta doke kungiyar Tottenham da ci 3-2 a wasan mako na 35 a gasar Premier da suka kara a wasan hamayya kuma Arsenal ce ta fara zura kwallaye uku a raga ta hannun Pierre-Emile Hojbjerg, wanda ya ci gida a minti na 15 da fara wasa sai dan wasa Bukayo Saka da ya zura kwallo ta biyu sai kuma Kai Habertz da ya zura ta uku.

ADVERTISEMENT

Haka kuma dan wasa Saka ya zama dan wasan tawagar Ingila da ya ci Tottenham gida da waje a Premier League a kaka daya, tun bayan bajintar Ian Wright ya yi a shekarar 1993 zuwa 1994.

Amma daga baya Tottenham ta zare kwallaye biyu ta hannun Cristian Romero da Heung-min Son a bugun fenariti kuma sakamakon wasan ya nuna karo biyu a jere Arsenal na zuwa ta na cin Tottenham tun bayan Satumbar 1988 da ta yi nasara uku, karkashin George Graham.

LABARAI MASU NASABA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

Kafin nan wasa biyu Arsenal ta ci a gidan Tottenham daga wasanni 17 da ta kai ziyara a Premier da canjaras shida aka doke ta tara daga ciki wanda hakan ya nuna irin bajintar da Arsenal din tayi cikin ‘yan shekarun nan.

Wasan na ranar Lahadi shi ne wasa na 100 da Mikel Arteta ya ci a Premier League a karawa ta 169 da ya ja ragamar Arsenal a babbar gasar firimiya ta Ingila kuma cikin wasannin ya yi canjaras 27 aka doke shi 42 da cin kwallo 321, aka zura wa Arsenal 179.
Bayan da Arsenal ta doke Tottenham ta ci gaba da zama ta daya a kan teburin Premier League da maki 80, yayin da Manchester City ce ta biyu mai maki 79, mai kwantan wasa daya sai kungiyar Liberpool, wadda ta tashi 2-2 da West Ham United tana ta ukun teburi da maki 75.

Ita ma Manchester City ta ci gaba da zama ne a mataki na biyu a teburin Premier League, bayan da ta je ta doke Nottingham Forest 2-0 a wasan mako na 35 ranar Laha-din da yamma.

Dan wasa Josko Gbardiol ne ya fara zura kwallo a raga a minti na 32, sannan Erling Halland ya ci ta biyu saura minti 19 a tashi daga wasan kuma kwallo ta 21 da Halland ya zura a raga a wasa na 25 da ya buga a bana kenan a babbar gasar firimiya ta Ingila.

Rabon da Haaland ya ci kwallo a Manchester City tun ranar 13 ga Afirilu a karawar da Manchester City ta lallasa kungiyar Luton Town 5-1 a gasar ta Premier League kuma wannan shi ne wasa na 300 da Pep Guardiola ya ja ragamar Manchester City a Premier da yin nasara 221 da canjaras 41 aka doke shi 38 sannan ya ci kwallo 741 aka zura masa 247 a raga.

Guardiola dan kasar Spain mai shekara 53 a duniya ya koma Manchester City ranar 1 ga watan Yulin 2016, yanzu yana kakar wasa ta takwas da kungiyar sannan ya kuma fara jan ragamar karawar Premier League ranar 13 ga Agustan 2016, wanda ya doke Sunderland 2-1 a Etihad.

Haaland tsohon dan wasan Borussia Dortmund wanda ya yi jinya, bai yi wa Manchester City wasan FA Cup da ta doke Chelsea ta kai zagayen karshe ranar 20 ga Afirilu ba.

Haka kuma bai samu buga wa Manchester City wasan da ta je ta dura kwallaye 4-0 a ragar Brighton ba a Premier League ranar 25 ga watan Afirilu duka saboda ciwon da yake fama da shi.

Wasannin da ke gaban Manchester City da na Arsenal:
Man City: 4 Mayu a gida da Wolbes; 11 Mayu zuwa gidan Fulham; 14 Mayu zuwa gidan Tottenham; 19 Mayu a gida da West Ham. Arsenal: 4 Mayu a gida da Bournemouth; 12 Mayu zuwa gidan Man Utd; 19. Mayu a gida da Eberton.

Arsenal
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?
  • Abba Ibrahim Wada
    Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji
  • Abba Ibrahim Wada
    Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City

MASU ALAKA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
Wasanni

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
Wasanni

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Wasanni

Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu

July 11, 2026
Next Post
An Dakatar Da Fulham Daga Sayen Matasan ‘Yan Wasa

An Dakatar Da Fulham Daga Sayen Matasan ‘Yan Wasa

LABARAI MASU NASABA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.