ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Gaske Arsenal Ta Kawo Karfi?

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Arsenal

A shekarun baya idan ana maganar kungiyoyin da za su iya lashe gasar firimiyar Ingila kungiyar Arsenal ba ta shigowa saboda rashin kokarin kungiyar da kuma rashin tsarin shugabanci a lokacin, wanda har ta kai kungiyar ba ta iya zuwa gasar cin kofin Zakarun Turai a jere.

Amma a yanzu ya zama dole ka saka Arsenal a cikin jerin kungiyoyin da za su iya lashe gasar, ko ba don komai ba, domin irin kokarin kungiyar a cikin shekaru biyu, na zamowa daya daga cikin manyan kungiyoyin da suke takarar lashe firimiyar Ingila.

  • Arsenal Ta Sake Tabbatar Da Cancantar Lashe Firimiya
  • Hakuri Ya Zama Dole Ga Magoya Bayan Manchester United, Cewar Ratcliffe

A ranar Lahadi kungiyar kwallon kafa ta Arsenal ta je ta doke kungiyar Tottenham da ci 3-2 a wasan mako na 35 a gasar Premier da suka kara a wasan hamayya kuma Arsenal ce ta fara zura kwallaye uku a raga ta hannun Pierre-Emile Hojbjerg, wanda ya ci gida a minti na 15 da fara wasa sai dan wasa Bukayo Saka da ya zura kwallo ta biyu sai kuma Kai Habertz da ya zura ta uku.

ADVERTISEMENT

Haka kuma dan wasa Saka ya zama dan wasan tawagar Ingila da ya ci Tottenham gida da waje a Premier League a kaka daya, tun bayan bajintar Ian Wright ya yi a shekarar 1993 zuwa 1994.

Amma daga baya Tottenham ta zare kwallaye biyu ta hannun Cristian Romero da Heung-min Son a bugun fenariti kuma sakamakon wasan ya nuna karo biyu a jere Arsenal na zuwa ta na cin Tottenham tun bayan Satumbar 1988 da ta yi nasara uku, karkashin George Graham.

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

Kafin nan wasa biyu Arsenal ta ci a gidan Tottenham daga wasanni 17 da ta kai ziyara a Premier da canjaras shida aka doke ta tara daga ciki wanda hakan ya nuna irin bajintar da Arsenal din tayi cikin ‘yan shekarun nan.

Wasan na ranar Lahadi shi ne wasa na 100 da Mikel Arteta ya ci a Premier League a karawa ta 169 da ya ja ragamar Arsenal a babbar gasar firimiya ta Ingila kuma cikin wasannin ya yi canjaras 27 aka doke shi 42 da cin kwallo 321, aka zura wa Arsenal 179.
Bayan da Arsenal ta doke Tottenham ta ci gaba da zama ta daya a kan teburin Premier League da maki 80, yayin da Manchester City ce ta biyu mai maki 79, mai kwantan wasa daya sai kungiyar Liberpool, wadda ta tashi 2-2 da West Ham United tana ta ukun teburi da maki 75.

Ita ma Manchester City ta ci gaba da zama ne a mataki na biyu a teburin Premier League, bayan da ta je ta doke Nottingham Forest 2-0 a wasan mako na 35 ranar Laha-din da yamma.

Dan wasa Josko Gbardiol ne ya fara zura kwallo a raga a minti na 32, sannan Erling Halland ya ci ta biyu saura minti 19 a tashi daga wasan kuma kwallo ta 21 da Halland ya zura a raga a wasa na 25 da ya buga a bana kenan a babbar gasar firimiya ta Ingila.

Rabon da Haaland ya ci kwallo a Manchester City tun ranar 13 ga Afirilu a karawar da Manchester City ta lallasa kungiyar Luton Town 5-1 a gasar ta Premier League kuma wannan shi ne wasa na 300 da Pep Guardiola ya ja ragamar Manchester City a Premier da yin nasara 221 da canjaras 41 aka doke shi 38 sannan ya ci kwallo 741 aka zura masa 247 a raga.

Guardiola dan kasar Spain mai shekara 53 a duniya ya koma Manchester City ranar 1 ga watan Yulin 2016, yanzu yana kakar wasa ta takwas da kungiyar sannan ya kuma fara jan ragamar karawar Premier League ranar 13 ga Agustan 2016, wanda ya doke Sunderland 2-1 a Etihad.

Haaland tsohon dan wasan Borussia Dortmund wanda ya yi jinya, bai yi wa Manchester City wasan FA Cup da ta doke Chelsea ta kai zagayen karshe ranar 20 ga Afirilu ba.

Haka kuma bai samu buga wa Manchester City wasan da ta je ta dura kwallaye 4-0 a ragar Brighton ba a Premier League ranar 25 ga watan Afirilu duka saboda ciwon da yake fama da shi.

Wasannin da ke gaban Manchester City da na Arsenal:
Man City: 4 Mayu a gida da Wolbes; 11 Mayu zuwa gidan Fulham; 14 Mayu zuwa gidan Tottenham; 19 Mayu a gida da West Ham. Arsenal: 4 Mayu a gida da Bournemouth; 12 Mayu zuwa gidan Man Utd; 19. Mayu a gida da Eberton.

Arsenal
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
  • Abba Ibrahim Wada
    FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa
  • Abba Ibrahim Wada
    Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

MASU ALAKA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino
Wasanni

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya
Wasanni

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

June 22, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
Wasanni

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026
Next Post
An Dakatar Da Fulham Daga Sayen Matasan ‘Yan Wasa

An Dakatar Da Fulham Daga Sayen Matasan ‘Yan Wasa

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.