ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Gaske Arsenal Ta Kawo Karfi?

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Arsenal

A shekarun baya idan ana maganar kungiyoyin da za su iya lashe gasar firimiyar Ingila kungiyar Arsenal ba ta shigowa saboda rashin kokarin kungiyar da kuma rashin tsarin shugabanci a lokacin, wanda har ta kai kungiyar ba ta iya zuwa gasar cin kofin Zakarun Turai a jere.

Amma a yanzu ya zama dole ka saka Arsenal a cikin jerin kungiyoyin da za su iya lashe gasar, ko ba don komai ba, domin irin kokarin kungiyar a cikin shekaru biyu, na zamowa daya daga cikin manyan kungiyoyin da suke takarar lashe firimiyar Ingila.

  • Arsenal Ta Sake Tabbatar Da Cancantar Lashe Firimiya
  • Hakuri Ya Zama Dole Ga Magoya Bayan Manchester United, Cewar Ratcliffe

A ranar Lahadi kungiyar kwallon kafa ta Arsenal ta je ta doke kungiyar Tottenham da ci 3-2 a wasan mako na 35 a gasar Premier da suka kara a wasan hamayya kuma Arsenal ce ta fara zura kwallaye uku a raga ta hannun Pierre-Emile Hojbjerg, wanda ya ci gida a minti na 15 da fara wasa sai dan wasa Bukayo Saka da ya zura kwallo ta biyu sai kuma Kai Habertz da ya zura ta uku.

ADVERTISEMENT

Haka kuma dan wasa Saka ya zama dan wasan tawagar Ingila da ya ci Tottenham gida da waje a Premier League a kaka daya, tun bayan bajintar Ian Wright ya yi a shekarar 1993 zuwa 1994.

Amma daga baya Tottenham ta zare kwallaye biyu ta hannun Cristian Romero da Heung-min Son a bugun fenariti kuma sakamakon wasan ya nuna karo biyu a jere Arsenal na zuwa ta na cin Tottenham tun bayan Satumbar 1988 da ta yi nasara uku, karkashin George Graham.

LABARAI MASU NASABA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

Kafin nan wasa biyu Arsenal ta ci a gidan Tottenham daga wasanni 17 da ta kai ziyara a Premier da canjaras shida aka doke ta tara daga ciki wanda hakan ya nuna irin bajintar da Arsenal din tayi cikin ‘yan shekarun nan.

Wasan na ranar Lahadi shi ne wasa na 100 da Mikel Arteta ya ci a Premier League a karawa ta 169 da ya ja ragamar Arsenal a babbar gasar firimiya ta Ingila kuma cikin wasannin ya yi canjaras 27 aka doke shi 42 da cin kwallo 321, aka zura wa Arsenal 179.
Bayan da Arsenal ta doke Tottenham ta ci gaba da zama ta daya a kan teburin Premier League da maki 80, yayin da Manchester City ce ta biyu mai maki 79, mai kwantan wasa daya sai kungiyar Liberpool, wadda ta tashi 2-2 da West Ham United tana ta ukun teburi da maki 75.

Ita ma Manchester City ta ci gaba da zama ne a mataki na biyu a teburin Premier League, bayan da ta je ta doke Nottingham Forest 2-0 a wasan mako na 35 ranar Laha-din da yamma.

Dan wasa Josko Gbardiol ne ya fara zura kwallo a raga a minti na 32, sannan Erling Halland ya ci ta biyu saura minti 19 a tashi daga wasan kuma kwallo ta 21 da Halland ya zura a raga a wasa na 25 da ya buga a bana kenan a babbar gasar firimiya ta Ingila.

Rabon da Haaland ya ci kwallo a Manchester City tun ranar 13 ga Afirilu a karawar da Manchester City ta lallasa kungiyar Luton Town 5-1 a gasar ta Premier League kuma wannan shi ne wasa na 300 da Pep Guardiola ya ja ragamar Manchester City a Premier da yin nasara 221 da canjaras 41 aka doke shi 38 sannan ya ci kwallo 741 aka zura masa 247 a raga.

Guardiola dan kasar Spain mai shekara 53 a duniya ya koma Manchester City ranar 1 ga watan Yulin 2016, yanzu yana kakar wasa ta takwas da kungiyar sannan ya kuma fara jan ragamar karawar Premier League ranar 13 ga Agustan 2016, wanda ya doke Sunderland 2-1 a Etihad.

Haaland tsohon dan wasan Borussia Dortmund wanda ya yi jinya, bai yi wa Manchester City wasan FA Cup da ta doke Chelsea ta kai zagayen karshe ranar 20 ga Afirilu ba.

Haka kuma bai samu buga wa Manchester City wasan da ta je ta dura kwallaye 4-0 a ragar Brighton ba a Premier League ranar 25 ga watan Afirilu duka saboda ciwon da yake fama da shi.

Wasannin da ke gaban Manchester City da na Arsenal:
Man City: 4 Mayu a gida da Wolbes; 11 Mayu zuwa gidan Fulham; 14 Mayu zuwa gidan Tottenham; 19 Mayu a gida da West Ham. Arsenal: 4 Mayu a gida da Bournemouth; 12 Mayu zuwa gidan Man Utd; 19. Mayu a gida da Eberton.

Arsenal
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?

MASU ALAKA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
Next Post
An Dakatar Da Fulham Daga Sayen Matasan ‘Yan Wasa

An Dakatar Da Fulham Daga Sayen Matasan ‘Yan Wasa

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.