• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Gaske Ne An Tilasta Wa Al’umma Aiki A Xinjiang?

by CGTN Hausa
1 year ago
in Ra'ayi Riga
0
Xinjiang
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

“Zan so in ce muku, bisa abin da na gani da ido, zance na wai akwai ‘aikin ala tilas’ wajen noman auduga a Xinjiang karya ce.” Malam Akram Memtimin ne ya yi wannan furucin a yayin amsa tambayar manema labarai. Akram Memtimin dan kabilar Uygur ne da ya fito daga wani kauye da ke jihar Xinjiang, kuma dan majalisar wakilan jama’ar kasar Sin ne, wanda yanzu haka ke halartar taron shekara shekara na majalisar a birnin Beijing, babban birnin kasar. Ya ce, da wuya ya fahimci me ya sa akwai kafofin yada labarai na kasashen yamma da suke yada labarai na wai “an tilasta wa dubun dubatar ‘yan kananan kabilu a jihar Xinjiang aikin tsintar auduga da hannu”. Ya ce, “auduga fari fat arzikinmu ne, ta hanyar noman auduga, mun samu kudin sayen mota da gidaje, mun ji dadin rayuwarmu, har akwai bukatar a tilasta mana yin hakan?” 

Abin haka yake, al’umma a duk kasashen da suka fito, burinsu shi ne su samu kudi ta hanyar yin aiki, don jin dadin rayuwa. Amma hakan ya zama “aikin ala tilas” a bakin gungun ‘yan siyasa da kafofin yada labarai na Amurka da sauran kasashen yamma.

  • An Rufe Taron Koli Na Kafofin Yada Labarai Dangane Da Kwaikwayon Hazikancin Dan Adam A Afrika
  • Xi Ya Jaddada Zurfafa Gyare-gyare Don Inganta Kwarewa A Sabbin Fannoni

Ban da haka, Amurka ta kuma matsa wa wasu kamfanonin kasashen waje irinsu Volkswagen da BASF, da su dakatar da ayyukansu a Xinjiang, bisa dalili na wai akwai “aikin ala tilas”. A game da wannan, Dr. Björn Alpermann, wani masanin harkokin kasar Sin a jami’ar Würzburg ta kasar Jamus, ya yi gargadin cewa, babu tabbas dangane da zargin da aka yi na wai ana “aikin ala tilas”. An ce, Dr. Björn Alpermann ya gudanar da bincike dangane da zargin da aka yi na wai “ana tilasta wa ‘yan kabilar Uygur aiki”, amma ba tare da gano shaidu ba. Ya yi gargadin kada a bar alhakin kan kamfanoni masu alaka da jihar Xinjiang, har ma a sanya haramci kan jihar Xinjiang baki daya. Ya ce, “A ganina, hakan ya wuce gona da iri, wanda ka iya haifar da barna ga al’ummar yankin, a maimakon a ce an taimaka musu.”

Amma ita Amurka hakan ta yi. Tun watan Yunin shekarar 2022, gwamnatin Amurka ta fara gudanar da dokar wai “Hana Aikin Tilas Ga Al’ummar Uygur”, bisa ga dokar, ta hana shigar da kayayyakin da aka samar a jihar Xinjiang zuwa kasar. Amurka ta yi hakan ne bisa sunan kare “hakkin dan Adam”, amma a hakika, hakan ya haifar da rashin ayyukan yi tare da mayar da al’umma cikin kangin talauci da suka baro a baya, kuma burinta shi ne ta gurbata abubuwa a jihar Xinjiang, don cimma burin dakile ci gaban kasar Sin baki daya.

Na taba zuwa Xinjiang sau da dama. Amma wallahi ban taba gani da idona abin da aka ce wai “aikin tilas” ba, a maimakon haka, na ga yadda al’umma ‘yan kabilu daban daban ke rayuwa cikin walwala. Don haka, ina so in yi wa wadanda suka kirkiro karyar tambaya, shin al’ummar kabilar Uygur ba su da ‘yancin yin aiki? Jita-jitar da aka yada ta wai “aikin tilas”, a hakika tana tilasta musu barin aiki, wadda ta sa suka kasa sayar da kayayyakin da suka samar. To hakan na kiyaye hakkin su ne ko lalata hakkinsu?

Labarai Masu Nasaba

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

A zahiri dai, saurin bunkasuwar kasar Sin cikin ‘yan shekarun baya ya sa wasu kasashe matukar damuwa, don haka suke iya kokarin hana bunkasuwar kasar. Amma dai kasar Sin tana da ‘yancin tabbatar da ci gabanta, zamanintar da kasar mai al’ummar biliyan 1.4 babban ci gaba ne ga dan Adam baki daya. Baya ga haka, bunkasuwar kasar Sin da ma kasuwarta mai matukar girma, suna samar da sabbin damammaki ga kasashe daban daban.

Kamar yadda Bahaushe kan ce, gani ya kori ji. Muna fatan ‘yan uwanmu na Afirka za ku samu damar ziyartar jihar Xinjiang. Sabo da duk wadanda suka taba zuwa jihar, sun tarar da cewa, abubuwan da suka gani da ido a jihar, sun bambanta da wadanda suka karanta a rahotannin kafofin yada labarai na kasashen yamma. (Lubabatu Lei)

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Cafke ‘Yammata Masu Yawon Dare A Yamai

Next Post

Ku Yi Haƙuri Da Gwamnatin Tinubu – Shettima

Related

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…
Ra'ayi Riga

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

3 days ago
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba
Ra'ayi Riga

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

5 days ago
Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
Ra'ayi Riga

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

1 week ago
Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
Ra'ayi Riga

Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta

2 weeks ago
Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada
Ra'ayi Riga

Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

2 weeks ago
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

2 weeks ago
Next Post
Ku Yi Haƙuri Da Gwamnatin Tinubu – Shettima

Ku Yi Haƙuri Da Gwamnatin Tinubu – Shettima

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.