• English
  • Business News
Friday, October 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dabaru Da Fasahohin Sin Na Taimakawa Kasashen Afirka Wajen Tinkarar Kwararar Hamada

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
Hamada

Rumfar kasar Sin a taron kasashen da suka kulla yarjejeniyar hana kwararar hamada ta MDD karo na 16 wato COP 16, ta gudanar da karamin taro a kwanan baya, mai taken“Fasahar kiyaye muhalli da makoma mai kyau”, inda kasar Sin ta yi musayar dabarun samun ci gaban hadin gwiwarta da sauran kasashe a bangaren hana yaduwar hamada. A hakika dai, har kullum Sin na bude kofarta ga sauran kasashe kan more dabarar hana kwararar hamada, don samar da gudummawarta ga kasashen da suka yi fama da wannan matsala.

 

Afirka nahiya ce da ta fi fama da kwararar hamada a duniya, hukumar kiyaye muhalli ta MDD ta ba da alkaluma cewa, filayen da yawansu ya kai kashi 45% na fadin nahiyar Afirka na fama da kwararar hamada a mabambantan matakai. Don kare kwararar hamada, kasashen Afirka na gudanar da jerin shirye-shirye, musamman ma shirin “babbar ganuwar itatuwa ta Afirka ”.

  • Kasar Sin Ta Gudanar Da Muhimmin Taron Tattalin Arziki Don Tsara Ayyukan 2025
  • Gwamnatin Tinubu Na Amfani Da Kuɗaɗen Tallafin Mai Don Ci Gaban Al’umma – Minista

Don tallafa wa kasashen Afirka a kokarinsu na hana kwararowar hamada, Kasar Sin ta sha gudanar da kwasa-kwasai din horar da kwararrun kasashen Afrika dangane da wannan shiri. A shekarar 2017 kuma, cibiyar nazarin yanayin halittu da yanayin kasa ta jihar Xinjiang ta kasar Sin ta kulla yarjejeniyar fahimtar juna da sakatariyar kungiyar babbar ganuwar itatuwa ta Afirka, ta yadda za su yi hadin gwiwa a bangaren sa ido kan tsarin muhallin halittu da amfani da albarkatun kasa cikin dorewa da horar da kwararru da samar da fasaha da sauransu, don kara karfin kasashen Afirka wajen yaki da kwararar hamada. A jihar Kano na Najeriya, cibiyar nazari ta hadin kan Sin da Afirka ta yi nazari kan matsalolin da ake fuskanta a wurin, ta kafa sabon salon shingen kare kwararar hamada da yankin gwaji na dasa itatuwan dake iya samar da arziki. Duba da iyakacin kokarin da Sin da kasashen Afirka suke yi, kason hamada a yankin Sahel ya ragu daga kashi 72.31% na shekarar 2000 zuwa kashi 69.23% na shekarar 2020.

 

LABARAI MASU NASABA

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

Dabarar da Sin take samu da ma fasahar zamani da take da ita, ababen bukata ne ga Afirka tamkar ruwa a jallo wajen dakile kwarar hamada, an yi imanin cewa, kasashen Afirka za su kara karfinsu na daidaita muhallin halittu da samun bunkasuwa mai dorewa bisa fasahar zamani iri na kasar Sin, da aiwatar da manufofin Sin bisa yanayin da suke ciki. (Mai zane da rubutu: MINA)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta
Daga Birnin Sin

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

October 23, 2025
Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa
Daga Birnin Sin

Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

October 23, 2025
Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba
Daga Birnin Sin

Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

October 23, 2025
Next Post
Babbar Kotun Tarayyar Kaduna Ta Sa Ranar Sauraron Karar Wasu Mahajjata Kan Hajjin 2024

Babbar Kotun Tarayyar Kaduna Ta Sa Ranar Sauraron Karar Wasu Mahajjata Kan Hajjin 2024

LABARAI MASU NASABA

Buƙatar Daƙile Badaƙalar Amfani Da Takardun Karatun Bogi A Nijeriya

Buƙatar Daƙile Badaƙalar Amfani Da Takardun Karatun Bogi A Nijeriya

October 24, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

October 23, 2025
Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

October 23, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno

October 23, 2025
Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

October 23, 2025
Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

October 23, 2025
Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

October 23, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kasar Sin Ta Karyata Rahoto Na Zuki-ta-malle Da Wata Cibiyar Binciken Amurka Ta Fitar Game Da Hadin Gwiwar Sin Da Yammacin Afirka

October 23, 2025
An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

October 23, 2025
Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 23, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.