ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Gaske Ne An Tilasta Wa Al’umma Aiki A Xinjiang?

by CGTN Hausa
2 years ago
Xinjiang

“Zan so in ce muku, bisa abin da na gani da ido, zance na wai akwai ‘aikin ala tilas’ wajen noman auduga a Xinjiang karya ce.” Malam Akram Memtimin ne ya yi wannan furucin a yayin amsa tambayar manema labarai. Akram Memtimin dan kabilar Uygur ne da ya fito daga wani kauye da ke jihar Xinjiang, kuma dan majalisar wakilan jama’ar kasar Sin ne, wanda yanzu haka ke halartar taron shekara shekara na majalisar a birnin Beijing, babban birnin kasar. Ya ce, da wuya ya fahimci me ya sa akwai kafofin yada labarai na kasashen yamma da suke yada labarai na wai “an tilasta wa dubun dubatar ‘yan kananan kabilu a jihar Xinjiang aikin tsintar auduga da hannu”. Ya ce, “auduga fari fat arzikinmu ne, ta hanyar noman auduga, mun samu kudin sayen mota da gidaje, mun ji dadin rayuwarmu, har akwai bukatar a tilasta mana yin hakan?” 

Abin haka yake, al’umma a duk kasashen da suka fito, burinsu shi ne su samu kudi ta hanyar yin aiki, don jin dadin rayuwa. Amma hakan ya zama “aikin ala tilas” a bakin gungun ‘yan siyasa da kafofin yada labarai na Amurka da sauran kasashen yamma.

  • An Rufe Taron Koli Na Kafofin Yada Labarai Dangane Da Kwaikwayon Hazikancin Dan Adam A Afrika
  • Xi Ya Jaddada Zurfafa Gyare-gyare Don Inganta Kwarewa A Sabbin Fannoni

Ban da haka, Amurka ta kuma matsa wa wasu kamfanonin kasashen waje irinsu Volkswagen da BASF, da su dakatar da ayyukansu a Xinjiang, bisa dalili na wai akwai “aikin ala tilas”. A game da wannan, Dr. Björn Alpermann, wani masanin harkokin kasar Sin a jami’ar Würzburg ta kasar Jamus, ya yi gargadin cewa, babu tabbas dangane da zargin da aka yi na wai ana “aikin ala tilas”. An ce, Dr. Björn Alpermann ya gudanar da bincike dangane da zargin da aka yi na wai “ana tilasta wa ‘yan kabilar Uygur aiki”, amma ba tare da gano shaidu ba. Ya yi gargadin kada a bar alhakin kan kamfanoni masu alaka da jihar Xinjiang, har ma a sanya haramci kan jihar Xinjiang baki daya. Ya ce, “A ganina, hakan ya wuce gona da iri, wanda ka iya haifar da barna ga al’ummar yankin, a maimakon a ce an taimaka musu.”

ADVERTISEMENT

Amma ita Amurka hakan ta yi. Tun watan Yunin shekarar 2022, gwamnatin Amurka ta fara gudanar da dokar wai “Hana Aikin Tilas Ga Al’ummar Uygur”, bisa ga dokar, ta hana shigar da kayayyakin da aka samar a jihar Xinjiang zuwa kasar. Amurka ta yi hakan ne bisa sunan kare “hakkin dan Adam”, amma a hakika, hakan ya haifar da rashin ayyukan yi tare da mayar da al’umma cikin kangin talauci da suka baro a baya, kuma burinta shi ne ta gurbata abubuwa a jihar Xinjiang, don cimma burin dakile ci gaban kasar Sin baki daya.

Na taba zuwa Xinjiang sau da dama. Amma wallahi ban taba gani da idona abin da aka ce wai “aikin tilas” ba, a maimakon haka, na ga yadda al’umma ‘yan kabilu daban daban ke rayuwa cikin walwala. Don haka, ina so in yi wa wadanda suka kirkiro karyar tambaya, shin al’ummar kabilar Uygur ba su da ‘yancin yin aiki? Jita-jitar da aka yada ta wai “aikin tilas”, a hakika tana tilasta musu barin aiki, wadda ta sa suka kasa sayar da kayayyakin da suka samar. To hakan na kiyaye hakkin su ne ko lalata hakkinsu?

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

A zahiri dai, saurin bunkasuwar kasar Sin cikin ‘yan shekarun baya ya sa wasu kasashe matukar damuwa, don haka suke iya kokarin hana bunkasuwar kasar. Amma dai kasar Sin tana da ‘yancin tabbatar da ci gabanta, zamanintar da kasar mai al’ummar biliyan 1.4 babban ci gaba ne ga dan Adam baki daya. Baya ga haka, bunkasuwar kasar Sin da ma kasuwarta mai matukar girma, suna samar da sabbin damammaki ga kasashe daban daban.

Kamar yadda Bahaushe kan ce, gani ya kori ji. Muna fatan ‘yan uwanmu na Afirka za ku samu damar ziyartar jihar Xinjiang. Sabo da duk wadanda suka taba zuwa jihar, sun tarar da cewa, abubuwan da suka gani da ido a jihar, sun bambanta da wadanda suka karanta a rahotannin kafofin yada labarai na kasashen yamma. (Lubabatu Lei)

 

 

Xinjiang
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

MASU ALAKA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Next Post
Ku Yi Haƙuri Da Gwamnatin Tinubu – Shettima

Ku Yi Haƙuri Da Gwamnatin Tinubu – Shettima

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.