ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Gaske Ne An Tilasta Wa Al’umma Aiki A Xinjiang?

by CGTN Hausa
2 years ago
Xinjiang

“Zan so in ce muku, bisa abin da na gani da ido, zance na wai akwai ‘aikin ala tilas’ wajen noman auduga a Xinjiang karya ce.” Malam Akram Memtimin ne ya yi wannan furucin a yayin amsa tambayar manema labarai. Akram Memtimin dan kabilar Uygur ne da ya fito daga wani kauye da ke jihar Xinjiang, kuma dan majalisar wakilan jama’ar kasar Sin ne, wanda yanzu haka ke halartar taron shekara shekara na majalisar a birnin Beijing, babban birnin kasar. Ya ce, da wuya ya fahimci me ya sa akwai kafofin yada labarai na kasashen yamma da suke yada labarai na wai “an tilasta wa dubun dubatar ‘yan kananan kabilu a jihar Xinjiang aikin tsintar auduga da hannu”. Ya ce, “auduga fari fat arzikinmu ne, ta hanyar noman auduga, mun samu kudin sayen mota da gidaje, mun ji dadin rayuwarmu, har akwai bukatar a tilasta mana yin hakan?” 

Abin haka yake, al’umma a duk kasashen da suka fito, burinsu shi ne su samu kudi ta hanyar yin aiki, don jin dadin rayuwa. Amma hakan ya zama “aikin ala tilas” a bakin gungun ‘yan siyasa da kafofin yada labarai na Amurka da sauran kasashen yamma.

  • An Rufe Taron Koli Na Kafofin Yada Labarai Dangane Da Kwaikwayon Hazikancin Dan Adam A Afrika
  • Xi Ya Jaddada Zurfafa Gyare-gyare Don Inganta Kwarewa A Sabbin Fannoni

Ban da haka, Amurka ta kuma matsa wa wasu kamfanonin kasashen waje irinsu Volkswagen da BASF, da su dakatar da ayyukansu a Xinjiang, bisa dalili na wai akwai “aikin ala tilas”. A game da wannan, Dr. Björn Alpermann, wani masanin harkokin kasar Sin a jami’ar Würzburg ta kasar Jamus, ya yi gargadin cewa, babu tabbas dangane da zargin da aka yi na wai ana “aikin ala tilas”. An ce, Dr. Björn Alpermann ya gudanar da bincike dangane da zargin da aka yi na wai “ana tilasta wa ‘yan kabilar Uygur aiki”, amma ba tare da gano shaidu ba. Ya yi gargadin kada a bar alhakin kan kamfanoni masu alaka da jihar Xinjiang, har ma a sanya haramci kan jihar Xinjiang baki daya. Ya ce, “A ganina, hakan ya wuce gona da iri, wanda ka iya haifar da barna ga al’ummar yankin, a maimakon a ce an taimaka musu.”

ADVERTISEMENT

Amma ita Amurka hakan ta yi. Tun watan Yunin shekarar 2022, gwamnatin Amurka ta fara gudanar da dokar wai “Hana Aikin Tilas Ga Al’ummar Uygur”, bisa ga dokar, ta hana shigar da kayayyakin da aka samar a jihar Xinjiang zuwa kasar. Amurka ta yi hakan ne bisa sunan kare “hakkin dan Adam”, amma a hakika, hakan ya haifar da rashin ayyukan yi tare da mayar da al’umma cikin kangin talauci da suka baro a baya, kuma burinta shi ne ta gurbata abubuwa a jihar Xinjiang, don cimma burin dakile ci gaban kasar Sin baki daya.

Na taba zuwa Xinjiang sau da dama. Amma wallahi ban taba gani da idona abin da aka ce wai “aikin tilas” ba, a maimakon haka, na ga yadda al’umma ‘yan kabilu daban daban ke rayuwa cikin walwala. Don haka, ina so in yi wa wadanda suka kirkiro karyar tambaya, shin al’ummar kabilar Uygur ba su da ‘yancin yin aiki? Jita-jitar da aka yada ta wai “aikin tilas”, a hakika tana tilasta musu barin aiki, wadda ta sa suka kasa sayar da kayayyakin da suka samar. To hakan na kiyaye hakkin su ne ko lalata hakkinsu?

LABARAI MASU NASABA

Bikin Baje Koli CIIE, Bikin Zaburar Da Manoman Afirka

CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

A zahiri dai, saurin bunkasuwar kasar Sin cikin ‘yan shekarun baya ya sa wasu kasashe matukar damuwa, don haka suke iya kokarin hana bunkasuwar kasar. Amma dai kasar Sin tana da ‘yancin tabbatar da ci gabanta, zamanintar da kasar mai al’ummar biliyan 1.4 babban ci gaba ne ga dan Adam baki daya. Baya ga haka, bunkasuwar kasar Sin da ma kasuwarta mai matukar girma, suna samar da sabbin damammaki ga kasashe daban daban.

Kamar yadda Bahaushe kan ce, gani ya kori ji. Muna fatan ‘yan uwanmu na Afirka za ku samu damar ziyartar jihar Xinjiang. Sabo da duk wadanda suka taba zuwa jihar, sun tarar da cewa, abubuwan da suka gani da ido a jihar, sun bambanta da wadanda suka karanta a rahotannin kafofin yada labarai na kasashen yamma. (Lubabatu Lei)

 

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bikin Baje Koli CIIE, Bikin Zaburar Da Manoman Afirka
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Koli CIIE, Bikin Zaburar Da Manoman Afirka

November 12, 2025
CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 
Ra'ayi Riga

CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

November 11, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Next Post
Ku Yi Haƙuri Da Gwamnatin Tinubu – Shettima

Ku Yi Haƙuri Da Gwamnatin Tinubu – Shettima

LABARAI MASU NASABA

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025
Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

November 15, 2025
Za A Yi Gwanjon Rigunan Messi Na Gasar Kofin Duniya Ta 2022 Da Kudi Tsagwagwa

Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi

November 15, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

November 15, 2025
Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

November 15, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

November 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

November 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.