ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Gaske Ne An Tilasta Wa Al’umma Aiki A Xinjiang?

by CGTN Hausa
2 years ago
Xinjiang

“Zan so in ce muku, bisa abin da na gani da ido, zance na wai akwai ‘aikin ala tilas’ wajen noman auduga a Xinjiang karya ce.” Malam Akram Memtimin ne ya yi wannan furucin a yayin amsa tambayar manema labarai. Akram Memtimin dan kabilar Uygur ne da ya fito daga wani kauye da ke jihar Xinjiang, kuma dan majalisar wakilan jama’ar kasar Sin ne, wanda yanzu haka ke halartar taron shekara shekara na majalisar a birnin Beijing, babban birnin kasar. Ya ce, da wuya ya fahimci me ya sa akwai kafofin yada labarai na kasashen yamma da suke yada labarai na wai “an tilasta wa dubun dubatar ‘yan kananan kabilu a jihar Xinjiang aikin tsintar auduga da hannu”. Ya ce, “auduga fari fat arzikinmu ne, ta hanyar noman auduga, mun samu kudin sayen mota da gidaje, mun ji dadin rayuwarmu, har akwai bukatar a tilasta mana yin hakan?” 

Abin haka yake, al’umma a duk kasashen da suka fito, burinsu shi ne su samu kudi ta hanyar yin aiki, don jin dadin rayuwa. Amma hakan ya zama “aikin ala tilas” a bakin gungun ‘yan siyasa da kafofin yada labarai na Amurka da sauran kasashen yamma.

  • An Rufe Taron Koli Na Kafofin Yada Labarai Dangane Da Kwaikwayon Hazikancin Dan Adam A Afrika
  • Xi Ya Jaddada Zurfafa Gyare-gyare Don Inganta Kwarewa A Sabbin Fannoni

Ban da haka, Amurka ta kuma matsa wa wasu kamfanonin kasashen waje irinsu Volkswagen da BASF, da su dakatar da ayyukansu a Xinjiang, bisa dalili na wai akwai “aikin ala tilas”. A game da wannan, Dr. Björn Alpermann, wani masanin harkokin kasar Sin a jami’ar Würzburg ta kasar Jamus, ya yi gargadin cewa, babu tabbas dangane da zargin da aka yi na wai ana “aikin ala tilas”. An ce, Dr. Björn Alpermann ya gudanar da bincike dangane da zargin da aka yi na wai “ana tilasta wa ‘yan kabilar Uygur aiki”, amma ba tare da gano shaidu ba. Ya yi gargadin kada a bar alhakin kan kamfanoni masu alaka da jihar Xinjiang, har ma a sanya haramci kan jihar Xinjiang baki daya. Ya ce, “A ganina, hakan ya wuce gona da iri, wanda ka iya haifar da barna ga al’ummar yankin, a maimakon a ce an taimaka musu.”

ADVERTISEMENT

Amma ita Amurka hakan ta yi. Tun watan Yunin shekarar 2022, gwamnatin Amurka ta fara gudanar da dokar wai “Hana Aikin Tilas Ga Al’ummar Uygur”, bisa ga dokar, ta hana shigar da kayayyakin da aka samar a jihar Xinjiang zuwa kasar. Amurka ta yi hakan ne bisa sunan kare “hakkin dan Adam”, amma a hakika, hakan ya haifar da rashin ayyukan yi tare da mayar da al’umma cikin kangin talauci da suka baro a baya, kuma burinta shi ne ta gurbata abubuwa a jihar Xinjiang, don cimma burin dakile ci gaban kasar Sin baki daya.

Na taba zuwa Xinjiang sau da dama. Amma wallahi ban taba gani da idona abin da aka ce wai “aikin tilas” ba, a maimakon haka, na ga yadda al’umma ‘yan kabilu daban daban ke rayuwa cikin walwala. Don haka, ina so in yi wa wadanda suka kirkiro karyar tambaya, shin al’ummar kabilar Uygur ba su da ‘yancin yin aiki? Jita-jitar da aka yada ta wai “aikin tilas”, a hakika tana tilasta musu barin aiki, wadda ta sa suka kasa sayar da kayayyakin da suka samar. To hakan na kiyaye hakkin su ne ko lalata hakkinsu?

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

A zahiri dai, saurin bunkasuwar kasar Sin cikin ‘yan shekarun baya ya sa wasu kasashe matukar damuwa, don haka suke iya kokarin hana bunkasuwar kasar. Amma dai kasar Sin tana da ‘yancin tabbatar da ci gabanta, zamanintar da kasar mai al’ummar biliyan 1.4 babban ci gaba ne ga dan Adam baki daya. Baya ga haka, bunkasuwar kasar Sin da ma kasuwarta mai matukar girma, suna samar da sabbin damammaki ga kasashe daban daban.

Kamar yadda Bahaushe kan ce, gani ya kori ji. Muna fatan ‘yan uwanmu na Afirka za ku samu damar ziyartar jihar Xinjiang. Sabo da duk wadanda suka taba zuwa jihar, sun tarar da cewa, abubuwan da suka gani da ido a jihar, sun bambanta da wadanda suka karanta a rahotannin kafofin yada labarai na kasashen yamma. (Lubabatu Lei)

 

 

Xinjiang
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Ku Yi Haƙuri Da Gwamnatin Tinubu – Shettima

Ku Yi Haƙuri Da Gwamnatin Tinubu – Shettima

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi

Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi

June 5, 2026
An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe

An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe

June 5, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Ma’aurata A Abuja

Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Ma’aurata A Abuja

June 5, 2026
Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi

Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi

June 5, 2026
An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

June 5, 2026
Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

June 5, 2026
Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 5, 2026
Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya

Mulkin Tinubu A Shekara 3:Ina Aka Fito? Ina Aka Dosa?

June 5, 2026
Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

June 5, 2026
Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

June 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.